< Jeremiah 49 >

1 Of the sons of Ammon-Thus saith Yahweh: Hath Israel no, sons? Hath he no, heir? Why hath, Malkam, taken possession of Gad, Or have, his people, in the cities thereof, made their dwelling?
Game da Ammonawa. Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Isra’ila ba shi da’ya’ya maza ne? Ba shi da magāda ne? To, me ya sa Molek ya mallaki Gad? Me ya sa mutanensa suka zama a garuruwansa?
2 Therefore, lo! days are coming, Declareth Yahweh When I will cause to be heard against Rabbah of the sons of Ammon, an alarm of war, So shall she become a mound of desolation, And, her villages, with fire, shall blaze, —Then shall Israel, inherit them who inherited him, Saith Yahweh.
Amma kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da zan yi kirarin yaƙi a kan Rabba ta Ammonawa; zai zama tarin juji, za a sa wuta a ƙauyukan da suke kewayenta. Sa’an nan Isra’ila zai kori waɗanda suka kore shi,” in ji Ubangiji.
3 Howl, O Heshbon, for Ai is spoiled Make outcry, ye daughters of Rabbah, Gird you with sackcloth, Lament ye and run to and fro among the fences, —For, Malkam, into captivity, shall go, His priests and his princes, together.
“Ki yi kuka, ya Heshbon, gama an hallaka Ai! Ku tā da murya ku yi kuka, ya mazaunan Rabba! Ku sa tufafin makoki; ku ruga nan da can a cikin katanga, gama Molek zai tafi bauta, tare da firistocinsa da kuma fadawansa.
4 Why shouldst thou glory in the vales, The flowing of thy vale O apostate daughter? She who is trusting in her treasures, [saying, ] Who shall invade, me?
Me ya sa kuke taƙama da kwarurukanku, taƙama da kwarurukanku masu amfani? Ya ke diya marar aminci, kin dogara a wadatarki kika kuma ce, ‘Wa zai iya fāɗa mini?’
5 Behold me! bringing upon thee, terror Declareth My Lord, Yahweh of hosts, From all who are round about thee, —And ye shall be driven out every man before it, And there shall be none to bring home the wanderer;
Zan kawo razana a kanki daga waɗanda suke kewaye da ke,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. “Za a kore kowannenku, babu wani da zai tattara masu gudun hijira.
6 But afterwards, will I bring back the captivity of the sons of Ammon, Declareth Yahweh.
“Duk da haka, daga baya, zan maido da wadatar Ammonawa,” in ji Ubangiji.
7 Of Edom—Thus, saith Yahweh of hosts, Is there no longer wisdom in Teman? Hath counsel perished from the discerning? Is their wisdom corrupt?
Game da Edom. Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Babu sauran hikima a Teman ne? Shawara ta ɓace daga masu basira ne? Hikimarsu ta ruɓe ne?
8 Flee ye turn go down deep to dwell, O inhabitant of Dedan, —For the doom of Esau, have I brought in upon him The time of his visitation.
Ku juya ku gudu, ku ɓuya a cikin kogwanni masu zurfi, ku da kuke zama a Dedan, gama zan kawo masifa a kan Isuwa a lokacin da zan hukunta shi.
9 If, grape-gatherers, came to thee, Would they not leave, gleanings? If, thieves in the night, Would they not have taken away what sufficed them?
In masu tsinkar’ya’yan inabi suka zo maka, ba za su rage’ya’yan inabi kaɗan ba? In ɓarayi suka zo da dare, ba za su sata abin da kawai suke bukata ba?
10 But, I, have stripped Esau bare, I have uncovered his secret places, And to conceal himself, shall he not be able! Spoiled, are his seed, and his brethren, and his neighbours, and he is not.
Amma zan washe Isuwa sarai; zan bubbuɗe wuraren ɓuyarsa, don kada yă ɓoye kansa.’Ya’yansa, danginsa da maƙwabtansa za su hallaka, ba kuwa zai ƙara kasancewa ba.
11 Leave thy fatherless children I, will preserve them alive, —And thy widows, In me, let them trust.
Ka bar marayunka; zan tsare ransu. Gwaurayenka kuma za su dogara a gare ni.”
12 For, thus saith Yahweh—Lo! they who had not been adjudged to drink the cup, shall surely drink, And art thou, the one to go unpunished? Thou shalt not go unpunished, but shalt surely drink.
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “In waɗanda ba su dace su sha kwaf ɗin ba suka sha shi, me ya sa za ka kuɓuta? Ba za ka kuɓuta ba, sai ka sha shi.
13 For by myself, have I sworn, Declareth Yahweh, That, Bozrah shall become, an astonishment: a reproach and a desolation, and a contempt, —And all her cities shall become age-abiding desolations.
Na rantse da kaina,” in ji Ubangiji, “cewa Bozra za tă zama kufai da kuma abin tsoro, abin dariya da abin la’ana; kuma dukan garuruwanta za su kasance kufai har abada.”
14 A report, have I heard from Yahweh, Yea, an envoy, throughout the nations, hath been sent, —Gather yourselves together and come against her, And arise to the battle.
Na ji saƙo daga Ubangiji cewa; an aiki jakada zuwa ga al’ummai ya ce, “Ku tattara kanku don ku fāɗa mata! Ku tashi don yaƙi!”
15 For lo! Small, have I made thee among the nations, —Despised among men!
“Yanzu zan mai da kai ƙanƙani a cikin al’ummai abin reni a cikin mutane.
16 Thy monstrous thing, hath deceived thee, The insolence of thy heart, O thou that inhabitest the hidden recesses of the cliff, That holdest fast the height of the hill, —Though thou set high as an eagle, thy nest, From thence, will I bring thee down, Declareth Yahweh;
Tsoron da ka sa ake ji da kuma girman kan zuciyarka ya ruɗe ka, kai da kake zama a kogon dutse, kai da kake kan tudu. Ko da yake ka gina wa kanka sheƙa can bisa kamar na gaggafa, daga can zan sauko da kai ƙasa,” in ji Ubangiji.
17 So shall, Edom, become an astonishment, —Every one passing by her, will be astonished and hiss, over all her plagues:
“Edom za tă zama abin tsoro; dukan wanda ya wuce zai giggice ya yi tsaki saboda dukan mikinta.
18 Like the overthrow of Sodom and Gomorrah and her neighbours, Saith Yahweh, —There shall not dwell there—a man, Nor sojourn therein—any son of the earth-born.
Kamar yadda aka tumɓuke Sodom da Gomorra, tare da garuruwan da suke maƙwabtaka da su,” in ji Ubangiji, “haka ba wanda zai zauna a can; ba wani da zai zauna a cikinta.
19 Lo! like a lion, will he come up from the majesty of the Jordan, unto the pasture perennial, But I will wink—I will make him run away therefrom, Who then shall be the Chosen One whom over it, I may set in charge? For who shall be like unto, me? And who shall appoint me, a time? And who is the Shepherd that shall stand before, me?
“Kamar zaki mai haurawa daga kurmin Urdun zuwa wurin kiwo mai kyau, zan kori Edom daga ƙasarta nan da nan. Wane ne zaɓaɓɓen da zan naɗa don wannan? Wane ne yake kama da ni kuma wa zai kalubalance ni? Kuma wane makiyayi ne zai yi gāba da ni?”
20 Wherefore, hear ye The counsel of Yahweh which he hath counseled against Edom, And his devices which he hath devised against the inhabitants of Teman, —Surely the little ones of the flock shall drag them away, Surely he will cause their fold to be astounded over them.
Saboda haka, ku ji abin da Ubangiji ya shirya a kan Edom, abin da ya nufa wa waɗanda suke zama a Teman. Za a ja ƙanana na garken tumaki a tafi; zai hallaka wurin kiwonsu sarai saboda su.
21 At the noise of their fall, hath trembled the earth, At the outcry, in the Red Sea, was heard its noise.
Amon fāɗuwarsu zai sa ƙasa ta girgiza; za a kuma ji muryar kukansu a Jan Teku.
22 Lo! as an eagle, he shall mount and dart, and spread his wings over Bozrah, —So shall the heart of the heroes of Edom, in that day, become as the heart of a woman in her pain.
Duba! Gaggafa tana firiya tana kuma saukowa, tana buɗe fikafikanta a bisa Bozra. A wannan rana zukatan jarumawan Edom za su zama kamar macen da take naƙuda.
23 Of Damascus. Turned pale have Hamath and Arpad, For, a calamitous report, have they heard—they tremble, —In the sea, is anxiety, it cannot, rest.
Game da Damaskus. “Hamat da Arfad sun giggice, gama sun ji mummunar labari. Suna damuwa, sun damu kamar tekun da baya hutu.
24 Enfeebled is Damascus She hath turned to flee But terror, hath seized her, —Anguish and pangs, have seized her as a woman in childbirth.
Damaskus ta karai ta juya don ta gudu tsoro kuma ya kama ta; wahala da zafi sun kama ta, zafi kamar na mace mai naƙuda.
25 Alas! is she not forsaken—The city so praised! The citadel I rejoiced in!
Me ya sa ba a tafi aka bar sanannen birnin nan ba, birnin da nake jin daɗi?
26 Therefore shall her young men fall in her broadways, —And, all her men of war, shall be silent in that day, Declareth Yahweh of hosts;
Tabbatacce, samarinta za su fāɗi a tituna; dukan sojojinta za su yi shiru a wannan rana,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
27 Then will I kindle a fire in the walls of Damascus, —And it shall devour the palaces of Ben-hadad.
“Zan cinna wa katangar Damaskus wuta; za tă ci kagaran Ben-Hadad.”
28 Of Kedar. And of the kingdoms of Hazor Which Nebuchadrezzar king of Babylon smote—Thus, saith Yahweh, —Arise ye go up against Kedar, So shall they spoil the sons of the East:
Game da Kedar da mulkokin Hazor, waɗanda Nebukadnezzar sarkin Babilon ya fāɗa wa. Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Tashi, ku fāɗa wa Kedar ku kuma hallaka mutanen Gabas.
29 Their tents and their flocks, shall they take, And their curtains and all their baggage and their camels, shall they carry off for themselves, —And shall cry out unto them, Terror round about!
Za a ƙwace tentunansu da garkunansu; za a tafi da mafakanta tare da dukan kayayyakinsu da raƙumansu. Mutane za su yi musu ihu, ‘Razana ko’ina!’
30 Flee remove far away, go deep to dwell, Ye inhabitants of Hazor, Urgeth Yahweh; For Nebuchadrezzar king of Babylon—hath counseled against you, a counsel, And devised against you a device.
“Ku yi maza ku gudu! Ku zauna a kogo masu zurfi, ku da kuke zama a Hazor,” in ji Ubangiji. “Nebukadnezzar sarkin Babilon ya shirya muku maƙarƙashiya; ya ƙulla maƙarƙashiya a kanku.
31 Arise ye, go up against a nation at ease—dwelling securely, Commandeth Yahweh, —Having neither doors nor bars, Alone, do they dwell:
“Ku tashi ku kuma fāɗa wa al’umma da sauƙi wadda take zama da ƙarfin hali,” in ji Ubangiji, “al’ummar da ba ta da ƙofofi ko ƙyamare; mutanenta suna zama su kaɗai.
32 So shall their camels, become, a prey, And the throng of their cattle, a spoil, Then will I scatter them to every wind even the clipt-beards, —And from all sides of him, will I bring in their doom Declareth Yahweh.
Za a washe raƙumansu, garkunansu mai girma za su zama ganima. Zan watsar da waɗanda suke a wurare masu nesa a ko’ina zan kuma kawo musu masifa a kowane gefe,” in ji Ubangiji.
33 So shall Hazor become A habitation of jackals An astonishment unto times age-abiding: There shall not dwell there—a man, Nor sojourn therein—a son of the earth-born.
“Hazor za tă zama mazaunin diloli, kufai har abada. Ba wanda zai zauna a can; ba wanda zai zauna a cikinta.”
34 So much of the word of Yahweh as came unto Jeremiah the prophet, Against Elam, —in the beginning of the reign of Zedekiah king of Judah saying: —
Ga maganar Ubangiji da ta zo wa Irmiya annabi game da Elam, a farkon mulkin Zedekiya sarkin Yahuda.
35 Thus, saith Yahweh of hosts, Behold me! breaking the bow of Elam, —The beginning of their might;
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Ga shi, zan karye ƙarfin Elam, zaunannen ƙarfinsu.
36 Then will I bring in against Elam four winds from the four quarters of the heavens, And will scatter them to all these winds, —And there shall be no nation whither the outcasts of Elam, shall not come;
Zan kawo a kan Elam a kusurwoyi huɗu daga kusurwoyi huɗu na duniya; zan watsar da su zuwa kusurwoyi huɗu, kuma ba al’ummar da masu gudun hijirar Elam ba za su kai ba.
37 And I will cause Elam to be dismayed Before their enemies Even before them who are seeking their life, So will I bring upon them calamity, Even the glow of mine anger Declareth Yahweh, —And will send after them the sword, until I have made an end of them;
Zan ragargaza Elam a gaban maƙiyansu, a gaban waɗanda suke neman ransu; zan kawo masifa a kansu, da zafin fushina,” in ji Ubangiji. “Zan runtume su da takobi sai na kawo ƙarshensu.
38 And I will set my throne in Elam, —And will destroy, from thence king and princes, Declareth Yahweh;
Zan sa kursiyina a Elam in kuma hallaka sarkinta da fadawanta,” in ji Ubangiji.
39 But it shall come to pass In the afterpart of the days, That I will bring back the captivity of Elam, Declareth Yahweh.
“Duk da haka zan maido da wadatar Elam a kwanaki masu zuwa,” in ji Ubangiji.

< Jeremiah 49 >