< John 13 >
1 Now, before the feast of the passover, Jesus, knowing that his hour had come, that he should remove out of this world unto the Father, having loved his own that were in the world, unto the end, loved them.
Kamin bukin idin ketarewa, sa'adda Yesu ya san lokaci ya yi da zai tashi daga wannan duniya zuwa wurin Uba, da yake ya kaunaci nasa wadanda ke duniya- ya kaunace su har karshe.
2 And, supper, being in progress, the adversary, having already thrust into the heart of Judas son of Simon Iscariot, that he should deliver him up, —
Iblis ya rigaya ya sa a zuciyar Yahuza Iskariyoti dan Saminu, ya bashe da Yesu.
3 [Jesus] knowing that, all things, the Father had given unto him, into his hands, and that, from God, he had come, and, unto God, he was going,
Ya san cewa Uba ya bada kome a hannunsa, kuma ya zo daga wurin Allah, kuma zai koma wurin Allah.
4 rouseth himself out of the supper, and layeth aside his garments, and taking a linen cloth, girded himself.
Ya tashi daga cin abincin, ya tube tufafinsa, ya dauki tawul ya lullube kansa da shi.
5 Next, he poureth water into the wash-basin, and began to be washing the feet of the disciples, and to be wiping them with the linen cloth wherewith he was girded.
Sa'an nan ya zuba ruwa a bangaji, ya fara wanke kafafun almajiran, yana shafe su da tawul din da ya lullube jikinsa da shi.
6 So he cometh unto Simon Peter. He saith unto him—Lord, dost, thou, wash my feet?
Ya zo wurin Bitrus Saminu, sai Bitrus ya ce masa,”Ubangiji, za ka wanke mani kafa?”
7 Jesus answered, and said unto him—What, I, am doing, thou, knowest not, as yet; howbeit, thou shalt got to know, hereafter.
Yesu ya amsa ya ce, “Abin da nake yi ba za ka fahimce shi yanzu ba, amma daga baya za ka fahimta.”
8 Peter saith unto him—In nowise shalt thou, ever, wash my feet. Jesus answered him—If I wash thee not, thou hast no part with me. (aiōn )
Bitrus ya ce masa, “Ba za ka taba wanke mani kafa ba.” Yesu ya amsa masa ya ce, “In ban wanke maka ba, ba ka da rabo da ni”. (aiōn )
9 Simon Peter saith unto him—Lord! not my feet only, but my hands also, and my head.
Bitrus ya ce masa, “Ubangiji, ba kafafuna kadai za ka wanke ba, amma da hannayena da kaina.”
10 Jesus saith unto him—He that hath bathed himself, hath no need [save as to the feet] to get washed; but is pure, as a whole. And, ye, are, pure, but not ye, all.
Yesu ya ce masa, “Duk wanda ya yi wanka ba ya da bukata, sai dai a wanke kafafunsa, amma shi tsarkakakke ne baidaya; ku tsarkakakku ne, amma ba dukanku ba.”
11 For he know the man that was delivering him up; therefore, said he—Not ye all, are pure.
(Don Yesu ya san wanda zai bashe shi, shiyasa ya ce, “Ba dukanku ne ke da tsarki ba.”)
12 When, therefore, he had washed their feet, and taken his garments, and reclined, again said he unto them—Are ye taking note, what I have done unto you?
Bayan Yesu ya wanke masu kafafu, ya dauki tufafinsa ya zauna kuma, ya ce masu, “Kun san abin da na yi muku?
13 Ye, call me, The Teacher, and, The Lord, —and, well, say, for I am.
kuna kirana, 'Malam, da Ubangiji,' kun fadi daidai, don haka Nake.
14 If then, I, have washed your feet, —[I] The Lord, and, The Teacher, ye also, ought to wash, one another’s, feet;
Idan ni Ubangiji da kuma mallam, na wanke maku kafafu, ya kamata kuma ku wanke wa junan ku kafafu.
15 For, an example, have I given you, —that, just as, I, did unto you, ye also, should be doing.
Gama na baku misali, saboda ku yi yadda na yi maku.
16 Verily, verily, I say unto you—A servant is not greater than his lord, neither one sent forth greater than he that sent him.
Lalle hakika ina gaya muku, bawa ba ya fi mai gidansa girma ba; dan aike kuma ba ya fi wanda ya aiko shi girma ba.
17 If, these things, ye know, happy, are ye, if ye be doing them.
Idan kun san wadannan abubuwa, ku masu albarka ne idan kun aikata su.
18 Not, concerning you all, am I speaking, —for, I, know of whom I made choice; but…that, the Scripture, might be fulfilled: He that feedeth on my bread, hath lifted up against me, his heel.
Ba ina magana akan dukanku ba; Na san wadanda na zaba. Amma domin Nassi ya cika: 'Shi Wanda ya ci gurasata, ya tayar mani'.
19 Henceforth, I tell you, before it cometh to pass, —that ye may believe, whensoever it doth come to pass, that, I, am he.
Ina fada maku wannan yanzu tun kafin haka ta faru domin sa'adda ta faru, ku gaskata Ni ne.
20 Verily, verily, I say unto you—He that receiveth whomsoever I shall send, receiveth, me; and, he that receiveth, me, receiveth him that sent me.
Hakika, hakika, Ina gaya maku, wanda ya karbi wanda na aiko, Ni ya karba, wanda kuma ya karbe ni, ya karbi wanda ya aiko ni.
21 These things, having said, Jesus, was troubled in spirit, and bare witness, and said—Verily, verily, I say unto you—One from among you, will deliver me up.
Bayan Yesu ya fadi haka, ya damu a ruhu, ya yi shaida ya ce, “Lalle hakika, ina gaya muku cewa daya daga cikinku zai bashe ni.”
22 The disciples began to look one at another, being at a loss concerning whom he was speaking.
Almajiran suka kalli juna, suna juyayin ko akan wa yake magana.
23 One of Jesus’ disciples was reclining in his bosom, one whom Jesus loved:
Daya daga cikin almajiransa, wanda Yesu yake kauna, yana a teburi, jingine a kirjin Yesu.
24 so Simon Peter beckoneth unto the same, and saith unto him—Say, Who is it? concerning whom he speaketh.
Siman Bitrus ya ce wa almajirin, “ka fada mana ko akan wa ya ke magana.”
25 He, falling back thus, upon the breast of Jesus, saith unto him—Lord! who is it?
Sai ya sake jingina a kirjin Yesu, ya ce masa, “Ubangiji, wanene?”
26 Jesus, therefore, answereth—That one, it is, for whom, I, shall dip the morsel, and give unto him. So, dipping the morsel, he taketh and giveth it unto Judas, son of Simon Iscariot.
Sannan Yesu ya amsa, “Shine wanda zan tsoma gutsuren gurasa in ba shi.” Sannan bayan ya tsoma gurasar, sai ya ba Yahuza Dan Siman Iskariyoti.
27 And, after the morsel, then, entered, Satan, into that man. Jesus, therefore, saith unto him—What thou art doing, do quickly!
To bayan gurasar, sai shaidan ya shige shi, sai Yesu ya ce masa, “Abinda kake yi, ka yi shi da sauri.”
28 But, as to this, none of them who were reclining with him knew respecting what, he said it to him.
Babu wani a teburin da ya san dalilin dayasa ya fada masa wannan.
29 For, some, were thinking, since Judas held the bag, that Jesus was saying to him—Buy the things of which we have, need, for the feast; or that, unto the destitute, he should give something.
Wadansu sun yi tsamanin cewa, tun da Yahuza ne ke rike da jakkar kudi, Yesu ya ce masa, “Ka sayi abinda muke bukata don idin”, ko kuma ya bada wani abu domin gajiyayyu.
30 So, he, taking the morsel, went out straightway; —and it was night.
Bayan Yahuza ya karbi gurasar, sai ya fita nan da nan. Da daddare ne kuwa.
31 When, therefore, he had gone out, Jesus saith—Just now, was, the Son of Man, glorified, and, God, was glorified in him;
Bayan Yahuza ya tafi, Yesu ya ce, “Yanzu an daukaka Dan mutum, kuma an daukaka Allah a cikinsa.
32 And, God, will glorify him, in himself, —and, straightway, glorify him.
Allah zai daukaka shi a cikin kansa, kuma zai daukaka shi nan da nan.
33 Dear children! Yet a little, am I, with you. Ye shall seek me, and, just as I said unto the Jews, Whither, I, go, ye, cannot come, unto you also, I say it, even now.
'Ya'ya kanana, ina tare da ku na wani gajeren lokaci. Zaku neme ni, kuma kamar yadda na fadawa Yahudawa, 'in da zan tafi ba za ku iya zuwa ba.' Yanzu kuma na fada maku wannan.
34 A new commandment, give I unto you, —That ye be loving one another: Just as I loved you, that, ye also, be loving one another:
Ina baku sabuwar doka, ku kaunaci juna; kamar yadda na kaunace ku, haka kuma ku kaunaci juna.
35 By this, shall all men take knowledge, that, my disciples, ye are, —If ye have, love, one to another.
Ta haka kowa zai san ku almajiraina ne, idan kuna kaunar juna.”
36 Simon Peter saith unto him—Lord! whither dost thou withdraw? Jesus answered—Whither I withdraw, thou canst not, now, follow me, but thou shalt follow, hereafter.
Siman Bitrus ya ce masa, “Ubangiji, ina za ka?” Yesu ya amsa ya ce, “Inda za ni, ba zaka iya bi na ba yanzu, amma zaka bini daga baya.”
37 Peter saith unto him—Lord! why, cannot I follow thee, even now? My life, in thy behalf, will I lay down.
Bitrus ya ce masa, “Ubangiji, don me ba zan iya binka a yanzu ba? Zan bada raina domin ka.”
38 Jesus answereth—Thy life, in my behalf, wilt thou lay down? Verily, verily, I say unto thee—In nowise shall a cock crow till thou hast denied me, thrice.
Yesu ya amsa ya ce, “Za ka bada ranka domina? Lalle hakika, ina gaya maka, kafin zakara ya yi cara zaka yi musu na sau uku.”