< Deuteronomy 5 >
1 Then called Moses unto all Israel and said unto them—Hear, O Israel, the statutes and the regulations, which I am speaking in your ears to-day, —so shall ye learn them, and observe to do them.
Musa ya tattara dukan Isra’ila ya ce, Ku ji, ya Isra’ila, ƙa’idodi da dokokin da na furta a kunnuwanku a yau. Ku koye su, ku kuma tabbata kun bi su.
2 Yahweh our God, solemnised with us a covenant in Horeb:
Ubangiji Allahnmu ya yi alkawari da mu a Horeb.
3 not with our fathers did Yahweh solemnise this covenant, —but with us, ourselves—these here to-day, all of us living.
Ba da kakanninmu ba ne Ubangiji ya yi wannan alkawari, amma da mu ne, da dukanmu waɗanda muke da rai a yau.
4 Face to face, spake Yahweh with you in the mount out of the midst of the fire,
Ubangiji ya yi magana fuska da fuska da ku daga wuta a kan dutse.
5 (I was standing between Yahweh and you, at that time, to declare unto you the word of Yahweh, —for ye shrank with fear from the presence of the fire, and went not up in the mount) saying: —
(A wannan lokaci na tsaya tsakanin Ubangiji da ku, don in furta muku maganar Ubangiji, domin kun ji tsoron wutar, ba ku kuwa hau dutsen ba.) Ya ce,
6 I, am Yahweh thy God, who have brought thee forth out of the land of Egypt out of the house of servants: —
“Ni ne Ubangiji Allahnka, wanda ya fitar da ku daga Masar, daga ƙasar bauta.
7 Thou shalt not have other gods, besides me:
“Ba za ka kasance da waɗansu alloli a gabana ba.
8 Thou shalt not make unto thee an image, any form that is in the heavens above, or that is in the earth beneath or that is in the waters beneath the earth:
Ba za ka yi wa kanka gunki, ko wata siffar abin da take a sama a bisa, ko siffar abin da yake a duniya a ƙasa, ko siffar abin da yake a cikin ruwa a ƙarƙashin ƙasa ba.
9 thou shalt not bow thyself down to them nor be led to serve them, —for, I Yahweh thy God, am a jealous GOD, visiting the iniquity of fathers upon sons even unto three generations and unto four, unto them that hate me;
Ba za ka rusuna musu, ko ka yi musu sujada ba. Gama Ni, Ubangiji Allahnka, Allah ne mai kishi, nakan hukunta’ya’ya saboda zunuban iyaye har tsara ta uku da ta huɗu na waɗanda suka ƙi ni.
10 but shewing lovingkindness unto a thousand generation—unto them who love me, and keep my commandments:
Amma nakan nuna ƙauna ga dubban tsararraki na waɗanda suke ƙaunata, suke kuma kiyaye dokokina.
11 Thou shalt not utter the name of Yahweh thy God, for falsehood, —for Yahweh will not let him go unpunished who uttereth his name for falsehood:
Ba za ka yi amfani da sunan Ubangiji Allahnka a banza ba, gama Ubangiji zai ba wa duk mai yin amfani da sunansa a banza laifi.
12 Observe the sabbath day, to hallow it, —as Yahweh thy God, hath commanded thee:
Ka kiyaye ranar Asabbaci ta wurin kiyaye ta da tsarki, yadda Ubangiji Allahnka ya umarce ka.
13 six days, shalt thou labour, and do all thy work;
Kwanaki shida za ka yi aiki, ka kuma yi dukan aikinka,
14 but, the seventh day, is a sabbath unto Yahweh thy God, —thou shalt do no work—thou nor thy son nor thy daughter nor thy servant nor thy handmaid nor thine ox nor thine ass nor any of thy cattle, nor thy sojourner who is within thy gates, that thy servant and thy handmaid may rest, as well as thou.
amma rana ta bakwai, Asabbaci ne ga Ubangiji Allahnka. A kanta ba za ka yi wani aiki ba, ko kai, ko ɗanka, ko’yarka, ko bawanka, ko baiwarka, ko saniyarka, ko jakinka, ko wani daga dabbobinka, ko baƙo a ƙofofinka, don bayinka maza da mata su ma su huta, kamar ka.
15 So shalt thou remember that a servant, wast thou in the land of Egypt, and that Yahweh thy God brought thee forth from thence, with a firm hand, and with a stretched-out arm, —for this cause, hath Yahweh thy God commanded thee to keep the sabbath day:
Ka tuna fa, dā kai bawa ne a ƙasar Masar amma Ubangiji Allahnka ya fitar da kai daga can da iko da kuma ƙarfi. Saboda haka Ubangiji Allahnka ya umarce ka ka kiyaye ranar Asabbaci.
16 Honour thy father and thy mother, as Yahweh thy God hath commanded thee, —that thy days may be prolonged and that it may go well with thee, upon the soil which Yahweh thy God is about to give unto thee:
Ka ba da girma ga mahaifinka da mahaifiyarka, yadda Ubangiji Allahnka ya umarce ka, don ka yi tsawon rai, ka kuma sami zaman lafiya a ƙasar da Ubangiji Allahnka yake ba ka.
17 Thou shalt not commit murder:
Kada ka yi kisankai.
18 Neither shalt thou commit adultery:
Kada ka yi zina.
19 Neither shalt thou steal:
Kada ka yi sata.
20 Neither shalt thou testify against thy neighbour with a witness of falsehood:
Kada ka ba da shaidar ƙarya a kan maƙwabcinka.
21 Neither shalt thou covet thy neighbour’s wife, —neither shalt thou desire thy neighbour’s house, his field, or his servant, or his handmaid, his ox or his ass, or anything that is thy neighbour’s.
Kada ka yi ƙyashin matar maƙwabcinka. Kada kuma ka yi sha’awar gidan maƙwabcinka, ko gonarsa, ko bayinsa maza da mata, ko saniyarka, ko jakinsa, ko dai wani abin da yake na maƙwabtanka.”
22 These words, spake Yahweh unto all the convocation of you in the mount out of the midst of the fire the cloud and the thick gloom, a loud voice, and added not, —and he wrote them upon two tables of stone, and gave them unto me.
Waɗannan su ne dokokin da Ubangiji ya furta da babbar murya ga taronku gaba ɗaya, a can dutse ta tsakiyar wuta, girgije da kuma baƙin duhu; bai kuma ƙara kome ba. Sa’an nan ya rubuta su a kan alluna biyu na dutse, ya kuma ba ni su.
23 And it came to pass, when ye heard the voice out of the midst of the darkness, the mountain also burning with fire, then drew ye near unto me, even all the heads of your tribes and your elders,
Sa’ad da kuka ji muryar daga duhu, yayinda dutsen yana cin wuta, dukan manyan kabilanku da dattawanku suka zo wurina.
24 and ye said—Lo! Yahweh our God hath let us see his glory and his greatness, his voice also, have we heard out of the midst of the fire, —this day, have we seen, that God may speak with man who yet may live.
Kuka kuma ce, “Ubangiji Allahnmu ya nuna mana ɗaukakarsa da zatinsa, mun kuma ji muryarsa a tsakiyar wutar. A yau mun ga cewa mutum zai iya rayu idan ma Allah ya yi magana da shi.
25 Now, therefore why should we die? for this great fire, will consume, us, —if we ourselves, hear the voice of Yahweh our God any more, we shall die.
Amma yanzu, don me za mu mutu? Wannan wuta mai girma za tă cinye mu, za mu kuwa mutu in muka ci gaba da jin muryar Ubangiji Allahnmu.
26 For who [is there] of all flesh, that ever heard the voice of a Living God speaking out of the midst of fire as we, and yet lived?
Gama wanda ɗan adam ne ya taɓa jin muryar Allah mai rai yana magana daga wuta, kamar yadda muka ji, ya kuma tsira?
27 Go, thou, near, and hear, all that Yahweh our God shall say, —so shalt thou speak unto us, all that Yahweh our God shall speak unto thee and we will hear and do.
Kai, ka matsa kusa, ka saurara ga dukan abin da Ubangiji Allahnmu ya faɗa. Sa’an nan ka faɗa mana dukan abin da Ubangiji Allahnmu ya faɗa maka. Za mu saurara, mu kuma yi biyayya.”
28 And Yahweh heard the voice of your words, when ye spake unto me, —and Yahweh said unto me—I have heard the voice of the words of this people which they have spoken unto thee, they have well said all which they have spoken.
Ubangiji ya ji ku, sa’ad da kuka yi magana da ni, sai Ubangiji ya ce mini, “Na ji abin da wannan mutane suka faɗa maka. Abin da suka faɗa daidai ne.
29 Oh that this their heart might remain in them to revere me, and to keep all my commandments all the days, —that it might be well with them and with their sons unto times age-abiding.
Kash, da a ce zukatansu za su zama masu tsorona, su kuma kiyaye dukan dokokina kullum mana, saboda kome yă zama da lafiya gare su, da kuma’ya’yansu har abada!
30 Go, say unto them, —Return ye to your tents.
“Je, ka faɗa musu su koma tentunansu.
31 Thou, therefore here stand with me and let me speak unto thee—all the commandment and the statutes and the regulations which thou shalt teach them, —that they may do [them] in the land which I am giving unto them to possess it.
Kai kuwa ka tsaya a nan tare da ni saboda in ba ka umarnai, ƙa’idodi da kuma dokoki duka, da za ka koya musu don su bi a ƙasar da nake ba su, su mallaka.”
32 So then ye must observe to do, as Yahweh your God hath commanded you, —ye must not turn aside to the right hand or to the left.
Sai ku yi hankali don ku yi abin da Ubangiji Allahnku ya umarce ku; kada ku juya dama ko hagu.
33 In all the way which Yahweh your God hath commanded you, must ye walk, —that ye may live and it be well with you, and that ye may prolong your days in the land, which ye shall possess.
Ku yi tafiya cikin dukan hanyar da Ubangiji Allahnku ya umarce ku, saboda ku zauna, ku yi nasara, ku kuma yi tsawon rai a ƙasar da za ku mallaka.