< Isaiah 7 >

1 And it came to pass in the days of Ahaz son of Jotham son of Uzziah king of Judah, that Rezin king of Syria, and Pekah son of Remaliah king of Israel, came up, to Jerusalem, to war against it, but could not prevail against it.
Sa’ad da Ahaz ɗan Yotam, ɗan Uzziya, yake sarkin Yahuda, Sarki Rezin na Aram da Feka ɗan Remaliya sarkin Isra’ila suka haura don su yaƙi Urushalima, amma ba su iya cinta da yaƙi ba.
2 And it was told the house of David, saying, Syria hath settled down upon Ephraim. Then shook his heart, and the heart of his people, as the trees of a forest shake before a wind.
Sai fa aka faɗa wa gidan Dawuda cewa, “Aram ya haɗa kansa da Efraim”; saboda haka zuciyar Ahaz da ta mutanensa suka firgita, sai ka ce itatuwa a kurmin da iska ta girgiza.
3 Then said Yahweh, unto Isaiah, Go forth, I pray thee, to meet Ahaz, thou, and Shear-jashub thy son, —unto the end of the channel of the upper pool, unto the highway of the fuller’s field;
Sai Ubangiji ya ce wa Ishaya, “Fita, kai da ɗanka Sheyar-Yashub, don ku sadu da Ahaz a ƙarshen wuriyar da take kawo ruwa daga Tafkin Tudu, a hanyar Filin Mai Wanki.
4 and say unto him—Take heed and keep thyself calm—do not fear, neither let thy heart be faint, because of these two fag-ends of smoking firebrands, —in spite of the glow of the anger of Rezin and Syria and the son of Remaliah.
Ka faɗa masa, ‘Ka yi hankali, ka natsu kada kuma ka ji tsoro ko ka damu, kada ka ji tsoron fushin sarki Rezin da na Aram da na ɗan Remaliya, ba wani abu mai hatsari ba ne, bai fi hayaƙin’yan ƙirare biyu da suke cin wuta ba.
5 Because Syria, hath taken counsel against thee, for mischief, —[with] Ephraim and the son of Remaliah, saying,
Aram, Efraim da ɗan Remaliya sun ƙulla maƙarƙashiya, suna cewa,
6 Let us go up against Judah, and besiege it, and break it open, for ourselves, —and set up a king in the midst thereof, even the son of Tabeal,
“Bari mu kai wa Yahuda hari; bari mu yayyage su mu rarraba su a tsakaninmu, mu naɗa Tabeyel sarki a kansu.”
7 Thus, saith My Lord, Yahweh, —It shall not stand Neither shall it come to pass!
Duk da haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce, “‘Ba zai faru ba, ba zai auku ba,
8 For, though the head of Syria is Damascus, And, the head of Damascus, is Rezin, Yet within threescore and five years more, shall Ephraim be broken that it shall not be a people;
gama kan Aram shi ne Damaskus, kan Damaskus kuma kawai shi ne Rezin. Cikin shekaru sittin da biyar za a wargaje Efraim har ba za tă iya rayuwa ta zama al’umma ba.
9 Even though the head of Ephraim is Samaria, And, the head of Samaria, is the son of Remaliah. If ye trust not, Surely, ye cannot be trusted!
Kan Efraim shi ne Samariya, kan Samariya kuma kawai shi ne ɗan Remaliya. In ba ku tsaya da ƙarfi cikin bangaskiyarku ba, ba za ku dawwama ba.’”
10 And again spake Yahweh unto Ahaz saying—
Ubangiji ya kuma yi magana wa Ahaz ya ce,
11 Ask thee a sign, of Yahweh thy God, —Go down deep for a request, Or ascend on high! (Sheol h7585)
“Ka roƙi Ubangiji Allahnka yă ba ka alama, ko daga zurfafa masu zurfi ko kuwa daga can cikin sama.” (Sheol h7585)
12 But Ahaz said, —I will not ask Nor will I put Yahweh to the proof.
Amma Ahaz ya ce, “Ba zan nema ba; ba zan gwada Ubangiji ba.”
13 Then said he—Hear, I pray you, O house of David! Is it, too little, for you to weary men, that ye must weary even my God?
Sa’an nan Ishaya ya ce, “To, ku saurara, ya ku gidan Dawuda! Abin kirki kuke yi ne da kuka ƙure haƙurin jama’a? Ko haƙurin Allah ne kuma kuke so ku ƙure?
14 Wherefore let My Lord Himself give you a sign, —Lo! a Virgin, being with child and giving birth to a son, thou wilt call his name Immanuel.
Saboda haka Ubangiji kansa zai ba ku alama. Ga shi budurwa za tă yi ciki, za tă haifi ɗa, za tă kuwa kira shi Immanuwel.
15 Curds and honey, shall he eat, by the time that he knoweth to refuse the bad and choose the good;
In ya yi girma har ya isa yanke shawara don kansa, madara da zuma ne abincinsa.
16 for before the boy knoweth to refuse the bad and choose the good, forsaken shall be the land, at which, thou, art alarmed, of the presence of both her kings.
Amma kafin yaron yă isa yanke shawara yă ƙi abin da yake mummuna, yă zaɓi abin da yake nagari, ƙasashen sarakunan nan biyu da kuke tsoro za su zama kango.
17 Yahweh will bring upon thee and upon thy people, and upon the house of thy father, days which have not come, from the day when Ephraim departed from Judah, —even the king of Assyria.
Ubangiji zai aukar maka da kwanakin wahala, kai da jama’arka, da dukan iyalin gidan sarauta, waɗanda suka fi muni tun lokacin da aka raba mulkin Efraim daga na Yahuda, zai kawo sarkin Assuriya.”
18 And it shall come to pass in that day that Yahweh will give a signal—To the fly that is in the uttermost part of the Nile-canals of Egypt, And to the bee that is in the land of Assyria.
A wannan rana Ubangiji zai yi feɗuwa yă kira ƙudaje daga rafuffuka masu nisa na Masar da kuma ƙudan zuma daga ƙasar Assuriya.
19 And they shall all of them come and settle down—In the desolate torrent-valleys, And in the rents of the crags, —And on all the thorn-bushes, And on all the pastures,
Za su zo su mamaye kwazazzabai da kogwanni cikin duwatsu, a kan dukan ƙayayyuwa da dukan rammukan ruwa.
20 In that day, will My Lord shave, with a hired razor, even with them of the lands over the River Euphrates, with the king of Assyria, the head and the hair of the feet, —yea, even the beard, will it sweep off.
A wannan rana Ubangiji zai yi amfani da rezan da aka yi haya daga ƙetaren Kogi, sarkin Assuriya ke nan, yă aske kanku da gashin ƙafafunku, zai kuma aske gemunku.
21 And it shall come to pass in that day, that a man shall keep alive a young cow and two sheep.
A ranar, mutum zai bar karsana ɗaya da awaki biyu da rai.
22 Yea it shall come to pass for the abundance of the yield of milk, that he shall eat curds, —for, curds and honey, shall every one eat that is left in the midst of the land.
Kuma saboda yalwa madarar da suke bayarwa, zai kasance da madarar da zai sha. Dukan waɗanda suka rage a ƙasar za su sha madara da zuma.
23 And it shall some to pass in that day, that, every place wherein there used to be a thousand vines at a thousand pieces of silver, —yea, even for briars and thorns, shall it be.
A wannan rana, a kowane wuri inda akwai kuringa dubu da kuɗinsu ya kai shekel dubu na azurfa, ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiya ne kawai za su kasance a can.
24 With arrows and with a bow, shall one come in thither, —for briars and thorns, shall be all the land.
Mutane za su je can da baka da kibiyoyi, gama ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiya ne za su rufe ƙasar.
25 But all the hills which, with the hoe, can be weeded, —there shall not come thither, the fear of briars and thorns, —but it shall be for the sending forth of oxen, and for the tread of lesser cattle.
Game da dukan tuddai da dā ake nome da garemani kuwa, ba za ku ƙara je wurin ba saboda tsoron ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiya; za su zama wuraren da ake kai shanu a sake su su yi ta yawo da kansu, tumaki kuma su yi ta gudu.

< Isaiah 7 >