< Jeremiah 23 >

1 Alas for the shepherds who are destroying and scattering the sheep of my pasture Declareth Yahweh.
“Kaiton makiyayan da suka hallakar suka kuma warwatsar da tumakin makiyayanta!” In ji Ubangiji.
2 Therefore, Thus, saith Yahweh God of Israel, Concerning the shepherds who are tending my people, —Ye have scattered my flock and have driven them away, and have not visited them, —Behold me! visiting upon you the wickedness of your doings Declareth Yahweh.
Saboda haka ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila yana ce wa makiyayan da suke lura da mutanena, “Domin kun watsar da garkena kuka kuma kore su ba ku kuma lura da su ba, zan kawo hukunci a kanku saboda muguntar da kuka yi,” in ji Ubangiji.
3 I myself, therefore will gather the remnant of my flock, out of all the lands whither I have driven them, —And will bring them back unto their own fold, And they shall be fruitful and multiply;
“Ni kaina zan tattara raguwar garkena daga ƙasashen da na kore su zuwa zan kuma dawo da su ga makiyayansu, inda za su yi ta haihuwa su riɓaɓɓanya.
4 And I will raise up over them shepherds who will tend them, —So shall they not be afraid any more, nor be dismayed nor be missing, Declareth Yahweh.
Zan sa makiyaya a kansu waɗanda za su lura da su, ba za su ƙara jin tsoro ko razana ba, ba kuwa waninsu da zai ɓace,” in ji Ubangiji.
5 Lo! days are coming, Declareth Yahweh, when I will raise up to David A righteous Bud, And he shall reign as king, and prosper, And shall execute justice and righteousness in the land.
“Kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da zan tā da wa Dawuda Reshen adalci, Sarki wanda zai yi mulki da hikima ya kuma yi abin da yake gaskiya da kuma daidai a ƙasar.
6 In his days, Shall Judah be saved, And Israel abide securely, —And, this, is his name whereby he shall be called Yahweh, our Righteousness.
A cikin zamaninsa za a ceci Yahuda Isra’ila kuma zai zauna lafiya. Sunan da za a kira shi ke nan, Ubangiji Adalcinmu.
7 Therefore, lo! days are coming, Declareth Yahweh, When it shall not be said any more As Yahweh liveth, who brought up the sons of Israel out of the land of Egypt;
“Saboda haka fa, kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da mutanen ba za su ƙara cewa, ‘Muddin Ubangiji yana raye, wanda ya fito da Isra’ila daga Masar ba,’
8 but—As Yahweh liveth who hath brought up and who hath brought in the seed of the house of Israel out of the land of the North, and out of all the lands whither I have driven them, —And they shall remain upon their own soil.
amma za su ce, ‘Muddin Ubangiji yana raye, wanda ya fito da zuriyar Isra’ila daga ƙasar arewa da kuma daga dukan ƙasashen da ya yashe su.’ Sa’an nan za su zauna a ƙasarsu.”
9 As for the prophets, —Broken is my heart within me Trembled have all my bones, I have become as a drunken man, And as a strong man whom wine hath overcome, —Because of Yahweh, And because of his holy words.
Game da annabawa kuwa, Zuciyata ta karai; dukan ƙasusuwana suna kaɗuwa. Na zama kamar wanda ya bugu, kamar mutumin da ruwan inabi ya sha kansa, saboda Ubangiji da kuma maganarsa mai tsarki.
10 For with adulterers, is the land filled, Yea because of cursing, doth the land mourn, Dried up are the oases of the desert, —And, their oppression hath become wicked, And, their might is not right.
Ƙasar ta cika da mazinata; saboda la’ana ƙasar ta zama kango makiyaya a hamada ta bushe. Annabawa suna bin mugayen muradu suna kuma amfani da ƙarfinsu a hanyar marar kyau.
11 For both prophet and priest, are profane, —Even in my house, have I found their wickedness, Declareth Yahweh.
“Annabi da firist dukansu biyu marasa sanin Allah ne; har ma a cikin haikalina na tarar da muguntarsu,” in ji Ubangiji.
12 Therefore, shall their way become to them like slippery places in darkness, They shall be driven on and shall fall therein, —For I will bring in upon them calamity—The year of their visitation, Declareth Yahweh.
“Saboda haka hanyarsu za tă yi santsi; za a jefar da su cikin duhu a can kuwa za su fāɗi. Zan kawo musu masifa a shekarar da za a hukunta su,” in ji Ubangiji.
13 Even among the prophets of Samaria, had I seen a foolish thing, —They prophesied by Baal, And led astray my people Israel.
“A cikin annabawan Samariya na ga wannan abin banƙyama. Suna annabci ta wurin Ba’al suna ɓad da mutanena Isra’ila.
14 But among the prophets of Jerusalem, have I seen a horrible thing, —Committing adultery, And walking in falsehood, And so strengthening the hands of doers of wickedness, not to return any man from his wickedness: They have all of them become to me as Sodom, And her inhabitants as Gomorrah.
A cikin annabawan Urushalima kuma na ga wani abin bantsoro. Suna zina suna kuma rayuwar ƙarya. Sun ƙarfafa hannuwa masu aikata mugunta, domin kada wani ya juya daga muguntarsa. Dukansu sun yi kama da Sodom a gare ni; mutanen Urushalima sun yi kama da Gomorra.”
15 Therefore, Thus, saith Yahweh of hosts Concerning the prophets, —Behold me! Feeding them with wormwood, And I will cause them to drink poisoned water, —For from the prophets of Jerusalem, hath there gone forth profanity unto all the land.
Saboda haka, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa game da annabawa, “Zan sa su ci abinci mai ɗaci su kuma sha ruwa mai dafi, domin daga annabawan Urushalima rashin sani Allah ya bazu ko’ina a ƙasar.”
16 Thus, saith Yahweh of hosts, —Do not hearken unto the words of the prophets who are prophesying unto you, They are filling you, with vain hopes, —The vision of their own hearts, do they speak, Not from the mouth of Yahweh!
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Kada ku saurari abin da annabawan suke muku annabci; suna cika ku da sa zuciyar ƙarya. Suna maganar wahayi daga tunaninsu, ba daga bakin Ubangiji ba.
17 They keep on saying to them who despise me, Yahweh, hath spoken, saying, Prosperity, shall ye have! And to every one who is going on in the stubbornness of his own heart, have they said, There shall come on you, no calamity
Suna cin gaba da ce wa waɗanda suka rena ni, ‘Ubangiji ya ce za ku zauna lafiya.’ Ga duka waɗanda suke bin taurin zukatansu kuwa sukan ce, ‘Babu lahanin da zai same ku.’
18 For who hath stood in the council of Yahweh, that he should see and hear his word? Who hath given ear to his word and heard it?
Amma wane ne a cikinsu ya taɓa tsaya a majalisar Ubangiji yă ga ko ya ji maganarsa? Wa ya saurari ya kuma ji maganarsa?
19 Lo! the tempest of Yahweh! Indignation, hath come forth, Even a tempest whirling along: On the head of the lawless, shall it hurl itself down.
Ga shi, hadarin Ubangiji zai taso cikin hasala guguwa tana kaɗawa a kan kawunan mugaye.
20 The anger of Yahweh, wilt not return, Until he hath executed nor Until he hath established The purposes of his heart, —In the afterpart of the days, shall ye understand it perfectly.
Fushin Ubangiji ba zai kau ba sai ya aikata nufin zuciyarsa. A kwanakin masu zuwa za ku gane sarai.
21 I sent not the prophets yet they, ran, I spake not unto them yet, they, prophesied.
Ban aiki waɗannan annabawa ba, duk da haka sun tafi da saƙonsu; ban yi musu magana ba, duk da haka sun yi annabci.
22 But if they had stood in my council, Then might they have announced my words unto my people, And have turned them from their wicked way and from the wickedness of their doings.
Amma da a ce sun tsaya a majalisata, da sun yi shelar maganata ga mutanena sun kuma juyar da su daga mugayen hanyoyinsu da kuma daga mugayen ayyukansu.
23 Am I, a God at hand, Demandeth Yahweh, And not a God afar off?
“Ni ɗin Allah na kusa ne kawai,” in ji Ubangiji, “ba Allah na nesa ba?
24 Can any hide himself in secret places that I, shall not see him? Demandeth Yahweh, —The heavens and the earth, do I not fill? Demandeth Yahweh.
Akwai wanda zai iya ɓuya a lungu har da ba zan iya ganinsa ba?” In ji Ubangiji “Ban cika sama da ƙasa ba?” In ji Ubangiji.
25 I have heard what the prophets have said, who prophesy in my name falsely, saying, —I have dreamed! I have dreamed!
“Na ji abin da annabawa suna cewa su da suke annabcin ƙarya a sunana. Suna cewa, ‘Na yi mafarki! Na yi mafarki!’
26 How long shall it be in the heart of the prophets, To be prophets of falsehood, —And prophets of the deceit of their own heart?
Har yaushe wannan zai ci gaba a cikin zukata annabawa masu ƙarya, waɗanda suke annabcin ruɗun tunaninsu?
27 Who lay a plot to cause my people to forget my name by their dreams which they relate every man to his neighbour, —Just as their fathers forgat, my name, for Baal.
Suna tsammanin mafarkan da suke faɗa wa juna za su sa mutane su manta da sunana, kamar yadda kakanninsu suka manta da sunana ta wurin yin wa Ba’al sujada.
28 The prophet with whom is a dream, Let him relate it as a dream, And he with whom is my word, Let him speak my word as truth, —What is the chaff to the wheat? Demandeth Yahweh:
Bari annabin da ya yi mafarki ya faɗa mafarkinsa, amma bari wanda yake da maganata ya yi ta da aminci. Gama me ya haɗa ciyawa da alkama?” In ji Ubangiji.
29 Is not my word, like this, Like fire? Demandeth Yahweh, —And like a hammer, that breaketh in pieces a cliff?
“Maganata ba wuta ba ce,” in ji Ubangiji, “kuma kamar gudumar da kan ragargaza dutse?
30 Therefore! behold me! against the prophets, Declareth Yahweh, —who steal my words, every man from his neighbour:
“Saboda haka,” in ji Ubangiji, “Ina gāba da annabawan da suke satar maganganuna daga juna.
31 Behold me! against the prophets, Declareth Yahweh, who presume with their tongue and declare He declareth:
I,” in ji Ubangiji, “Ina gāba da annabawan da suke kaɗa harsunansu sa’an nan su ce, ‘Ubangiji ne ya furta.’
32 Behold me! against such as prophesy the dreams of falsehood, Declareth Yahweh, who have related them and led astray my people, with their falsehoods and with their recklessness, —whereas, I, had not sent them nor commanded them, so that they could be of no, profit, to this people, Declareth Yahweh.
Tabbatacce, ina gāba da waɗannan da suke annabci mafarkan karya,” in ji Ubangiji. “Suna faɗarsu suna ɓad da mutanena da ƙarairayinsu na rashin hankali, duk da haka ban aike su ba, ban kuwa umarce su ba. Ba su amfani wannan mutane ba ko kaɗan,” in ji Ubangiji.
33 But when this people or a prophet or a priest shall ask thee saying What is the oracle of Yahweh? Then shalt thou say unto them Ye, yourselves, are the oracle, Therefore will I reject you Declareth Yahweh;
“Sa’ad da waɗannan mutane, ko annabi ko firist, ya tambaye ka, ‘Mece ce maganarUbangiji?’ Ka ce musu, ‘Wace magana? Zan yashe ku, in ji Ubangiji.’
34 But the prophet, or the priest or the people who shall say—the oracle of Yahweh, I will bring punishment upon that man and upon his house.
In annabi ko firist ko da wani dabam ya ce, ‘Wannan ne abin da Ubangiji yake cewa,’ zan hukunta wannan mutum da kuma gidansa.
35 Thus, shall ye say—every man unto his neighbour and every man unto his brother, —What hath Yahweh, answered? or, What hath Yahweh, spoken?
Ga abin da kowannenku yana cin gaba da ce wa abokinsa ko danginsa, ‘Mece ce amsar Ubangiji?’ Ko kuwa ‘mene ne Ubangiji ya faɗa?’
36 but the oracle of Yahweh, shall ye not mention, any more, —for, every man’s oracle, shall be his own word, because ye have perverted the words of a Living God, Yahweh of hosts our God.
Amma kada ku ƙara ambatar ‘maganar Ubangiji’ domin kowace maganar mutum kan zama maganarsa. Ta haka kukan lalace maganar Allah mai rai, Ubangiji Maɗaukaki, Allahnmu.
37 Thus, shalt thou say unto the prophet, —What hath Yahweh, answered thee? or What hath Yahweh, spoken?
Ga abin da za ku ci gaba da faɗa wa annabi, ‘Mece ce amsar Ubangiji gare ka?’ Ko kuwa ‘mene ne Ubangiji ya faɗa?’
38 But, since ye keep on saying, The Oracle of Yahweh, therefore, Thus saith Yahweh, Because ye have said this word, The oracle of Yahweh, whereas I had sent unto you saying, Ye shall not say, The oracle of Yahweh
Ko da yake kuna cewa, ‘Wannan ce maganar Ubangiji,’ ga abin da Ubangiji yana cewa kuna amfani da kalmomi, ‘Wannan ce maganar Ubangiji,’ ko da yake na ce muku kada ku ce, ‘Wannan ce maganar Ubangiji.’
39 therefore, behold me! I will lift you up, —and carry you away, and the city which I gave to you and to your fathers from before my face;
Saboda haka, tabbatacce zan manta da ku in kuma jefar da ku daga gabana tare da birnin da na ba ku da kuma kakanninku.
40 and will give unto you reproach age-abiding, —and disgrace age-abiding, which shall not be forgotten.
Zan kawo muku madawwamiyar kunya, kunya ta har abada wadda ba za a taɓa manta ba.”

< Jeremiah 23 >