< Hosea 11 >

1 When Israel was, a child, then I loved him, —and, out of Egypt, called I my son.
“Sa’ad da Isra’ila yake yaro, na ƙaunace shi, daga Masar kuma na kira ɗana.
2 They invited them, —at once, they departed from before me, they, to the Baals, sacrificed, and, to the images, offered incense.
Amma yawan kiran da na yi wa Isra’ila haka nesa da ni da suke ta yi. Suka miƙa hadaya ga Ba’al suka kuma ƙona turare ga siffofi.
3 Yet, I, had taught Ephraim to walk, I used to take them upon mine arms, —But they acknowledged not that I had healed them.
Ni ne na koya wa Efraim tafiya ina kama su da hannu; amma ba su gane cewa ni ne na warkar da su ba.
4 With human cords, used I to draw them, with the bands of love, so became I unto them like those who remove the yoke [that was] on their jaws, —and, holding out [food] to him, I let him eat.
Na bishe su da linzamin alheri da tausayi, da ragamar ƙauna; Na cire karkiya daga wuyansu na kuma rusuna na ciyar da su.
5 He was not to turn back into the land of Egypt, Howbeit, the Assyrian—he, became his king, for they refused to turn.
“Ba za su koma Masar ba Assuriya kuma ba za tă yi mulki a bisansu ba saboda sun ƙi su tuba ba?
6 Therefore shall the sword, rage, in his cities, and make an end of his multitudes, and consume them, —because of their counsels.
Takuba za su yi ta wulgawa a biranensu, za su hallaka sandunan ƙarafan ƙofofinsu su kuma kawo ƙarshen ƙulle-ƙullensu.
7 But, my people, are bent towards turning from me, though upwards they call them, none of them can lift them.
Mutanena sun ƙudura su juye daga gare ni. Ko da ma suka yi kira ga Mafi Ɗaukaka, ta ko ƙaƙa ba zai girmama su ba.
8 How can I give thee up, Ephraim? abandon thee Israel? How can I make thee as Admah? set thee as Zeboim? Mine own heart, turneth against me, at once, are kindled my compassions.
“Yaya zan ba da kai, Efraim? Yaya zan miƙa ka, Isra’ila? Yaya zan yi da kai kamar Adma? Yaya zan yi da kai kamar Zeboyim? Zuciyata ta canja a cikina; dukan tausayina ya huru.
9 I cannot execute the glow of mine anger, I cannot turn to destroy Ephraim, —for, GOD, am, I, and not man, When thou drawest near, [I am] a Holy One, though I do not enter a city.
Ba zan zartar da fushina mai zafi ba, ba kuwa zan juya in ragargaza Efraim ba. Gama ni Allah ne, ba mutum ba, Mai Tsarki a cikinku. Ba zan zo cikin fushi ba.
10 After Yahweh, let them go, Like a lion, will he roar, —When, he, shall roar, then let sons, come trembling, out of the West.
Za su bi Ubangiji; zai yi ruri kamar zaki. Sa’ad da ya yi ruri,’ya’yansa za su zo da rawan jiki daga yamma.
11 Let them come trembling like a small bird out of Egypt, and like a dove out of the land of Assyria, —so will I cause them to dwell by their own houses, Declareth Yahweh.
Za su zo da rawan jiki kamar tsuntsaye daga Masar, kamar kurciyoyi daga Assuriya. Zan zaunar da su a cikin gidajensu,” in ji Ubangiji.
12 They have compassed me about—with denial, Ephraim, with deceit, the house of Israel, —but, Judah, hath, again and again, run riot with GOD, though, with the holy places, entrusted.
Mutanen Efraim sun kewaye ni da ƙarairayi, gidan Isra’ila da ruɗu. Mutanen Yahuda kuma suna yi wa Allah ƙin ji, har ma a kan Mai Tsarkin nan mai aminci.

< Hosea 11 >