< Genesis 12 >
1 And Yahweh said unto Abram: Come thou on thy way, Out of thy land and out of the place of thy birth and out of the house of thy father, —Unto the land that I will show thee;
Ubangiji ya ce wa Abram, “Tashi ka bar ƙasarka, da mutanenka, da iyalin mahaifinka, ka tafi ƙasar da zan nuna maka.
2 That I may make thee into a great nation, And bless thee and make great thy name, And become thou a blessing;
“Zan mai da kai al’umma mai girma, zan kuma albarkace ka; zan sa sunanka yă zama mai girma, ka kuma zama sanadin albarka.
3 That I may bless them who bless thee, But him who maketh light of thee, will I curse, —So shall be, blessed in thee, all the families of the ground.
Zan albarkaci duk wanda ya albarkace ka, in kuma la’anci duk wanda ya la’anta ka, dukan mutanen duniya za su sami albarka ta wurinka.”
4 And Abram came on his way, according to that which Yahweh had spoken unto him, and Lot came with him, —now, Abram, was seventy-five years old, when he came forth out of Haran.
Saboda haka Abram ya tashi yadda Ubangiji ya faɗa masa; Lot ma ya tafi tare da shi. Abram yana da shekaru 75, sa’ad da ya tashi daga Haran.
5 And Abram took Sarai his wife, and Lot his brother’s son, with all the goods that they had gathered and the souls that they had gained in Haran, —and they came forth to go towards the land of Canaan, and came in to the land of Canaan.
Abram ya ɗauki matarsa Saira da Lot ɗan ɗan’uwansa, da dukan mallakar da suka tattara, da kuma mutanen da suka samu a Haran, suka kama hanya zuwa ƙasar Kan’ana.
6 And Abram passed along throughout the land, as far as the place of Shechem as far as the Teacher’s Terebinth, the Canaanite being then in the land.
Abram ya ratsa ƙasar har zuwa wurin babban itace na More a Shekem. A lokacin Kan’aniyawa suna a ƙasar.
7 And Yahweh appeared unto Abram, and said: To thy seed, will I give this land, —And he built there an altar, unto Yahweh who appeared unto him.
Ubangiji ya bayyana ga Abram ya ce, “Ga zuriyarka ne zan ba da wannan ƙasa.” Saboda haka Abram ya gina bagade a can ga Ubangiji, wanda ya bayyana gare shi.
8 And he moved on from thence towards the hill country, on the east of Bethel and pitched his tent, —with Bethel on the west, and Ai on the east, and built there an altar to Yahweh, and called on the name of Yahweh.
Daga can, ya ci gaba zuwa wajen tuddai a gabashin Betel ya kafa tentinsa, Betel yana yamma, Ai, kuma a gabas. A can ya gina bagade ga Ubangiji ya kuma kira bisa sunan Ubangiji.
9 Thus Abram brake up, again and again, towards the South.
Sa’an nan Abram ya tashi ya ci gaba da tafiya zuwa wajen Negeb.
10 And it came to pass that there was a famine, in the land, —so Abram went down towards Egypt, to sojourn there, because grievous, was the famine in the land.
To, a lokacin, an yi yunwa a ƙasar, sai Abram ya gangara zuwa Masar don yă zauna a can na ɗan lokaci, domin yunwa ta yi tsanani.
11 And it came to pass when he had come near to enter into Egypt, that he said unto Sarai his wife: Behold! I beseech thee I know that a woman fair to look on, thou art:
Yayinda yana gab da shiga Masar, sai ya ce wa matarsa Saira, “Na sani ke kyakkyawar mace ce.
12 so will it come to pass when the Egyptians behold thee, that they will say, His wife, this! and will slay me while thee, they preserve alive.
Sa’ad da Masarawa suka ganki, za su ce, ‘Wannan matarsa ce.’ Za su kuwa kashe ni, su bar ki da rai.
13 Say, I beseech thee that my sister, art thou, —to the end it may be well with me for thy sake, so shall my soul be preserved alive because of thee.
Saboda haka ki ce ke’yar’uwata ce, domin ta dalilinki a mutunta ni, a kuma bar ni da rai.”
14 And so it was when Abram entered into Egypt, the Egyptians beheld the woman, that fair, was she exceedingly.
Sa’ad da Abram ya isa Masar, Masarawa suka ga cewa Saira kyakkyawa mace ce ƙwarai.
15 And the princes of Pharaoh beheld her, and praised her unto Pharaoh, —so the woman was taken to the house of Pharaoh;
Sa’ad da fadawan Fir’auna suka gan ta kuwa, sai suka yabe ta wajen Fir’auna, aka kuwa kawo ta cikin fadarsa.
16 and with Abram, dealt he well for her sake, —so that he came to have flocks and herds and he-asses, and men-servants, and maid-servants, and she-asses and camels.
Ya mutunta Abram sosai saboda ita, Abram kuwa ya mallaki tumaki da shanu, da jakuna maza da mata, da bayi maza da mata, da kuma raƙuma.
17 And Yahweh plagued Pharaoh with great plagues, also his house, —for the matter of Sarai, wife of Abram.
Amma Ubangiji ya wahalar da Fir’auna da gidansa da cututtuka masu zafi saboda Saira, matar Abram.
18 And Pharaoh called out to Abram, and said, What is this thou hast done to me? Wherefore didst thou not tell me, that she was, thy wife?
Saboda haka Fir’auna ya kira Abram ya ce, “Me ke nan ka yi mini? Me ya sa ba ka faɗa mini cewa ita matarka ce ba?
19 Wherefore saidst thou My sister, she; and so I was about to take her to me, to wife? But now, lo! thy wife take her and go thy way.
Don me ka ruɗe ni cewa, ‘Ita’yar’uwata ce,’ har na ɗauke ta tă zama matata? To, ga matarka. Ɗauke ta ka tafi.”
20 And Pharaoh gave command concerning him unto certain men, —and sent him away, with his wife and all that he had.
Sa’an nan Fir’auna ya yi wa mutanensa umarni a kan Abram, suka kuwa sallame shi tare da matarsa da kuma dukan abin da yake da shi.