< Job 9 >

1 Then responded Job, and said—
Sai Ayuba ya amsa,
2 Of a truth, I know that so it is, But how can a mortal be just with GOD?
“Lalle, na san wannan gaskiya ne. Amma ta yaya mutum zai iya zama mai adalci a gaban Allah?
3 If he choose to contend with him, he cannot answer him, one of a thousand:
Ko da mutum yana so yă yi gardama da shi, ba zai taɓa amsa masa ba ko da sau ɗaya cikin dubu.
4 Wise in heart, and alert in vigour, What man hath hardened himself against him, and prospered!
Hikimarsa tana da zurfi, ikonsa yana da yawa. Wane ne ya taɓa yin faɗa da shi har ya yi nasara?
5 Who removeth mountains, unawares, Who overturneth them in his anger;
Yana matsar da manyan duwatsu kafin su sani kuma yana juya su cikin fushinsa.
6 Who shaketh the earth, out of its place, and, the pillars thereof, shudder;
Yana girgiza ƙasa, yana girgiza harsashenta.
7 Who commandeth the sun, and it breaketh not forth, and, about the stars, he putteth a seal;
Yana magana da rana sai ta ƙi yin haske; yana hana taurari yin haske.
8 Who spreadeth out fire heavens, by himself alone! and marcheth along, on the heights of the sea;
Shi kaɗai ya shimfiɗa sammai ya kuma yi tafiya a kan raƙuman ruwan teku.
9 Who made the Bear, the Giant and the Cluster, and the chambers of the south;
Shi ne ya halicci Mafarauci da Kare da Zomo, da Kaza, da’Ya’yanta da tarin taurari a sama, da taurarin kudu.
10 Who doeth great things, past finding out, and marvels, beyond number.
Yana yin abubuwan banmamaki waɗanda ba a iya ganewa, mu’ujizai waɗanda ba a iya ƙirgawa.
11 Lo! he cometh upon me, yet can I not see him, Yea he passeth on, yet can I not discern him.
Ba na iya ganinsa lokacin da ya wuce ni; ba na sani ya wuce lokacin da ya wuce.
12 Lo! he snatcheth away, who can bring it back? Who shall say unto him, What wouldst thou do?
Wane ne ya isa yă hana shi in ya ƙwace abu? Wa zai ce masa, ‘Me kake yi?’
13 As for GOD, if he withdraw not his anger, under him, will have submitted themselves—the proud helpers.
Allah ba ya danne fushinsa; ko dodannin ruwan da ake kira ayarin Rahab ya tattake su.
14 How much less that, I, should answer him, should choose my words with him?
“Ta yaya zan iya yin faɗa da shi? Ina zan iya samun kalmomin da zan yi gardama da shi?
15 Whom, though I were righteous, yet would I not answer, to be absolved, I would make supplication.
Ko da yake ba ni da laifi, ba zan iya amsa masa ba; sai dai roƙon jinƙai zan iya yi ga mahukuncina.
16 Though I had called, and he had answered me, I could not believe, that he would lend an ear to my voice.
Ko da na yi kira gare shi ya amsa mini, ban yarda cewa zai saurare ni ba.
17 For, with a tempest, would he fall upon me, and would multiply my wounds without need;
Zai sa hadari yă danne ni yă ƙara mini ciwona ba dalili.
18 He would not suffer me to recover my breath, for he would surfeit me with bitter things.
Ba zai bari in yi numfashi ba, sai dai yă ƙara mini azaba.
19 If it regardeth vigour, bold is he! If justice, who could summon him?
In maganar ƙarfi ne, shi babban mai ƙarfi ne! In kuma maganar shari’a ne, wa zai kai kararsa?
20 If I should justify myself, mine own mouth, would condemn me, —I blameless? then had it shewn me perverse.
Ko da ni marar ƙarfi ne, bakina ya isa yă sa in zama mai laifi; in ba ni da laifi, zai sa in yi laifi.
21 I blameless? I should not know my own soul, I should despise my own life!
“Ko da yake ba ni da laifi, ban damu da kaina ba; na rena raina.
22 One thing, there is, for which cause, I have said it, The blameless and the lawless, he bringeth to an end.
Ba bambanci; shi ya sa na ce, ‘Yana hallaka marasa laifi da kuma mugaye.’
23 If, a scourge, slay suddenly, at the despair of innocent ones, he mocketh.
Lokacin da bala’i ya kawo ga mutuwa, yakan yi dariyar baƙin cikin marasa laifi.
24 The earth, hath been given into the hand of a lawless one, The faces of her judges, he covereth, If not, then who is it?
Lokacin da ƙasa ta faɗa a hannun mugaye, yakan rufe idanun masu shari’a. In ba shi ba wa zai yi wannan?
25 My days, therefore, are swifter than a runner, They have fled, they have seen no good.
“Kwanakina sun fi mai gudu wucewa da sauri; suna firiya babu wani abin jin daɗi a cikinsu.
26 They have passed away with boats of paper-reed, like a vulture [which] rusheth upon food.
Suna wucewa kamar jirgin ruwan da aka yi da kyauro, kamar jahurma da ta kai wa namanta cafka.
27 If I say, I will forget my complaint, I will lay aside my sad countenance, and brighten up,
‘In na ce zan manta da abin da yake damu na, zan yi murmushi in daina nuna ɓacin rai,’
28 I am afraid of all my pains, I know, that thou wilt not pronounce me innocent.
duk da haka ina tsoron duk wahalata, domin na san ba za ka ɗauke ni marar laifi ba.
29 I, shall be held guilty, —Wherefore then, in vain, should I toil?
Tun da an riga an ɗauke ni mai laifi, duk ƙoƙarina a banza yake.
30 Though I bathe myself in snow water, and cleanse, in cleanness itself, my hands,
Ko da na wanke jikina duka da sabulu, na wanke hannuwana kuma da soda,
31 Then, in a ditch, wouldst thou plunge me, and mine own clothes should abhor me:
duk da haka za ka jefa ni cikin ƙazamin wuri, yadda ko rigunan jikina ma za su ƙi ni.
32 For he is not a man like myself, whom I might answer, nor could we come together into judgment:
“Shi ba mutum ba ne kamar ni wanda zan iya amsa masa, har da za mu yi faɗa da juna a wurin shari’a.
33 There is not, between us, a mediator, who might lay his hand upon us both.
In da akwai wanda zai iya shiga tsakaninmu, ya ɗora hannunsa a kanmu tare,
34 Let him take from off me his rod, and, his terror, let it not startle me:
wani wanda zai sa Allah yă daina duka na, don yă daina ba ni tsoro.
35 I could speak, and not be afraid of him, although, not so, am, I, in myself!
Sa’an nan ne zan iya yin magana ba tare da jin tsoronsa ba, amma a yadda nake a yanzu ba zan iya ba.

< Job 9 >