< Isaiah 48 >
1 Hear ye this—O house of Jacob, Ye who call yourselves by the name of Israel, Yea from the waters of Judah, came they forth, —Who swear by the name of Yahweh, And, by the God of Israel, call to remembrance—Not in truth, nor in righteousness;
“Ku kasa kunne ga wannan, ya gidan Yaƙub, waɗanda ake kira da sunan Isra’ila suka kuma fito daga zuriyar Yahuda, ku da kuke yin rantsuwa da sunan Ubangiji kuna kuma kira sunan Allah na Isra’ila, amma ba da gaskiya ko adalci ba,
2 For of the holy city, do they call themselves, And on the God of Israel, do they stay themselves, —Yahweh of hosts, is his name.
ku da kuke kiran kanku’yan ƙasar birni mai tsarki kuna kuma dogara ga Allah na Isra’ila, Ubangiji Maɗaukaki ne sunansa,
3 Things in advance, of old, I declared, Yea out of mine own mouth, came they forth, that I might let them be known, —Suddenly, I wrought and they came to pass.
na nanata abubuwan da suka riga suka faru tuntuni, bakina ya yi shelar su na kuma sanar da su; sai nan da nan na aikata, suka kuma faru.
4 Because I knew that—Obstinate, thou wast, —And, a sinew of iron, was thy neck, And thy brow, brazen,
Gama na san yadda kuke da taurinkai; jijiyoyin wuyanku ƙarafa ne, goshinku tagulla ne.
5 therefore told I thee—in time past, Ere yet it came, I let thee hear, —Lest thou shouldest say Mine idol wrought them, Yea, my carved image and my molten image, commanded them!
Saboda haka na faɗa waɗannan abubuwa tuntuni; kafin su faru na yi shelarsu gare ku saboda kada ku ce, ‘Gumakana ne suka yi su; siffar itacena da allahn zinariyana ne ya ƙaddara su.’
6 Thou hast heard—see it whole, And will, ye, not tell? I have let thee hear new things—from the present time, Even secrets which ye knew not.
Kun riga kun ji waɗannan abubuwa; kuka gan su duka. Ba za ku yarda da su ba? “Daga yanzu zuwa gaba zan faɗa muku sababbin abubuwa, na ɓoyayyun abubuwan da ba ku sani ba.
7 Now, are they created, and not in time past, And, before to-day, thou hadst not heard of them, —Lest thou shouldest say, Lo! I knew them!
Yanzu an halicce su, ba da daɗewa ba; ba ku riga kun ji game da su kafin yau ba. Saboda haka ba za ku ce, ‘I, na san da su ba.’
8 Nay! thou hadst not heard, Nay! thou hadst not known, Nay! in time past, thine ear, was not opened, —For I knew that thou, wouldst be treacherous, Yea a transgressor from birth, hast thou been called.
Ba ku ji ko balle ku gane ba; tun da kunnenku bai buɗu ba. Tabbatacce na san yadda kun zama masu tayarwa; an kira ku’yan tawaye daga haihuwa.
9 For the sake of mine own Name, will I defer mine anger, And for my praise, will I restrain myself towards thee, —So as not to cut thee off.
Saboda girman sunana na jinkirta fushina; saboda girman yabona na janye shi daga gare ku, don dai kada a yanke ku.
10 Lo! I have refined thee, but not as silver, —I have tested thee, in a smelting-pot of affliction.
Duba, na tace ku, ko da yake ba kamar azurfa ba; na gwada ku cikin wutar wahala.
11 For mine own sake—for mine own sake, will I effectually work For how should it be profaned? And, my glory—to another, will I not give.
Saboda girmana, saboda girmana, na yi haka. Yaya zan ƙyale a ƙazantar da kaina? Ba zan raba ɗaukakata da wani ba.
12 Hearken unto me O Jacob, And Israel, my called one, —I, am, the Same I, the first, yea, I, the last:
“Ka kasa kunne gare ni, ya Yaƙub, Isra’ila, wanda na kira cewa, Ni ne shi; ni ne na farko ni ne kuma na ƙarshe.
13 Surely, mine own hand, founded the earth, And, my right hand, stretched out the heavens, —While I was calling unto them, they stood forth, at once
Hannuna ne ya kafa harsashen duniya, hannuna na dama kuma ya shimfiɗa sammai; sa’ad da na kira su, duka suka miƙe tsaye gaba ɗaya.
14 Assemble yourselves—all of you and hear, Who among them, hath told these things? he whom Yahweh loveth, will execute—His pleasure, on Babylon, And his stroke on the Chaldeans.
“Ku tattaru, dukanku ku kuma saurara, Wanne a cikin gumakan ya iya faɗa waɗannan abubuwa? Zaɓaɓɓen da Ubangiji yake ƙauna zai aikata nufinsa a kan Babilon; hannunsa zai yi gāba da Babiloniyawa.
15 I—I, have spoken, Yea I have called him, —I have brought him in, and he shall make prosperous his way.
Ni kaina, na faɗa; I, na kira shi. Zan kawo shi, zai kuma yi nasara a cikin aikinsa.
16 Draw ye near unto me—hear ye this, Not in advance in secret, have I spoken, From the very time it cometh into being, there, am I, —And, now, My Lord Yahweh hath sent me and his spirit.
“Ku zo kusa da ni ku kuma saurari wannan. “Daga farkon shela ban yi magana a ɓoye ba; a lokacin da ya faru, ina nan a wurin.” Yanzu kuwa Ubangiji Mai Iko Duka ya aiko ni, da Ruhunsa.
17 Thus saith Yahweh—Thy Redeemer, The Holy One of Israel, —I—Yahweh, am thy God, Teaching thee to profit, Guiding thee in the way thou shouldest go.
Ga abin da Ubangiji yana cewa, Mai Fansarku, Mai Tsarkin nan na Isra’ila ya ce, “Ni ne Ubangiji Allahnku, wanda ya koya muku abin da ya fi muku kyau, wanda ya muku hanyar da za ku bi.
18 Oh! that thou hadst hearkened to my commandments, —Then had been, like a river, thy prosperity, And, thy righteousness, like the waves of the sea:
Da a ce kawai za ku mai da hankali ga umarnaina, da salamarku ta zama kamar kogi, adalcinku kamar raƙuman teku.
19 Then had been, like the sand, thy seed, And, the offspring of thy body, like the grains thereof, —Neither cut off nor destroyed had been his name from before me.
Da zuriyarku ta zama kamar yashi,’ya’yanku kamar tsabar hatsin da ba a iya ƙidayawa; da ba za a taɓa yanke sunansu balle a hallaka su daga gabana ba.”
20 Come ye forth out of Babylon, Flee from among the Chaldeans, With triumphant voice, tell ye—let this be heard, Let it go forth as far as the end of the earth, —Say ye—Yahweh hath redeemed his servant Jacob!
Ku bar Babilon, ku gudu daga Babiloniyawa! Ku yi shelar wannan da sowa ta farin ciki ku kuma furta shi. Ku aika shi zuwa iyakokin duniya; ku ce, “Ubangiji ya fanshi bawansa Yaƙub.”
21 And they thirsted not, when, through dry places, he led them, Waters out of the rock, caused he to flow out to them, —Yea be cleft a rock and, there gushed out waters:
Ba su ji ƙishi ba sa’ad da ya bishe su a cikin hamada; ya sa ruwa ya malalo dominsu daga dutse; ya tsage dutse ruwa kuwa ya kwararo.
22 No well-being, saith Yahweh to the lawless,
“Babu salama ga mugaye” in ji Ubangiji.