< Genesis 29 >
1 Then Jacob lifted up his feet, —and went his way towards the land of the sons of the East.
Sa’an nan Yaƙub ya ci gaba da tafiyarsa har ya kai ƙasar mutanen gabashi.
2 And he looked, and lo! a well, in the field and lo! there, three flocks of sheep, lying down near it, for out of that well, do they water the flocks, but, the stone, is great, on the mouth of the well:
A can ya ga rijiya a jeji da garkuna uku na tumaki kwance kusa da ita, gama a wannan rijiya ce ake shayar da garkuna. Dutsen da ake rufe bakin rijiyar mai girma ne.
3 so they gather together thither all the flocks, and roll away the stone from off the mouth of the well, and water the sheep, —and put back the stone upon the mouth of the well, to its place.
Sa’ad da dukan garkuna suka taru a can, sai makiyayan su gungurar da dutsen daga bakin rijiyar su shayar da tumaki. Sa’an nan su mai da dutsen a wurinsa a bakin rijiya.
4 And Jacob said to them, My brethren, whence are ye? And they said: From haran, are we.
Yaƙub ya tambayi makiyayan ya ce, “’Yan’uwa, ina kuka fito?” Suka amsa, “Mu daga Haran ne.”
5 And he said to them, Know ye Laban, son of Nahor? And they said, We know him.
Sai ya ce musu, “Kun san Laban, jikan Nahor?” Suka amsa, “I, mun san shi.”
6 And he said to them, Is it well with him? And they said, Well, but lo! Rachel his daughter, coming in with the sheep.
Sa’an nan Yaƙub ya tambaye su, “Yana nan lafiya?” Suka ce, “I, yana lafiya, ga ma’yarsa Rahila tafe da tumaki.”
7 And he said Lo! the day is yet high, it is not time for gathering together the cattle, —water the sheep, and go feed.
Ya ce, “Duba har yanzu da sauran rana da yawa, lokaci bai kai na tara garkuna ba. Ku shayar da tumaki ku mai da su wurin kiwo.”
8 And they said, We cannot, until that all the flocks are gathered together, and they roll away the stone, from off the mouth of the well, —and then can we water the sheep.
Suka amsa suka ce, “Ba za mu iya ba, sai dukan garkunan sun taru, aka kuma gungurar da dutsen daga bakin rijiyar. Sa’an nan za mu shayar da tumakin.”
9 While yet he was speaking with them, Rachel, had come in with the sheep which belonged to her father, for a shepherdess, was she.
Tun yana cikin magana da su, sai ga Rahila ta zo da tumakin mahaifinta, gama ita makiyayyiya ce.
10 And it came to pass when Jacob saw Rachel daughter of Laban, his mother’s brother, and the sheep of Laban, his mother’s brother, that Jacob went near, and rolled away the stone from off the mouth of the well, and watered the sheep of Laban his mother’s brother,
Sa’ad da Yaƙub ya ga Rahila’yar Laban, ɗan’uwan mahaifiyarsa, da tumakin Laban, sai ya tafi ya gungurar da dutsen daga bakin rijiyar, ya kuma shayar da tumakin kawunsa.
11 And Jacob kissed Rachel, —and lifted up his voice, and wept.
Sa’an nan Yaƙub ya sumbaci Rahila, ya kuma ɗaga murya ya yi kuka.
12 And when Jacob told Rachel that he was her father’s brother, and that he was Rebekah’s son, then ran she, and told her father.
Ya riga ya faɗa wa Rahila cewa shi dangin mahaifinta ne kuma ɗan Rebeka. Saboda haka ta ruga da gudu ta faɗa wa mahaifinta.
13 And it came to pass when Laban heard the tidings of Jacob his sister’s son, that he ran to meet him, and embraced him, and fondly kissed him, and brought him into his house, —when he recounted to Laban all these things.
Nan da nan, da Laban ya sami labari game da Yaƙub, ɗan’yar’uwarsa, ya gaggauta yă sadu da shi. Sai ya rungume shi ya sumbace shi, ya kuma kawo shi gidansa, a can kuwa Yaƙub ya faɗa masa dukan waɗannan abubuwa.
14 And Laban said to him, Surely, my bone and my flesh, art thou. So he abode with him a month of days.
Sa’an nan Laban ya ce masa, “Kai nama da jinina ne.” Bayan Yaƙub ya zauna da shi na wata guda cif,
15 Then said Laban to Jacob, Is it because my brother, thou art, that thou shouldst serve me for naught? Come tell me! What shall be thy wages?
sai Laban ya ce masa, “Don kawai kai dangina ne na kusa, sai kawai ka yi mini aiki a banza? Faɗa mini abin da albashinka zai zama.”
16 Now, Laban, had two daughters, —the name of the elder, Leah, and the name of the younger, Rachel,
Laban dai yana da’ya’ya mata biyu; sunan babbar Liyatu, sunan ƙaramar kuwa Rahila.
17 But, the eyes of Leah were weak, —whereas, Rachel, was comely in form and comely in countenance.
Liyatu tana da raunannun idanu, amma Rahila dai tsarinta yana da kyau kuma kyakkyawa ce.
18 So Jacob loved Rachel, —and he said, I will serve thee seven years, for Rachel thy younger daughter.
Yaƙub ya ƙaunaci Rahila, sai ya ce, “Zan yi maka aiki na shekaru bakwai domin ƙaramar’yarka Rahila.”
19 And Laban said, Better that I give her to thee, than that I should give her to another man, —Abide with me!
Laban ya ce, “Ya fi kyau in ba ka ita, da in ba wani mutum dabam. Zauna tare da ni.”
20 So Jacob served for Rachel—seven years, —and they became, in his eyes, as single days, for his love to her.
Saboda haka Yaƙub ya yi bauta shekaru bakwai domin a ba shi Rahila, amma shekarun suka zama kamar’yan kwanaki ne kawai gare shi saboda ƙaunar da yake mata.
21 Then said Jacob unto Laban: Come give me my wife, for fulfilled are my days, —that I may go in unto her.
Sa’an nan Yaƙub ya ce wa Laban, “Ba ni matata. Lokacina ya cika, ina kuma so in kwana da ita.”
22 So Laban gathered together all the men of the place and made a banquet,
Saboda haka Laban ya tara dukan mutanen wurin, ya yi biki.
23 And it came to pass in the evening, that he took Leah his daughter and brought her in unto him, —and he went in unto her.
Amma da yamma ta yi, sai ya ɗauki’yarsa Liyatu ya ba da ita ga Yaƙub, sai Yaƙub ya kwana da ita.
24 And Laban gave her Zilpah, his handmaid, unto Leah his daughter. as handmaid.
Laban kuma ya ba da baranyarsa Zilfa wa’yarsa tă zama mai hidimarta.
25 And it came to pass in the morning, that lo! it was Leah, —and he said unto Laban, What is this thou hast done to me? Was it not, for Rachel, I served with thee? Wherefore then hast thou deceived me?
Sa’ad da safiya ta yi, sai ga Liyatu! Saboda haka Yaƙub ya ce wa Laban, “Mene ne ke nan ka yi mini? Na yi maka bauta domin Rahila, ba haka na yi ba? Don me ka ruɗe ni?”
26 And Laban said, It must not be done so in our place, —to give the later-born before the firstborn.
Laban ya amsa, “Ba al’adarmu ba ce a nan a ba da’ya ƙarama aure kafin’yar fari.
27 Fulfil the week of this one, —then must we give thee, the other one also, for the service wherewith thou shalt serve with me, yet seven years more.
Ka gama makon amaryanci na’yar nan; sa’an nan za mu ba ka ƙaramar ita ma, don ƙarin waɗansu shekaru bakwai na aiki.”
28 And Jacob did so, and fulfilled the week of this one, —and he gave him Rachel his daughter—to him to wife.
Haka kuwa Yaƙub ya yi. Ya gama mako guda da Liyatu, sa’an nan Laban ya ba shi’yarsa Rahila tă zama matarsa.
29 And Laban gave to Rachel his daughter Bilhah his handmaid, —to be hers as a handmaid.
Laban ya ba da baranyarsa Bilha wa’yarsa Rahila ta zama mai hidimarta.
30 So he went in, unto Rachel also, and loved, Rachel also, more than Leah, —and he served with him, yet seven years more.
Yaƙub ya kwana da Rahila ita ma, ya kuwa ƙaunaci Rahila fiye da Liyatu. Ya kuma yi wa Laban aiki na ƙarin waɗansu shekaru bakwai.
31 And, when Yahweh saw that Leah was hated, he granted her to bear children, —whereas, Rachel, was barren.
Sa’ad da Ubangiji ya ga ba a ƙaunar Liyatu, sai ya buɗe mahaifarta, amma Rahila ta zama bakararriya.
32 So Leah conceived, and bare a son, and called his name Reuben, —for she said, Because, Yahweh hath looked upon my humiliation, For, now, will my husband love me.
Sai Liyatu ta yi ciki ta haifi ɗa. Ta sa masa suna Ruben, gama ta ce, “Domin Ubangiji ya ga wahalata. Tabbatacce mijina zai ƙaunace ni yanzu.”
33 And she conceived again, and bare a son, and said. Because Yahweh heard that, I, was hated, he gave me, this one also. So she called his name Simeon.
Ta sāke yin ciki, sa’ad da kuma ta haifi ɗa sai ta ce, “Gama Ubangiji ya ji cewa ba a ƙaunata, ya ba ni wannan shi ma.” Saboda haka ta ba shi suna Simeyon.
34 And she conceived again and bare a son, and said, Now—this time, will my husband be bound unto me, For I have borne him three sons, —For this cause, called she his name Levi.
Har yanzu ta yi ciki, sa’ad da kuma ta haifi ɗa sai ta ce, “Yanzu, a ƙarshe mijina zai manne mini, gama na haifa masa’ya’ya maza uku.” Saboda haka ta ba shi suna Lawi.
35 And she conceived again and bare a son, and said This time, will I praise Yahweh, For which cause, she called his name Judah. And she left off bearing.
Ta sāke yin ciki, sa’ad da ta haifi ɗa sai ta ce, “A wannan lokaci zan yabi Ubangiji.” Saboda haka ta ba shi suna Yahuda. Sa’an nan ta daina haihuwa.