< Isaiah 54 >
1 Shout in triumph, O barren one, Who hadst not borne, —Break forth into shouts of triumph—and trill thy voice, Who hadst not travailed in birth, For, more, are the children of the Desolate Than the children of Her who had the husband, Saith Yahweh.
“Ki rera, ya ke bakararriya, ke da ba ki taɓa haihuwa ba; ki ɓarke da waƙa, ki yi sowa don farin ciki, ke da ba ki taɓa naƙuda ba; domin’ya’yan mace mai kaɗaici sun fi na mai miji yawa,” in ji Ubangiji.
2 Enlarge the space of thy tent And the curtains of thy habitations, let them spread forth do not spare, —Lengthen thy cords, And thy tent-pins, make thou fast;
“Ki fadada wurin tentinki, ki miƙe labulen tentinki da fāɗi, kada ki janye; ƙara tsawon igiyoyinta, ki kuma ƙara ƙarfin turakunta.
3 For, on the right hand and on the left, shalt thou break forth, —And thy seed, shall of the nations, take possession, And forsaken cities, shall they cause to be inhabited.
Gama za ki fadada zuwa dama da hagu; zuriyarki za su kori al’ummai su kuma zauna a kufan biranensu.
4 Do not fear for thou shalt not turn pale, Neither feel disgraced for thou shalt not be put to the blush, —For, the shame of thy youth, shalt thou forget, And the reproach of thy widowhood, shalt thou remember no more;
“Kada ki ji tsoro; ba za ki sha kunya ba. Kada ki ji tsoron wulaƙanci, ba za a ƙasƙantar da ke ba. Za ki manta da kunyar ƙuruciyarki ba kuwa za ki tuna da zargin zaman gwauruwarki ba.
5 For, thy husband, is, thy Maker, Yahweh of hosts, is his Name, —And, thy redeemer, the Holy One of Israel, The God of all the earth, shall he be called.
Gama Mahaliccinki shi ne mijinki, Ubangiji Maɗaukaki ne sunansa, Mai Tsarkin nan na Isra’ila ne Mai Fansarki; ana ce da shi Allahn dukan duniya.
6 For, like a wife forsaken and grieved in spirit, hath Yahweh called thee, —Even the wife of youthful days, in that thou wast rejected saith thy God.
Ubangiji zai kira sai ka ce ke mace ce da aka yashe ta tana kuma damuwa a ranta, macen da ta yi aure a ƙuruciya, sai kawai aka ƙi ta,” in ji Allahnki.
7 For a small moment, I forsook thee, —But, with abounding compassions, do I embrace thee:
“Gama a ɗan ƙanƙanen lokaci na rabu da ke, amma da ƙauna mai zurfi zan sāke dawo da ke.
8 In an overflow of vexation, I hid my face for a moment, from thee, But, with lovingkindness age-abiding, have I had compassion on thee, —saith thy Redeemer Yahweh.
Cikin fushi mai zafi na ɓoye fuskata daga gare ki na ɗan lokaci, amma da madawwamin alheri zan ji tausayinki,” in ji Ubangiji Mai Fansarki.
9 For, the waters of Noah, is this unto me, —As to which I sware that the waters of Noah should not again pass over the earth, So have I sworn Not to be vexed with thee Nor to rebuke thee.
“A gare ni wannan ya yi kamar kwanakin Nuhu, sa’ad da na rantse cewa ruwan Nuhu ba za su ƙara rufe duniya ba. Yanzu fa na rantse ba zan yi fushi da ke ba, ba zan ƙara tsawata miki kuma ba.
10 For, the mountains, may move away, And the hills, may be shaken, —But, my lovingkindness, from thee, shall not move away, And, my covenant of peace, shall not be shaken, saith he who hath compassion upon thee—Yahweh.
Ko da duwatsu za su girgiza a kuma tumɓuke tuddai, duk da haka madawwamiyar ƙaunata da nake yi miki ba za tă jijjigu ba ba kuwa za a kawar da alkawarin salamata ba,” in ji Ubangiji, wanda ya ji tausayinki.
11 O thou humbled one storm-tossed, uncomforted, —Lo! I, am about to set in antimony, thy stones, And will found thee in sapphires;
“Ya ke birni mai shan azaba, wadda hadari ya bulale ki ba a kuma ta’azantar da ke ba, zan gina ke da duwatsu turkuwoyis, zan kafa harsashenki da duwatsun saffaya.
12 And make rubies, thy battlements, And thy gates, sparkling stones, —And, all thy boundaries, stones of delight;
Zan gina hasumiyarki da jan yakutu, ƙofofinki kuma da duwatsu masu haske, dukan katangarki kuma da duwatsu masu daraja.
13 And, all thy children, shall be the instructed of Yahweh, —And, great, shall be the prosperity of thy children.
Ubangiji zai koya wa dukan’ya’yanki maza, da girma kuma salamar’ya’yanki zai zama.
14 In righteousness, shalt thou be established, —Be thou far from oppression—But indeed thou shalt not fear, And from crushing calamity—But indeed it shall not come nigh unto thee.
Da adalci za a kafa ke. Zalunci zai yi nesa da ke; ba za ki kasance da wani abin da za ki ji tsoro ba. Za a kawar da duk wani abin banrazana; ba zai yi kusa da ke ba.
15 Lo! they would, quarrel, with thee—not at all from me, —Whoso hath quarrelled with thee, over thee, shall fall.
In wani ya far miki, ba daga wurina ba ne; duk wanda ya far miki zai miƙa wuya gare ki.
16 Lo! I, have created the smith, who bloweth up a fire of coals, And who bringeth forth an instrument for his work, —And, I, have created the waster to destroy:
“Duba, ni ne wanda na halicci maƙeri wanda yake zuga garwashi ya zama harshen wuta ya kuma ƙera makamin da ya dace da aikinsa. Ni ne kuma na halicci mai hallakarwa ya yi ɓarna;
17 No instrument formed against thee, shall prosper, And every tongue that riseth against thee in judgment, shalt thou prove to be lawless, —This is the inheritance of the servants of Yahweh. And, their righteousness, is from me, Declareth Yahweh.
ba makamin da aka ƙera don yă cuce ki da zai yi nasara, za ki kuma mayar da magana ga duk wanda ya zarge ki. Wannan ne gādon bayin Ubangiji, kuma wannan ita ce nasararsu daga gare ni,” in ji Ubangiji.