< Lamentations 3 >
1 I, am the man, that hath seen affliction, by the rod of his indignation;
Ni ne mutumin da ya ga azaba ta wurin bulalar fushin Ubangiji.
2 Me, hath he driven out and brought into darkness, and not light;
Ya kore ni, ya sa na yi tafiya a cikin duhu maimakon a cikin haske;
3 Surely, against me, doth he again and again, turn his hand all the day.
ba shakka, ya juya mini baya, yana gāba da ni sau da sau, dukan yini.
4 He hath worn out my flesh and my skin, hath broken my bones;
Ya sa fatar jikina da naman jikina sun tsufa ya kuma karya ƙasusuwana.
5 He hath built up against me, and carried round me, fortifications and a trench;
Ya yi mini kwanton ɓauna ya kuma kewaye ni da baƙin ciki da kuma wahala.
6 In dark places, hath he made me sit, like the dead of age-past times.
Ya sa na zauna a cikin duhu kamar waɗanda suka mutu da jimawa.
7 He hath walled up around me, that I cannot get out, hath weighted my fetter;
Ya kewaye ni yadda ba zan iya gudu ba; Ya daure ni da sarƙa mai nauyi.
8 Yea, when I make outcry and implore, he hath shut out my prayer;
Ko lokacin da nake kira don neman taimako, ba ya jin addu’ata.
9 He hath walled in my ways with hewn stone, my paths, hath he caused to wind back.
Ya tare hanyata da tubula na duwatsu; ya sa hanyata ta karkace.
10 A bear lying in wait, he is to me, a lion, in secret places;
Kamar beyar da take a laɓe tana jira, kamar zaki a ɓoye,
11 My ways, hath he turned aside, and hath torn me in pieces, hath made me desolate;
ya janye ni daga kan hanya ya ɓatar da ni ya bar ni ba taimako.
12 He hath trodden his bow, and set me up, as a mark for the arrow.
Ya ja kwarinsa ya sa in zama abin baratarsa.
13 He hath caused to enter my reins, the sons of his quiver;
Ya harbi zuciyata da kibiyoyin kwarinsa.
14 I have become a derision to all my people, their song all the day;
Na zama abin dariya ga mutanena duka; suna yi mini ba’a cikin waƙa dukan yini.
15 He hath sated me with bitter things, hath drenched me with wormwood.
Ya cika ni da kayan ɗaci ya gundure ni da abinci mai ɗaci.
16 And he hath crushed, with gravel-stones, my teeth, hath made me cower in ashes;
Ya kakkarya haƙorana da tsakuwa; ya tattake ni cikin ƙura.
17 And thou hast thrust away from welfare, my soul, I have forgotten prosperity;
An hana ni salama; na manta da ko mene ne ake kira wadata.
18 And I said, Vanished is mine endurance, even mine expectation, from Yahweh.
Saboda haka na ce, “Darajata ta ƙare da kuma duk abin da nake begen samu daga wurin Ubangiji.”
19 Remember my humiliation and my fleeings, the wormwood and poison;
Na tuna da azabata da kuma sintiri, da na yi ta yi da ɗacin rai.
20 Thou wilt, indeed remember, that, bowed down concerning myself, is my soul;
Na tuna su sosai, sai kuma na ji ba daɗi a raina.
21 This, will I bring back to my heart, therefore, will I hope.
Duk da haka na tuna da wannan na kuma sa bege ga nan gaba.
22 The lovingkindnesses of Yahweh, verily they are not exhausted, Verily! not at an end, are his compassions:
Domin ƙaunar Ubangiji ba mu hallaka ba; gama jiyejiyanƙansa ba su ƙarewa.
23 New things for the mornings! Abundant is thy faithfulness:
Sababbi ne kowace safiya; amincinka kuwa mai girma ne.
24 My portion, is Yahweh, saith my soul, For this cause, will I wait for him.
Na ce wa kaina, “Ubangiji shi ne nawa; saboda haka zan jira shi.”
25 Good is Yahweh, to them who wait for him, to the soul that will seek him;
Ubangiji mai alheri ne ga waɗanda suke da bege a cikinsa, ga kuma wanda yake neman shi;
26 Good it is—both to wait and to be silent, for the deliverance of Yahweh;
yana da kyau ka jira shiru domin samun ceton Ubangiji.
27 Good it is for a man, that he should bear the yoke in his youth.
Yana da kyau mutum yă sha wuya tun yana yaro.
28 Let him sit alone, and keep silence, because he took it upon himself:
Bari yă zauna shiru shi kaɗai, gama haka Ubangiji ya sa yă yi.
29 Let him put, in the dust, his mouth, peradventure, there is hope!
Bari yă ɓoye fuskarsa cikin ƙura kila akwai bege.
30 Let him give, to him that smiteth him, his cheek, let him be sated with reproach.
Bari yă ba da kumatunsa a mare shi, yă kuma bari a ci masa mutunci.
31 Surely My Lord, will not cast off, unto times age-abiding;
Gama Ubangiji ba ya yashe mutane har abada.
32 Surely, though he cause grief, yet will he have compassion, according to the multitude of his lovingkindnesses;
Ko da ya kawo ɓacin rai, zai nuna tausayi sosai, ƙaunarsa tana da yawa.
33 Surely he hath not afflicted from his heart, nor caused sorrow to the sons of men.
Gama ba haka kawai yake kawo wahala ko ɓacin rai ga’yan adam ba.
34 To crush, under his feet, any of the prisoners of the earth;
Bai yarda a tattake’yan kurkuku a ƙasa ba,
35 To turn aside the right of a man, before the face of the Most High;
ko kuma a danne wa mutum hakkinsa a gaban Maɗaukaki,
36 To oppress a son of earth in his cause, My Lord, hath made no provision.
ko kuma a danne wa mutum shari’ar gaskiya ashe Ubangiji ba zai ga irin waɗannan abubuwa ba?
37 Who was it that spake, and it was done, [when], My Lord, had not commanded?
Wane ne ya isa yă yi magana kuma ta cika in ba Ubangiji ne ya umarta ba?
38 Out of the mouth of the Most High, Proceed there not misfortunes and blessing?
Ba daga bakin Maɗaukaki ne bala’i da abubuwa masu kyau suke fitowa ba?
39 Why should a living son of earth complain, [Let] a man [complain] because of his sins?
Don mene ne wani mai rai zai yi gunaguni sa’ad da aka ba shi horo domin zunubansa?
40 Let us search out our ways, and examine them well, and let us return unto Yahweh;
Bari mu auna tafiyarmu mu gwada ta, sai mu kuma koma ga Ubangiji.
41 Let us lift up our heart, to the opened palms, to the Mighty One in the heavens;
Bari mu ɗaga zuciyarmu da hannuwanmu ga Allah na cikin sama, mu ce,
42 We, have trespassed and rebelled, Thou, hast not pardoned.
“Mun yi zunubi mun yi tawaye ba ka kuwa gafarta ba.
43 Thou hast covered thyself with anger, and pursued us, hast slain—hast not spared;
“Ka rufe kanka da fushi, ka fafare mu; ka karkashe mu ba tausayi.
44 Thou hast screened thyself with the clouds, that prayer, should not pass through;
Ka rufe kanka da gajimare don kada addu’armu ta kai wurinka.
45 Offscouring and refuse, dost thou make us, in the midst of the peoples.
Ka mai da mu tarkace da juji a cikin mutane.
46 With their mouth, opened wide over us, [stand] all our foes.
“Dukan maƙiyanmu suna ta yin mana magana marar daɗi.
47 Terror and a pit, have befallen us, tumult and grievous injury;
Muna cika da tsoro, da lalatarwa da hallakarwa.”
48 With streams of water, mine eye runneth down, over the grievous injury of the daughter of my people.
Hawaye na kwararowa daga idanuna domin an hallaka mutanena.
49 Mine eye, poureth itself out and ceaseth not, without relief;
Idanuna za su ci gaba da kwararowa da hawaye, ba hutawa.
50 Until Yahweh out of the heavens shall look forth, and see,
Har sai in Ubangiji ya duba daga sama ya gani.
51 Mine eye dealeth severely with my soul, because of all the daughters of my city.
Abin da nake gani yana kawo mini baƙin ciki domin dukan matan birnina.
52 They, have laid snares, for me as a bird, who are mine enemies without cause:
Maƙiyana suna farauta ta ba dalili kamar tsuntsu.
53 They have cut off, in the dungeon, my life, and have cast a stone upon me;
Sun yi ƙoƙari su kashe ni a cikin rami suka kuma jajjefe ni da duwatsu;
54 Waters, flowed over, my head, I said, I am cut off!
ruwaye suka rufe kaina, sai na yi tunani cewa na kusa mutuwa.
55 I have called upon thy Name, O Yahweh, out of the dungeon below;
Na yi kira ga sunanka, ya Ubangiji, daga rami mai zurfi.
56 My voice, thou hast heard, —do not close thine ear to my respite, to mine outcry;
Ka ji roƙona, “Kada ka toshe kunnuwanka ka ƙi jin roƙona na neman taimako.”
57 Thou drewest near, in the day I kept calling on thee, thou saidst, Do not fear!
Ka zo kusa lokacin da na kira ka, kuma ka ce mini, “Kada ka ji tsoro.”
58 Thou hast pleaded, O My Lord, the pleas of my soul, hast redeemed my life;
Ya Ubangiji, ka goyi bayana; ka fanshi raina.
59 Thou hast beheld, O Yahweh, my failure to get justice, Pronounce thou my sentence;
Ya Ubangiji, ka ga inda aka yi mini ba daidai ba. Ka shari’anta, ka ba ni gaskiya!
60 Thou hast seen all their vindictiveness, all their plots against me.
Ka ga zurfin ramakonsu, da duk mugun shirin da suke yi mini.
61 Thou hast heard their reproach, O Yahweh, all their plots against me;
Ya Ubangiji, ka ji zaginsu, da duka mugun shirin da suke yi mini
62 The lips of mine assailants, and their mutterings, are against me, all the day;
Abin da maƙiyana suke yin raɗa a kai game da ni duk yini.
63 On their downsitting and their uprising, do thou look, I, am their song.
Dube su! A zaune ko a tsaye, suna yi mini ba’a cikin waƙoƙinsu.
64 Thou wilt render to them a recompense, O Yahweh, according to the work of their hands;
Ka ba su abin da ya dace su samu, ya Ubangiji, domin abin da hannuwansu suka yi.
65 Thou wilt suffer them a veiling of heart, thy curse to them;
Ka sa yana ta rufe zuciyarsu, kuma bari la’anarka ta bi su.
66 Thou wilt pursue in anger, and wilt destroy them, from under the heavens of Yahweh.
Ka fafare su cikin fushi ka hallaka su daga cikin duniya ta Ubangiji.