< Judges 11 >
1 Now, Jephthah the Gileadite, was a mighty man of valour, but, he, was the son of an unchaste woman, —yet Gilead was the father of Jephthah.
Yefta mutumin Gileyad, jarumi ne ƙwarai. Mahaifinsa ne Gileyad; mahaifiyar kuwa karuwa ce.
2 And the wife of Gilead bare him sons, —and, when the wife’s sons grew up, they thrust out Jephthah, and said unto him—Thou shalt not inherit with the house of our father, for, son of an alien woman, art thou.
Matar Gileyad ta haifa masa’ya’ya maza, kuma sa’ad da suka yi girma, sai suka kore Yefta, suka ce “Ba ka da gādo a cikin iyalinmu, domin kai ɗan wata mace ce.”
3 So Jephthah fled from the face of his brethren, and dwelt in the land of Tob, —and there gathered about Jephthah unemployed men, who went forth with him.
Saboda haka Yefta ya tsere daga’yan’uwansa ya zauna a ƙasar Tob, inda waɗansu’yan iska suka kewaye shi suka bi shi.
4 And so it came to pass, after a time, —that the sons of Ammon made war with Israel.
Ana nan, sa’ad da Ammonawa suka kai wa Isra’ilawa hari,
5 When, therefore, it came to pass that the sons of Ammon made war with Israel, then went the elders of Gilead, to summon Jephthah out of the land of Tob.
dattawan Gileyad suka je suka nemo Yefta daga ƙasar Tob.
6 And they said to Jephthah, Oh! come and be our commander, —that we may do battle with the sons of Ammon.
Suka ce masa, “Ka zo ka zama mana shugaba, don mu yaƙi Ammonawa.”
7 But Jephthah said to the elders of Gilead, Have not, ye, hated me, and thrust me out from the house of my father? Wherefore then, are ye come unto me, now, when ye are in distress?
Yefta ya ce musu, “Ba kun ƙi ni kuka kuma kore ni daga gidan mahaifina ba? Me ya sa kuke zuwa wurina yanzu sa’ad da kuke cikin wahala?”
8 And the elders of Gilead said unto Jephthah—Therefore, have we, now, returned unto thee, that, if thou go with us, and do battle with the sons of Ammon, then shalt thou become our head, for all the inhabitants of Gilead.
Mutanen Gileyad suka ce masa, “Duk da haka, muna juyo wajenka yanzu, ka zo tare da mu mu yaƙi Ammonawa, za ka kuma zama shugaban duk wanda yake zama a Gileyad.”
9 And Jephthah said unto the elders of Gilead—If ye do bring me back to do battle with the sons of Ammon, and Yahweh deliver them up before me, shall, I myself, become your head?
Yefta ya ce, “A ce kun dawo da ni in yaƙi Ammonawa, Ubangiji kuwa ya ba da su a hannuna, zan zama shugabanku?”
10 And the elders of Gilead said unto Jephthah—Yahweh himself, will be hearkening between us, if, according to thy word, so, we do not.
Dattawan Gileyad suka ce, “Ubangiji ne shaidanmu; za mu yi duk abin da ka ce.”
11 Then went Jephthah with the elders of Gilead, and the people set him over them, as head and commander, —and Jephthah spake all his words before Yahweh, in Mizpah.
Saboda haka Yefta ya tafi tare da dattawan Gileyad, mutanen kuwa suka naɗa shi shugabansu da kuma sarkinsu. Ya kuwa maimaita dukan maganarsa a gaban Ubangiji a Mizfa.
12 So then Jephthah sent messengers unto the king of the sons of Ammon, saying, —What occasion is there between us, that thou shouldst have come unto me, to fight against my land?
Sa’an nan Yefta ya aiki jakadu zuwa wurin sarkin Ammonawa su tambaya, “Me ya haɗa ka da ni, da ka kawo wa ƙasata yaƙi?”
13 And the king of the sons of Ammon said unto the messengers of Jephthah—Because Israel took away my land, when they came up out of Egypt, from Arnon even unto the Jabbok, and unto the Jordan, —now, therefore, restore them in peace.
Sarkin Ammonawa ya ce wa jakadu, “Sa’ad da Isra’ilawa suka fito daga Masar, sun ƙwace mini ƙasa tun daga Arnon zuwa Yabbok, har zuwa Urdun. Yanzu ka mayar mini ita cikin salama.”
14 And Jephthah yet once more sent messengers unto the king of the sons of Ammon;
Yefta ya sāke aikan jakadu wurin sarki,
15 and said unto him, Thus, saith Jephthah, —Israel took not away the land of Moab, or the land of the sons of Ammon;
yana cewa, “Ga abin da Yefta yake faɗi, Isra’ila ba tă ƙwace ƙasar Mowab ko ta Ammonawa ba.
16 for, when they came up out of Egypt, and Israel journeyed through the desert as far as the Red Sea, and came in unto Kadesh,
Amma sa’ad da suka bar Masar, Isra’ila ta bi ta hamada zuwa Jan Teku har suka zo Kadesh.
17 then did Israel send messengers unto the king of Edom, saying—Let me pass, I pray thee, through thy land, but the king of Edom hearkened not, unto the king of Moab also, sent they, but he would not consent, —so Israel abode in Kadesh.
Sa’an nan Isra’ila ta aiki jakadu zuwa ga sarkin Edom cewa, ‘Ka ba mu izini mu ratsa ƙasarka,’ amma sarkin Edom bai saurara ba. Suka kuma aika wa sarkin Mowab, shi ma ya ƙi. Saboda haka Isra’ila ta zauna a Kadesh.
18 Then journeyed they through the desert, and went round the land of Edom, and the land of Moab, and so came, from the rising of the sun, to the land of Moab, but encamped beyond Arnon, —and entered not within the boundary of Moab, for, Arnon, is the boundary of Moab.
“Daga can suka ci gaba ta hamada, suka zaga ƙasashen Edom da Mowab, suka wuce ta gabashin ƙasar Mowab, sa’an nan suka yi sansani a ɗaya gefen Arnon. Ba su shiga yankin Mowab ba, gama Arnon ce iyakarta.
19 Then did Israel send messengers unto Sihon king of the Amorites, king of Heshbon, —and Israel said unto him, Let us pass, we pray thee, through thy land as far as my own place.
“Sa’an nan Isra’ila ta aiki jakadu zuwa ga Sihon sarkin Amoriyawa, wanda yake mulki a Heshbon, ta ce masa, ‘Ka bar mu mu ratsa ƙasarka mu wuce zuwa wurinmu.’
20 But Sihon trusted not Israel, to pass through his boundary, so Sihon gathered together all his people, and encamped in Jahaz, —and fought against Israel.
Sihon dai, bai amince da Isra’ila su ratsa ƙasarsa ba. Ya tattara dukan mutanensa suka yi sansani a Yahza suka kuwa yaƙi Isra’ila.
21 Then did Yahweh, God of Israel, deliver up Sihon, and all his people, into the hand of Israel, and they smote them, —so Israel took possession of all the land of the Amorites, the inhabitants of that land.
“Sa’an nan Ubangiji, Allah na Isra’ila, ya ba da Sihon da dukan mutanensa a hannun Isra’ila, suka kuwa ci nasara a kansu. Isra’ila ta ƙwace dukan ƙasar Amoriyawa da suke zaune a ƙasar,
22 Yea they took possession of all the territory of the Amorites, —from Arnon, even as far as the Jabbok, and from the desert, even as far as the Jordan.
suka ƙwace dukan yankin Amoriyawa tun daga ƙasar Arnon zuwa Yabbok, daga hamada har zuwa Urdun.
23 Now, therefore, it was, Yahweh God of Israel, that dispossessed the Amorites from before his people Israel, —and shalt, thou, possess it?
“To, da yake Ubangiji, Allah na Isra’ila, ya kori Amoriyawa a gaban mutanensa Isra’ila, wane’yanci kake da shi da za ka karɓe ta?
24 What Chemosh thy god giveth thee to possess, that, wilt thou not possess? and, whatsoever Yahweh our God hath set before us to possess, that, shall we not possess?
Ba za ka karɓi abin da allahnka Kemosh ya ba ka ba? Haka mu ma, duk abin da Ubangiji Allahnmu ya riga ya ba mu, za mu mallake shi.
25 Now, therefore, art thou, really better, than Balak son of Zippor, king of Moab? Hath there been any, striving at all, with Israel, or any, fighting at all, with them,
Ka fi Balak ɗan Ziffor, sarkin Mowab ne? Ka taɓa ji ya yi hamayya da Isra’ila ko yă yi yaƙi da su?
26 all the time that Israel hath been dwelling in Heshbon and in her towns, and in Aroer and in her towns, and in all the cities that are on the banks of Arnon, —for three hundred years? Wherefore, then, have ye not made a rescue within that time?
Shekara ɗari uku Isra’ilawa suka yi zamansu a Heshbon, Arower da ƙauyukan kewayenta da dukan biranen da suke gefen Arnon. Me ya sa ba ka karɓe su a lokacin ba?
27 I, therefore, have not sinned against thee; but, thou, art doing me a wrong, in fighting against me, —Let Yahweh, the Judge, give judgment today, between the sons of Israel, and the sons of Ammon!
Ban yi maka laifi ba, amma kana musguna mini ta wurin kawo mini hari. Bari Ubangiji yă zama Alƙali, yă yanke hukunci tsakani Isra’ilawa da Ammonawa.”
28 But the king of the sons of Ammon hearkened not unto the words of Jephthah, which he sent unto him.
Duk da haka sarkin Ammonawa bai kula da saƙon da Yefta ya aika ba.
29 Then came upon Jephthah the spirit of Yahweh, and he passed through Gilead and Manasseh, —and passed through Mizpeh of Gilead, and, from Mizpeh of Gilead, he passed through [unto] the sons of Ammon.
Sa’an nan Ruhun Ubangiji ya sauko wa Yefta. Sai ya haye Gileyad da Manasse, ya ratsa ta Mizfa zuwa Gileyad, daga can kuma ya kai wa Ammonawa hari.
30 And Jephthah vowed a vow unto Yahweh, and said, —If thou wilt, deliver, the sons of Ammon into my hand,
Yefta kuwa ya yi wa’adi da Ubangiji ya ce, “In ka ba da Ammonawa a hannuwana,
31 then shall it be, that, whosoever cometh forth out of the doors of my house, to meet me, when I return successful, from the sons of Ammon, shall belong unto Yahweh, and I will offer him up, as an ascending-sacrifice.
duk abin da ya fara fitowa daga ƙofar gidana don yă tarye ni, sa’ad da na komo daga yaƙi da Ammonawa, zai zama na Ubangiji, zan miƙa shi hadaya ta ƙonawa.”
32 So then Jephthah passed over unto the sons of Ammon, to fight against them, —and Yahweh delivered them into his hand;
Sa’an nan Yefta ya haye zuwa wajen Ammonawa don yaƙi da su. Ubangiji kuwa ya ba da su a hannuwansa.
33 and he smote them, from Aroer even till thou enterest in to Minnith, even twenty cities, and as far as Abel-keramim, with an exceeding great smiting, —and thus were the sons of Ammon subdued before the sons of Israel.
Ya hallaka birane ashirin tun daga Arower zuwa yankin Minnit, har zuwa Abel-Keramim. Haka Isra’ila ta cinye Ammonawa ƙaf.
34 Then came Jephthah towards Mizpah, unto his own house, and lo! his daughter, coming forth to meet him, with timbrels, and with dances, —and, she, was none other than his only child, he had not, besides her, either son or daughter.
Sa’ad da Yefta ya komo gida a Mizfa, wa ya fito yă tarye shi,’yarsa tilo, tana rawa kiɗin ganguna! Ita ce kaɗai’yarsa. Ban da ita ba shi da ɗa ko’ya.
35 And it came to pass, when he saw her, that he rent his clothes, and said—Alas! my daughter, Thou hast, brought me low, Even, thou, hast come to be among them who trouble me, —Yet, I, opened wide my mouth unto Yahweh, and cannot go back.
Da ya gan ta, sai ya yayyage tufafinsa ya yi kuka ya ce, “Kaito!’Yata! Kin karya mini gwiwa, kuma na lalace, domin na yi wa’adi ga Ubangiji da ba zan iya in karya ba.”
36 And she said unto him—My father! Thou hast opened wide thy mouth unto Yahweh, Do with me, according to that which hath gone forth out of thy mouth, —after that Yahweh hath exacted for thee an avenging from thine enemies, from the sons of Ammon.
Ta ce, “Mahaifina, idan ka riga ka yi wa Ubangiji magana, sai ka yi da ni yadda ka yi alkawari, da yake Ubangiji ya ɗau maka fansa a kan Ammonawa.”
37 And she said unto her father, Let this thing, be done for me, —Let me alone two months, that I may depart, and go down upon the mountains, and bewail my virginity, I and my companions.
Sai ta kuma ce, “Sai dai, ka biya mini wannan bukata guda. Ka ba ni wata biyu in yi ta yawo da ni da ƙawayena a kan duwatsu mu yi makoki, domin ba zan yi aure ba.”
38 And he said—Depart. So he let her go, for two months, —and she departed, she and her companions, and bewailed her virginity, upon the mountains.
Ya ce mata, “Ki tafi,” Ya bar ta tă tafi har wata biyu. Ita da’yan matan suka tafi a kan duwatsu suka yi ta makoki domin ba za tă taɓa aure ba.
39 And it came to pass, at the end of two months, that she returned unto her father, and he fulfilled on her his vow which he had vowed, —she not having known man. And it became a statute, in Israel: —
Bayan watanni biyu ɗin sai ta komo wurin mahaifinta ya kuwa yi da ita yadda ya yi wa’adi. Ita kuwa ba tă taɓa san namiji ba. Wannan ya zama al’ada a Isra’ila,
40 From year to year, departed the daughters of Israel, to lament aloud for the daughter of Jephthah, the Gileadite, four days in the year.
cewa kowace shekara’yan mata sukan fita kwana huɗu don yin bikin tunawa da’yar Yefta mutumin Gileyad.