< Jeremiah 25 >
1 The word which came upon Jeremiah concerning all the people of Judah, in the fourth year of Jehoiakim son of Josiah king of Judah, —the same, was the first year of Nebuchadrezzar king of Babylon;
Magana ta zo wa Irmiya game da dukan mutanen Yahuda a shekara ta huɗu ta Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda, wadda ta kasance shekara ta fari ta Nebukadnezzar sarkin Babilon.
2 which word Jeremiah the prophet spake concerning all the people of Judah, and against all the inhabitants of Jerusalem saying: —
Saboda haka Irmiya annabi ya ce wa dukan mutanen Yahuda da dukan mazaunan Urushalima.
3 From the thirteenth year of Josiah son of Amon king of Judah even until this day, the which is the twenty-third year, hath the word of Yahweh come unto me; and I have spoken unto you, betimes, speaking, yet have ye not hearkened.
Shekaru ashirin da uku, daga shekara ta goma sha uku ta Yosiya ɗan Amon sarkin Yahuda har zuwa wannan rana, maganar Ubangiji ta zo mini na kuma yi muku magana sau da sau, amma ba ku saurara ba.
4 And Yahweh sent unto you all, his servants the prophets, betimes sending, though ye hearkened not, neither inclined ye your ear to hear:
Ko da yake Ubangiji ya aika dukan bayinsa annabawa gare ku sau da sau, ba ku saurara ba, ba ku kuma kula ba.
5 saying, —Return I pray you every one from his wicked way and from the wickedness of your doings, So shall ye remain on the soil which Yahweh hath given to you and to your fathers, —even from age to age;
Sun ce, “Ku juye yanzu, kowannenku, daga mugayen hanyoyinku da mugayen ayyukanku, za ku kuwa iya zauna a ƙasar da Ubangiji ya ba ku da kuma kakanninku har abada abadin.
6 But do not go away after other gods to serve them and to bow down to them, —So shall ye not provoke me to anger with the work of your hands, and I will not bring calamity upon you;
Kada ku bi waɗansu alloli don ku bauta ku kuma yi musu sujada; kada ku tsokane ni in yi fushi da abin da hannuwanku suka yi. Sa’an nan ba zan kawo muku lahani ba.”
7 Howbeit ye hearkened not unto me, Declareth Yahweh, —that ye might provoke me to anger with the work of your hands unto your own hurt.
“Amma ba ku saurare ni ba,” in ji Ubangiji, “kun tsokane ni da abin da kuka yi da hannuwanku, kuka kuma kawo lahani wa kanku.”
8 Therefore, Thus, saith Yahweh of hosts, —Because ye have not heard my words,
Saboda haka Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Domin kun ƙi ku saurara ga maganata,
9 Behold me! sending and fetching all the families of the North, Declareth Yahweh and Nebuchadrezzar king of Babylon my servant, And I will bring them in against this land and against its inhabitants, and against all these nations, round about, —And I will devote them to destruction, and make them an astonishment and a hissing, and age-abiding desolations.
zan kira dukan mutanen arewa da bawana Nebukadnezzar sarkin Babilon,” in ji Ubangiji, “zan kuma kawo su su yi gāba da wannan ƙasa da mazaunanta da kuma gāba da dukan al’ummai da suke kewaye. Zan hallaka su sarai in kuma mai da su abin bantsoro da abin dariya, za su kuma zama kufai har abada.
10 And I will banish from among them—The voice of joy, and the voice of gladness, The voice of the bridegroom, and the voice of the bride, —The sound of the millstones, and the light of the lamp:
Zan kawar da muryoyin farin ciki da murna daga gare su, muryoyin amarya da na ango, ƙarar dutsen niƙa da hasken fitila.
11 So shall all this land become a desolation, an astonishment, And these nations shall serve the king of Babylon, seventy years.
Dukan wannan ƙasa za tă zama kango, kuma waɗannan al’ummai za su bauta wa sarkin Babilon shekaru saba’in.
12 And it shall some to pass—When the seventy years are fulfilled, I will visit upon the king of Babylon and upon that nation, Declareth Yahweh their iniquity, and upon the land of the Chaldeans, —and I will turn it into age-abiding desolations.
“Amma sa’ad da shekaru saba’in ɗin suka cika, zan hukunta sarkin Babilon da kuma al’ummarsa, ƙasar Babiloniyawa, saboda laifinsu,” in ji Ubangiji, “in kuma mai da ita kango har abada.
13 So will I bring upon that land, All my words which I have spoken against it, —Even all that is written in this book, which Jeremiah hath prophesied against all the nations.
Zan kawo wa wannan ƙasa dukan abubuwan na yi magana a kanta, dukan abubuwan da aka rubuta a wannan littafi, abubuwan da Irmiya kuma ya yi annabci a kan dukan al’ummai.
14 For many nations and great kings have used, even them, as slaves, So will I recompense to them—According to their deed and According to the work of their own hands.
Su kansu al’ummai da sarakuna masu yawa za su bautar da su; zan sāka musu bisa ga ayyukansu da aikin hannuwansu.”
15 For, thus, said Yahweh, God of Israel unto me, Take this cup of indignation wine out of my hand, —and cause all the nations unto whom I am sending thee, to drink it:
Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, ya faɗa mini, “Ka karɓi kwaf ruwan inabin nan na fushina a wurina, ka sa dukan al’umman da na aike ka gare su, su sha.
16 Yea they shall drink and reel to and fro and act as madmen, because of the sword which I am sending between them.
Sa’ad da suka sha, za su yi ta tangaɗi su kuma yi hauka saboda takobin da zan aika a cikinsu.”
17 So I took the cup out of the hand of Yahweh, —and caused all the nations unto whom Yahweh had sent me to drink:
Saboda haka na karɓi kwaf daga hannun Ubangiji na sa dukan al’ummai waɗanda ya aiko ni wurinsu su sha.
18 [to wit said he] —Jerusalem, and the cities of Judah, and her kings her princes, —making them a desolation, an astonishment, a hissing, and a contempt, as at this day;
Urushalima da garuruwan Yahuda, sarakunan da fadawanta, don su mai da su kufai da kuma abin bantsoro da ba’a da la’ana, yadda suke a yau;
19 Pharaoh king of Egypt and his servants and his princes, and all his people;
Fir’auna sarkin Masar, ma’aikatansa, fadawansa da dukan mutanensa,
20 And all the Bedawin, and all the kings of the land of Uz, —and all the kings of the land of the Philistines, even Ashkelon, and Gaza, and Ekron, and the remnant of Ashdod;
da dukan baƙin da suke can; dukan sarakunan Uz; dukan sarakunan Filistiyawa (waɗannan na Ashkelon, Gaza, Ekron da mutanen da aka bari a Ashdod);
21 Edom and Moab, and the sons of Ammon;
Edom, Mowab da Ammon;
22 And all the kings of Tyre, and all the kings of Zidon, —and the kings of the Coastland, that is beyond the sea;
dukan sarakunan Taya da Sidon; sarakunan bakin teku a ƙetaren teku;
23 Dedan, and Tema, and Buz, and all the clipt-beards;
Dedan, Tema, Buz da dukan waɗanda suke a manisantan wurare;
24 And all the kings of Arabia, and all the kings of the Bedawin, who dwell in the desert;
dukan sarakunan Arabiya da dukan sarakunan baƙin da suke zama a hamada;
25 And all the kings of Zimri, and all the kings of Elam, and all the kings of the Medes;
dukan sarakunan Zimri, Elam da Mediya;
26 And all the kings of the North, the near and the far every man with his brother, and all the kingdoms of the earth which are on the face of the ground; And the king of Sheshach, shall drink, after them.
da kuma dukan sarakunan arewa, nesa da kuma kusa, bi da bi, dukan mulkokin duniya. Bayan dukansu kuma, sai sarkin Sheshak ma yă sha.
27 Therefore shalt thou say unto them—Thus, saith Yahweh of hosts God of Israel, —Drink ye and be drunken, and vomit, and fall and rise not, —because of the sword which I am sending between you.
“Sa’an nan na faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa ku sha, ku bugu ku kuma yi amai, ku fāɗi, kada kuma ku ƙara tashi saboda takobin da zan aiko muku.’
28 And it shall be when they shall refuse to take the cup at thy hand to drink, then shalt thou say unto them—Thus, saith Yahweh of hosts, Ye shall certainly drink;
Amma in suka ki su karɓi kwaf ɗin daga hannunka su sha, ka faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa dole ku sha!
29 For lo! with the city on which my Name hath been called, am I making a beginning of sending calamity, And shall, ye, be held, guiltless? Ye shall not be held guiltless: For a sword, am I proclaiming against all the inhabitants of the earth, Declareth Yahweh of hosts.
Ga shi, na sa masifa tă yi aiki cikin birnin da ake kira da sunana, kuna gani za ku tafi ba hukunci? Ba za ku tafi ba hukunci ba, gama ina kawo wa dukan mazaunan duniya takobi, in ji Ubangiji Maɗaukaki.’
30 Thou, therefore, shalt prophesy against them all these words, —and shalt say unto them—Yahweh, from on high, will roar Yea from his holy habitation, will utter his voice, He will, roar mightily over his home, With a shout as of them who tread the winepress, will he answer unto all the inhabitants of the earth.
“Yanzu ka yi annabcin dukan waɗannan maganganu a kansu ka kuma ce musu, “‘Ubangiji zai yi ruri daga bisa; zai yi tsawa daga mazauninsa mai tsarki ya kuma yi ruri da ƙarfi a kan ƙasarsa. Zai yi ihu kamar waɗanda suke matsin’ya’yan inabi, yi ihu a kan dukan waɗanda suke zaune a duniya.
31 There hath come in a tumult as far as the end of the earth, For a controversy, hath Yahweh with the nations, Himself, hath entered into judgment with all flesh, —As for the lawless, he hath delivered them to the sword Declareth Yahweh.
Hayaniya za tă taso har iyakar duniya, gama Ubangiji zai kawo tuhume-tuhume a kan al’ummai; zai kawo shari’a a kan dukan’yan adam ya kuma kashe mugaye da takobi,’” in ji Ubangiji.
32 Thus, saith Yahweh of hosts, Lo calamity! going forth from nation to nation, —And a great tempest, shall bestirred up, out of the remote parts of the earth.
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Duba! Masifa tana yaɗuwa daga al’umma zuwa al’umma; hadari mai girma yana tasowa daga iyakar duniya.”
33 Then shall the slain of Yahweh in that day, be from one end of the earth, even unto the other end of the earth, —They shall not be lamented, nor gathered together nor buried, As dung, on the face of the ground, shall they serve.
A lokacin waɗanda Ubangiji ya kashe za su kasance a ko’ina, daga wannan bangon duniya zuwa wancan. Ba za a yi kuka dominsu, ba za a tattara su don a binne ba, amma za su zama kamar juji da an tsiba a ƙasa.
34 Howl ye shepherds and make outcry, And roll in the dust ye illustrious of the flock, Because your days for being slaughtered, are fulfilled, —Therefore will I break you in pieces, and ye shall fall like a precious vessel!
Ku yi kuka ku kuma yi makoki, ku makiyaya; ku yi ta birgima a ƙura, ku shugabannin garke. Gama lokacin da za a yanka ku ya zo; za ku fāɗi ku kuma farfasa kamar tukunyar yumɓu mai kyau.
35 Then shall place of refuge vanish from the shepherds, And escape from the illustrious of the flock.
Makiyaya ba za su sami wurin da za su gudu su tafi ba, shugabannin garke ba za su sami wurin kuɓuta ba.
36 The voice of the outcry of the shepherds! Yea the howling of the illustrious of the flock!—Because Yahweh is laying waste the grounds where they fed.
Ji kukan makiyaya, kururuwan shugabannin garke, gama Ubangiji yana hallaka wurin kiwo.
37 Then shall be silenced the prosperous pastures, —Because of the fierceness of the anger of Yahweh.
Rafi mai gudu a hankali zai zama kango saboda zafin fushin Ubangiji.
38 He hath left as a lion his covert, For their land hath become a horror, Because of the fierceness of oppression and Because of the fierceness of his anger.
Kamar zaki zai bar wurin ɓuyarsa, ƙasarsu kuma za tă zama kufai saboda takobin masu danniya da kuma saboda zafin fushin Ubangiji.