< Isaiah 22 >

1 The oracle on the valley of vision, —What aileth thee, then, That thou art wholly gone up to the house-tops?
Abin da Allah ya faɗa game da Kwarin Wahayi. Mene ne ya dame ku a yanzu, da dukanku kuka hau kan rufin gidaje.
2 With tumults, art thou filled, thou citadel in commotion! city exultant! Thy slain, are Not the slain, of the sword, Nor the dead in battle.
Ya kai gari cike da hayaniya, Ya ke birnin tashin hankali da alkarya mai murna? Mutanenki ba su mutu ta wurin takobi ba, ba kuwa za su mutu a yaƙi ba.
3 All thy ruler, having fled, together, by the bow, are taken captive: All found in thee have been taken captive, together, Far away, have they fled.
Dukan shugabanninki sun gudu gaba ɗaya; an kama su ba tare da an yi amfani da baka ba. Dukanku da aka kama an kwashe ku ɗaurarru gaba ɗaya, kun gudu tun abokin gāba yana da nisa.
4 For this cause, I said—Look away from me, Bitterly, will I weep, —Do not press to comfort me, For the ruin of the daughter of my people.
Saboda haka na ce, “Ƙyale ni kurum; bari in yi kuka mai zafi. Kada ka yi ƙoƙarin ta’azantar da ni a kan hallakar mutanena.”
5 For a day of confusion and downtreading and perplexity, pertaineth to My Lord, Yahweh of hosts, in the valley of vision, an undermining of walls, and a crying for help to the mountain.
Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, yana da ranar giggicewa da tattakewa da banrazana a cikin Kwarin Wahayi, ranar ragargazawar katanga da ta yin kuka ga duwatsu.
6 Yea, Elam, beareth the quiver, With trains of men, [and] horsemen, —And, Kir, hath uncovered the shield.
Elam ya ɗauki kwari da baka, tare da mahayan kekunan yaƙinta da dawakai; Kir ta buɗe garkuwoyi.
7 And it hath come to pass that the choice of thy vales, are full of chariots; Yea, the horsemen, have set themselves, in array, at the gate.
Kwarurukanku mafi kyau sun cika da kekunan yaƙi, an kuma tsai da mahayan dawakai a ƙofofin birni.
8 Then removed he the veil of Judah, —Yea thou didst peer on that day, into the armoury of the forest-house;
An rurrushe kāriyar Yahuda, a ranan nan kuwa kun yi la’akari da makamai a cikin Fadan Kurmi;
9 And the breaches in the city of David, ye beheld for they were many, —So ye gathered together the waters of the lower pool;
kuka ga cewa Birnin Dawuda tana da wuraren kāriya masu yawa da suka tsattsage; kuka tattara ruwa a Tafkin Ƙasa.
10 And the houses of Jerusalem, ye counted, —And brake down the houses, to fortify the wall;
Kuka ƙirga gine-gine a Urushalima kuka kuma rurrushe gidaje don ku ƙarfafa katanga.
11 And a reservoir, ye made between the two walls, for the waters of the ancient pool, —And had no regard unto him that made it, Nor unto him that formed it long ago, had ye respect.
Kuka gina matarar ruwa tsakanin katanga biyu saboda ruwan Tsohon Tafki, amma ba ku yi la’akari da Wannan da ya yi su ba, ko ku kula da Wannan da ya shirya shi tuntuni.
12 And, when My Lord Yahweh of hosts called in that day, —for weeping, and for lamentation, and for shaving bare and for girding with sackcloth,
Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki ya kira ku a wannan rana don ku yi kuka ku yi ihu, don ku aske gashinku ku kuma sa tsummoki.
13 Then lo! joy and rejoicing, killing oxen and slaughtering sheep, eating flesh and drinking wine, —Let us eat and drink, For to-morrow, we may die!
Amma duba, sai ga shi kuna farin ciki kuna kuma murna, kuna yankan shanu kuna kashe tumaki, kuna cin nama kuna kuma shan ruwan inabi! Kuna cewa, “Bari mu ci mu kuma sha, gama gobe za mu mutu!”
14 Therefore did Yahweh reveal himself in mine ears. Surely there shall be no propitiatory-covering put over this iniquity for you until ye die, Saith My Lord Yahweh of hosts.
Ubangiji Maɗaukaki ya bayyana wannan a kunnena cewa, “Har ranar mutuwarka ba za a yi kafarar wannan zunubi ba,” in ji mai girma Ubangiji Maɗaukaki.
15 Thus, said My Lord Yahweh, of hosts, Come go in unto this steward, Unto Shebna, who is over the house:
Ga abin da Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, ya faɗa, “Je, ka faɗa wa wannan mai hidima, Shebna, sarkin fada.
16 What doest thou here? And whom hast thou here? That thou hast hewn for thyself here a sepulchre, —As one hewing on high his sepulchre, Cutting out in the cliff a habitation for himself?
Mene ne kake yi a nan kuma wa ya ba ka izini ka haƙa kabari wa kanka a nan, kana fafe kabarinka a bisa kana sassaƙa wurin hutunka a dutse?
17 Lo! Yahweh, is about to hurl thee, with a hurl, O mighty man, —And roll thee with a roll;
“Ka yi hankali, Ubangiji yana shirin ya kama ka da ƙarfi ya kuma ɗauke ka, ya kai mai ƙarfi.
18 He will, toss, thee, with a toss, like a ball, into a country wide on both hands, —There, shalt thou die, And there shall thy glorious chariots be the contempt of the house of thy lord.
Zai dunƙule ka kamar ƙwallo ya jefa ka a cikin ƙasa mai girma. A can za ka mutu a can kuma kekunan yaƙinka masu daraja za su kasance, abin kunya kake ga gidan maigidanka!
19 Thus will I thrust thee out from thine office, —And from thy station, shall one tear thee down.
Zan tumɓuke ka daga makaminka, za a kuma kore ka daga matsayinka.
20 And it shall come to pass in that day, That I will call for my servant, for Eliakim son of Hilkiah,
“A wannan rana zan kira bawana, Eliyakim ɗan Hilkiya.
21 And will clothe him with thy tunic And with thy girdle, will I gird him, And thine authority, will I deliver into his hand, —So shall he become a father To the inhabitant of Jerusalem and To the house of Judah.
Zan rufe shi da rigarka in kuma yi masa ɗamara in miƙa masa ikonka. Zai zama mahaifi ga waɗanda suke zama a Urushalima da kuma gidan Yahuda.
22 And I will lay the key of the house of David upon his shoulder, —And he shall open and none shall shut, And shut and none shall open;
Zan sa mabuɗin gidan Dawuda a kafaɗarsa; abin da ya buɗe ba mai rufewa, kuma abin da ya rufe ba mai buɗewa.
23 And I will fasten him as a peg in a sure place, —And he shall become a throne of glory, to the house of his father;
Zan kafa shi kamar turke a tsayayyen wuri; zai zama mazaunin daraja domin gidan mahaifinsa.
24 And they shall hang upon him all the weight of his father’s house—The offshoots and the side-twigs—All the small vessels, Both the cups and all the jugs
Dukan ɗaukakar iyalinsa za tă rataya a kansa daga’ya’yansa da zuriyarsa har zuwa dukan ƙananan kayan aikinsa, wato, daga kwanoni har zuwa tuluna.
25 In that day, —Declareth Yahweh of hosts Shall the peg, give way, that was fastened in a sure place, —Yea it shall be cut off and fall And the burden that was upon it shall perish, For, Yahweh, hath spoken!
“A ranan nan, in ji Ubangiji Maɗaukaki, turken da aka kafa a tsayayyen wuri zai sumɓule; za a sare shi ya fāɗi, za a kuma datse nauyin da yake rataya a kansa.” Ni Ubangiji na faɗa.

< Isaiah 22 >