< Job 24 >

1 Wherefore, since from the Almighty times are not hid, have, his knowing ones, no vision of his days?
“Domin me Maɗaukaki ba zai sa ranar shari’a ba? Don me waɗanda suka san shi suke faman samun irin ranakun nan?
2 Boundaries, men move back, flocks, they seize and consume;
Mugaye suna satar fili ta wurin matsar da duwatsun da aka yi iyaka da su; suna satar dabbobi su kuma yi kiwon su.
3 The ass of the fatherless, they drive off, they take in pledge the ox of the widow;
Suna ƙwace wa marayu jakunansu suna kuma ƙwace wa gwauruwa sa don suna binta bashi.
4 They turn aside the needy out of the way, at once, are the humbled of the land made to hide themselves.
Suna ture matalauta daga hanya suna kuma sa dole matalautan ƙasar su ɓoye.
5 Lo! [as] wild asses in the wilderness, they go forth with their work, eager seekers for prey, the waste plain, yieldeth them food for their young;
Kamar jakunan jeji a hamada, matalauta suna aikin neman abinci gonaki marasa amfani suna tanada abinci wa’ya’yansu.
6 In the field—a man’s fodder, they cut down, and, the vineyard of the lawless, they strip of its late berries;
Suna girbi a gonakin da ba nasu ba, suna yin kala a gonar inabi ta mugaye.
7 Ill-clad, they are left to lodge without clothing, and have no covering in the cold;
Don ba su da tufafi, sukan kwana tsirara; ba su da wani abin da zai rufe su cikin sanyi.
8 With the sweeping rain of the mountains, are they wet, and, through having no shelter, they embrace a rock.
Sun jiƙe sharkaf da ruwan da yake kwararowa daga duwatsu, sun rungume duwatsu don rashin wurin fakewa.
9 Men tear, from the breast, the fatherless, and, over the poor, they take a pledge;
Ana ƙwace jinjiri mai shan mama; ana ƙwace ɗan yaron matalauci don biyan bashi.
10 Naked, they go about without clothing, and, famished, they carry the sheaves;
Don ba su da tufafi suna yawo tsirara; suna dakon dammunan hatsi amma duk da haka suna cikin shan yunwa.
11 Between their walls, are they exposed to the sun, Wine-presses, they tread, and yet are thirsty;
Suna matse zaitun a cikin kunyoyi suna kuma matse ruwan inabi daga’ya’yan inabi, duk da haka suna fama da ƙishi.
12 Out of the city—out of the houses, they make outcry. and, the soul of the wounded, calleth for help, and, GOD, doth not regard it as foolish.
Ana jin nishin masu mutuwa daga birni, kuma rayukan waɗanda aka ji musu rauni suna kuka suna kira don taimako. Amma bai ba wani laifi ba.
13 They, have become rebels against the light, —they are not acquainted with the ways thereof, neither abide they in the paths thereof.
“Akwai waɗanda suke yi wa haske tawaye, waɗanda ba su san hanyoyinsa ba ko kuma ba su taɓa bin hanyoyinsa ba.
14 With the light, riseth the murderer, He slayeth the poor and needy, And, in the night, he becometh like a thief.
Sa’ad da hasken yini ya tafi, mai kisankai yakan tashi; yă je yă kashe matalauta da masu bukata; a cikin dare yake shigowa kamar ɓarawo.
15 And, the eye of the adulterer, watcheth for the evening twilight, saying, Not an eye will see me! A covering for the face, he putteth on;
Idanun mazinaci suna jiran yamma ta yi sosai; yana tunani cewa, ‘Ba wanda zai gan ni,’ sai kuma yă ɓoye fuskarsa.
16 He breaketh, in the dark, into houses, —By day, they lock themselves in, They know not the light;
Cikin duhu mutane suna fasa gidaje, amma da rana sukan kulle kansu; ba sa so wani abu yă haɗa su da haske.
17 For, in the case of all such, morning to them is the death-shade, For, to be recognised, is a death-shade terror.
Gama dukansu, duhu mai yawa shi ne safiyarsu; suna abokantaka da razanar duhu.
18 Swift is he on the face of the waters, Speedily vanished their share in the land, He turneth not to the way of the vineyards.
“Duk da haka kamar abu marar nauyi suke a kan ruwa; gefen ƙasar da suke, an la’anta ta, yadda ba wanda yake zuwa gonar inabinsu.
19 Drought and heat, steal away snow water, Hades, them who have sinned. (Sheol h7585)
Kamar yadda zafi da fări suke shanye ƙanƙarar da ta narke, haka kabari zai ƙwace waɗanda suka yi zunubi. (Sheol h7585)
20 Maternal love shall forget him, the worm shall find him sweet, No more shall he be remembered, but perversity shall be shivered like a tree.
Waɗanda suka haife su za su manta da su, tsutsotsi za su cinye su; ba za a sāke tunawa da mugaye ba amma an sare su kamar itace.
21 He oppresseth the barren who beareth not, and, to the widow, he doeth not good;
Suna cutar macen da ba ta da ɗa, suna nuna wa gwauruwa rashin alheri.
22 Yea he draggeth along the mighty by his strength, He riseth up, and none hath assurance of life;
Amma Allah cikin ikonsa yakan kawar da masu ƙarfi, ko da yake sun yi ƙarfi, ba su da tabbacin rayuwa.
23 It is given him to be secure, and confident, yet, his eyes, are upon their ways.
Mai yiwuwa zai bar su su zauna cikin kwanciyar hankali, amma idanunsa suna kansu.
24 They are exalted a little, and are not, Yea having been laid low, like all men, are they gathered, Even as the top of an ear of corn, do they hang down.
Sukan samu cin nasara na ɗan lokaci, amma kuma za su ɓace; za su fāɗi a tattara su kamar sauran; za a datse su kamar kan hatsi.
25 But, if not, who then can convict me of falsehood? or make of no account my words?
“In wannan ba haka ba ne, wane ne zai shaida ƙarya nake yi har yă ƙi yarda da maganata?”

< Job 24 >