< Genesis 13 >
1 So Abram came up out of Egypt he and his wife and all that he had and Lot with him, towards the South.
Saboda haka Abram ya haura daga Masar zuwa Negeb tare da matarsa, da dukan abin da yake da shi tare da Lot.
2 Now, Abram, was very rich, —in cattle, in silver and in gold.
Abram ya azurta ƙwarai da dabbobi, da azurfa, da kuma zinariya.
3 And he went his way, by his removals, from the South even as far as to Bethel, —as far as the place where his tent was at the beginning, between Bethel and Ai:
Daga Negeb, ya ci gaba da tafiyarsa a wurare dabam-dabam har ya kai tsakanin Betel da Ai, a inda dā ya kafa tentinsa na fari
4 unto the place of the altar, which he made there at first, —and Abram called there, on the name of Yahweh.
da kuma inda dā ya gina bagade. A can Abram ya kira bisa sunan Ubangiji.
5 Now, Lot also, who was going with Abram, had flocks and herds and tents.
Lot wanda yake tafiya tare da Abram, shi ma yana da garken shanu da tumaki da kuma tentuna.
6 And the land suffered them not to dwell together, —because their substance had become, great, so that they could not dwell together.
Wannan ya sa har ƙasar ba tă ishe su yayinda suke zama tare ba, saboda mallakarsu ta yi yawa har ba za su iya zama tare ba.
7 And there arose a strife betwixt the herdmen of Abram, and the herdmen of Lot. Now the Canaanite and the Perizzite, were then dwelling in the land.
Rikici kuma ya tashi tsakanin masu kiwon dabbobin Abram da na Lot. Mazaunan ƙasar, a lokacin kuwa Kan’aniyawa da Ferizziyawa ne.
8 So then Abram said unto Lot Pray let not cause of strife arise betwixt me and thee, or betwixt my herdmen and thy herdmen; for brethren, are we.
Saboda haka Abram ya ce wa Lot, “Kada mu bar rikici yă shiga tsakaninmu, ko kuma tsakanin masu kiwon dabbobinka da nawa, gama mu’yan’uwa ne.
9 Is not, all the land, before thee? I pray thee, separate thyself from me, —if to the left hand, then I will go to the right, if to the right hand, then I will go to the left.
Ba ga dukan ƙasar tana gabanka ba? Bari mu rabu. In ka yi hagu sai ni in yi dama. In ka yi dama, sai ni in yi hagu.”
10 So Lot lifted up his eyes and beheld all the circuit of the Jordan, that the whole of it, was well-watered, —before Yahweh destroyed Sodom and Gomorrah, like the Garden of Yahweh, like the land of Egypt, as thou enterest into Zoar.
Lot ya ɗaga idanunsa sama ya dubi kwarin Urdun, sai ya ga kwarin yana da ciyawa mai kyau ƙwarai sai ka ce lambun Ubangiji, kamar ƙasar Masar, wajajen Zowar. (Wannan fa kafin Ubangiji yă hallaka Sodom da Gomorra.)
11 And Lot chose for himself all the circuit of the Jordan, so Lot brake up eastwards, —and they separated themselves, each man from his brother:
Saboda haka sai Lot ya zaɓar wa kansa dukan kwarin Urdun, ya tashi ya nufi wajen gabas. Haka fa suka rabu da juna.
12 Abram, fixed his dwelling in the land of Canaan, —but, Lot, fixed his dwelling among the cities, of the circuit, and moved his tent as far as Sodom.
Abram ya zauna a ƙasar Kan’ana, yayinda Lot ya zauna cikin biranen kwari, ya kafa tentunansa kusa da Sodom.
13 Now, the men of Sodom were base and sinful, —against Yahweh, exceedingly.
Mutanen Sodom kuwa mugaye ne, sun aikata zunubi ƙwarai ga Ubangiji.
14 And, Yahweh, said unto Abram after that Lot had separated himself from him, Lift up, I pray thee thine eyes and look, from the place where thou art, —northward and southward and eastward and westward;
Bayan Lot ya rabu da Abram, sai Ubangiji ya ce wa Abram, “Ɗaga idanunka daga inda kake, ka dubi arewa da kudu, gabas da yamma.
15 for all the land which thou art beholding—to thee, will I give it, and to thy seed unto times age-abiding;
Dukan ƙasar da kake gani zan ba ka, kai da zuriyarka har abada.
16 and I will make thy seed as the dust of the earth, —so that if a man can number the dust of the earth, thy seed also, may be numbered.
Zan sa zuriyarka tă yi yawa kamar ƙurar ƙasa, har in wani yana iya ƙidaya ƙurar, to, za a iya ƙidaya zuriyarka.
17 Rise! go up and down in the land, to the length thereof and to the breadth thereof, for to thee, will I give it.
Tafi, ka ratsa tsawo da fāɗin ƙasar, gama zan ba ka ita.”
18 So Abram moved his tent and came in and dwelt among the oaks of Mamre, which were in Hebron, —and built there an altar to Yahweh.
Saboda haka Abram ya cire tentunansa, ya zo ya zauna kusa da manyan itatuwan Mamre a Hebron, inda ya gina bagade ga Ubangiji.