< Daniel 9 >

1 In the first year of Darius son of Ahasuerus, of the seed of the Medes, —who was made king over the kingdom of the Chaldeans:
A shekara ta fari da mulkin Dariyus ɗan Zerzes (wanda yake Bamediye), wanda aka mai da shi sarki a masarautar Babiloniyawa
2 in the first year of his reign, I, Daniel, perceived by the writings, —the number of the years, as to which the word of Yahweh came unto Jeremiah the prophet, to fulfil the desolations of Jerusalem, seventy years.
a shekara ta farko ta mulkinsa, ni, Daniyel na gane daga cikin littattafai, bisa ga maganar Ubangiji da aka faɗa wa annabi Irmiya, cewa zaman Urushalima kango zai kai shekara saba’in.
3 So I set my face unto the Lord God, to seek [him] by prayer, and supplication, —with fasting, and sackcloth and ashes;
Sai na juya wurin Ubangiji Allah na roƙe shi ta wurin addu’a da koke-koke, cikin azumi, ina saye da tsummoki, na kuma zauna a cikin toka.
4 yea I prayed unto Yahweh my God, and made confession, —and said—I beseech thee, O Lord, the GOD great and to be revered, keeping the covenant and the lovingkindness, to them who love him, and to them who keep his commandments.
Na yi addu’a ga Ubangiji Allahna na furta laifina. “Ya Ubangiji, mai alfarma da kuma Allah mai banrazana, wanda yake cika alkawarinsa na ƙauna ga duk wanda ya ƙaunace shi ya kuma kiyaye dokokinsa,
5 We have sinned and committed iniquity, and been guilty of lawlessness and been rebellious, —even departing from thy commandments, and from thy regulations;
mun yi zunubi muka kuma yi ba daidai ba. Mu mugaye ne da kuma’yan tawaye; mun juya wa umarninka da shari’unka baya.
6 and have not hearkened unto thy servants the prophets, who spake in thy name, unto our kings, our rulers, and our fathers, —and unto all the people of the land.
Ba mu saurari bayinka annabawa ba, waɗanda suka yi magana a sunanka ga sarakunanmu da masu mulkinmu da iyayenmu, da kuma dukan mutanen ƙasa.
7 To thee, O Lord, belongeth righteousness, but, to us, the shame of faces, as at this day, —to the men of Judah, and to the inhabitants of Jerusalem, and to all Israel, the near and the far off, throughout all the lands whither thou hast driven them, in their treachery, wherewith they had been treacherous against thee.
“Ubangiji, kai mai adalci ne, amma a yau kunya ta rufe mu, mutanen Yahuda da mutanen Urushalima da na dukan Isra’ila, waɗanda suke kusa da kuma nesa, a dukan ƙasashen da ka warwatsa mu saboda rashin amincinmu a gare ka.
8 O Yahweh, to us, belongeth the shame of faces, to our kings, to our rulers, and to our fathers, —in that we have sinned against thee.
Ya Ubangiji, mu da sarakunanmu, da masu mulkinmu da iyayenmu kunya ta rufe mu saboda mun yi maka zunubi.
9 To the Lord our God, belong compassions, and forgivenesses, —for we have rebelled against him;
Ubangiji Allahnmu mai jinƙai ne, mai gafartawa ne kuma, ko da yake mun yi masa tawaye;
10 and have not hearkened unto the voice of Yahweh our God, —to walk in his instructions which he set before us, through means of his servants the prophets;
ba mu yi biyayya ga Ubangiji Allahnmu ba, ba mu kuma kiyaye shari’unsa da ya ba mu ta wuri bayinsa annabawa ba.
11 yea, all Israel, have transgressed thy law, even going away, so as not to hearken unto thy voice, —therefore, were poured out upon us, the curse and the oath which had been written in the law of Moses the servant of God, because we had sinned against him.
Dukan Isra’ila sun karya dokokinka suka kuma juya maka baya, sun ƙi yi maka biyayya. “Saboda haka la’anoni da rantsuwar hukunce-hukuncen da suke a rubuce a cikin Dokar Musa, bawan Allah, sun kama mu domin mun yi maka zunubi.
12 Thus hath he confirmed his words which he had spoken against us, and against our judges who had judged us, by bringing in upon us a great calamity, —as to which there had not been done, under all the heavens, as hath been done unto Jerusalem.
Ka cika kalmomin da ka yi a kanmu da kuma a kan masu mulkinmu ta wurin kawo mana babban bala’i. A duniya duka ba a taɓa yin wani abu kamar yadda aka yi wa Urushalima ba.
13 Even as written in the law of Moses, hath, all this calamity, come in upon us, —yet entreated we not the face of Yahweh our God, by turning away from our iniquities, and by getting intelligence in thy truth.
Kamar yadda yake a rubuce cikin Dokar Musa, dukan wannan bala’i ya sauko a kanmu, duk da haka ba mu nemi tagomashin Ubangiji Allahnmu ta wurin barin aikatawa zunubanmu, mu kuma mai da hankali a kan gaskiyarka ba.
14 Therefore hath Yahweh, kept watch, for the calamity, and brought it in upon us, —for righteous is Yahweh our God concerning all his deeds which he hath done, seeing that we had not hearkened unto his voice.
Ubangiji bai yi wata-wata wajen kawo mana bala’i ba, domin Ubangiji Allahnmu mai adalci ne a cikin dukan abin da yake yi; duk da haka ba mu yi masa biyayya ba.
15 Now, therefore, O Lord our God, who didst bring forth thy people out of the land of Egypt with a firm hand, and didst make for thyself a name, as at this day, —we have sinned, we have been guilty of lawlessness.
“Yanzu, ya Ubangiji Allahnmu, wanda ya fito da mutanensa daga Masar ta hannu mai ƙarfi wanda kuma ya yi wa kansa sunan da ya dawwama har yă zuwa yau, mun yi zunubi, mun yi abin da ba daidai ba.
16 O Lord! according to all thy righteousness, I beseech thee, let thine anger and thine indignation turn away from thy city Jerusalem, thy holy mountain, —for, by reason of our sins, and by reason of the iniquities of our fathers, Jerusalem and thy people, have become a reproach, to all who are round about us.
Ya Ubangiji, ta wurin kiyaye dukan ayyukanka na adalci, ka huce daga fushinka da hukuncinka da ka yi a kan Urushalima, birninka, tudunka mai tsarki. Zunubinmu da laifofin iyayenmu sun mai da Urushalima da kuma mutanenka abin ba’a ga dukan waɗanda suke kewaye da mu.
17 Now, therefore, hearken, O our God, unto the prayer of thy servant, and unto his supplications, and let thy face shine, upon thy sanctuary, that is desolate, —for the sake of thy servants, O Lord.
“Yanzu, ya Allahnmu, ka ji addu’o’i da koke-koken bayinka. Saboda sunanka, ya Ubangiji, ka duba da rahama wurinka mai tsarki da ya zama kango.
18 Incline, O my God, thine ear, and hearken, open thine eyes, and behold our desolations, and the city on which hath been called thy name; for, not on the ground of our own righteousnesses, are we causing our supplications to fall down before thee, but on the ground of thine abounding compassions.
Ka kasa kunne, ya Allah, ka kuma ji; ka buɗe idanunka ka kuma ga yadda birninka ya zama kango, birnin da yake ɗauke da Sunanka. Ba cewa muna roƙonka saboda mu masu adalci ba ne, amma saboda girman jinƙanka.
19 O Lord, hear! O Lord, forgive! O Lord, hearken and perform! Do not delay! For thine own sake, O my God, because, thine own name, hath been called, upon thy city, and upon thy people.
Ya Ubangiji, ka saurara! Ya Ubangiji ka gafarta! Ya Ubangiji, ka ji ka kuma yi wani abu! Saboda sunanka, ya Allahna, kada ka yi jinkiri, domin da sunanka ake kiran birninka da jama’arka.”
20 And, while yet I was speaking, and praying, and confessing mine own sin, and the sin of my people Israel, —and causing my supplication to fall down before Yahweh my God, concerning the holy mountain of my God;
Yayinda da nake magana da addu’a, ina furta zunubina da zunubin mutanena Isra’ila ina miƙa koke-kokena ga Ubangiji Allahna saboda tudunsa mai tsarki,
21 while yet I was speaking in prayer, then, the man Gabriel, whom I had seen in vision at the beginning, wearied with rapid flight, touched me, about the time of the evening present.
yayinda nake cikin addu’a, sai Jibra’ilu, mutumin nan da na gani a wahayin da ya wuce, ya zo wurina gaggauce wajen lokacin yin hadaya ta yamma.
22 Yea he came, and spake with me, —and said—O Daniel! now, have I come forth, to teach thee understanding.
Ya umarce ni ya kuma ce mini, “Daniyel, yanzu na zo domin in ba ka hikima da ganewa.
23 At the beginning of thy supplications, came forth a word, I, therefore, am arrived to tell, because, a man delighted in, thou art, —mark then the word, and have understanding in the revelation: —
Da zarar ka fara addu’a, an amsa, wadda na zo in faɗa maka, gama ana ƙaunar ka sosai. Saboda haka, ka yi lura da saƙon ka kuma fahimci wahayin.
24 Seventy weeks, have been divided concerning thy people and concerning thy holy city—to put an end to the transgression, and fill up the measure of sin, and put a propitiatory-covering over iniquity, and bring in the righteousness of ages, and affix a seal the vision and prophecy, and anoint the holy of holies.
“An ƙayyade wa jama’arka da tsattsarkan birninka shekara ɗari huɗu da tasa’in domin a kawo ƙarshen laifi da zunubi, domin a yi kafarar laifi, sa’an nan a shigo da adalci madawwami, a rufe wahayi da annabci, a tsarkake haikali.
25 Thou must know, then, and understand: From the going forth of the word to restore and to build Jerusalem—unto the Anointed One, the Prince, [shall be] seven weeks, and sixty-two weeks, —the broadway and the wall, shall again be built, even in the end of the times.
“Sai ka sani ka kuma fahimci wannan; Tun daga sa’ad da aka kafa doka don a maido a kuma sāke gina Urushalima har sai Shafaffen nan, mai mulki, ya zo, za a yi shekara arba’in da tara, da shekara ɗari huɗu da talatin da huɗu. Za a sāke gina ta a yi mata tituna da mafaka.
26 And, after the sixty-two weeks, shall the Anointed One, be cut off, and have, nothing, —and, the city and the sanctuary, will one destroy with the Prince, and so will his own end come with an overwhelming flood, howbeit, up to the full end of the war, are decreed astounding things.
Bayan shekara ɗari huɗu da talatin da huɗu, za a datse Shafaffen nan zai kuma kasance ba shi da kome. Mutanen mai mulkin za su zo su hallaka birnin da kuma wuri mai tsarki. Ƙarshen zai zo kamar rigyawa. Yaƙi zai ci gaba har ƙarshe, a kuma hallakar kamar yadda aka ƙaddara.
27 And he will confirm a covenant to the many, for one week, —but, in the middle of the week, will cause sacrifice and present to cease, and, in his stead, [shall be] the horrid abomination that astoundeth, even till, a full end, and that a decreed one, shall be poured out on him that astoundeth.
Zai tabbatar da alkawari da mutane masu yawa har na shekara bakwai. A tsakiyar bakwai ɗin nan ɗaya zai kawo ƙarshen duk wata hadaya da baiko. Kuma a kusurwar haikali zai sa abin ƙyama mai kawo hallaka, har sai ƙarshen da aka ƙaddara ya auko wa wanda ya sa abin ƙyama.”

< Daniel 9 >