< Daniel 8 >

1 In the third year of the reign of Belshazzar the king, a vision, appeared unto me Daniel, after that which appeared unto me at the beginning.
A shekara ta uku ta mulkin sarki Belshazar, ni, Daniyel, na ga wahayi, bayan wancan da na riga gani.
2 So then I saw, in the vision, and it came to pass, when I saw, that I was in Shusan the fortress, which is in Persia the province, —yea I saw it in a vision, when, I, was by the river Ulai.
A cikin wahayin, na ga kaina a mafakar Shusha a yankin Elam; a wahayin na ga ina a bakin Kogin Ulai.
3 So then I lifted up mine eyes, and looked, and lo! a ram, standing before the river, and, it, had two horns, —and, the two horns, were high, but, the one, was higher than the other, and, the higher, had come up, last.
Na ɗaga ido, a gabana kuwa sai ga rago mai ƙahoni biyu, yana tsaye a gefen mashigin kogin, ƙahonin kuma suna da tsawo. Ɗaya daga cikin ƙahonin ya fi ɗayan tsawo. Wanda ya fi tsawon shi ne ya tsiro daga baya.
4 I saw the ram, pushing strongly westward and northward and southward, so that no wild beast could stand before him, and none could deliver out of his hand, —but he did according to his own pleasure, and shewed himself great.
Na lura da ragon sa’ad da ya kai karo wajen yamma da arewa da kudu. Babu wata dabbar da ta iya ƙarawa da shi, babu kuma wanda ya iya kuɓuta daga ikonsa. Ya yi yadda ya ga dama, ya kuma zama mai girma.
5 Now, I, was observing, when lo! a he-goat, coming in out of the west, over the face of all the earth, but it meddled not with the earth, —and, the goat, had a conspicuous horn between his eyes.
Yayinda nake tunani game da wannan, farat ɗaya sai ga bunsurun da yake da sanannen ƙaho tsakanin idanunsa ya ɓullo daga wajen yamma, yana ratsa dukan duniya ba ya ko taɓa ƙasa.
6 So then he came up to the ram having the two horns, which I had seen, standing before the river, —and ran unto him, in the fury of his strength.
Ya zo wajen rago mai ƙahoni biyu ɗin nan da na riga na gani tsaye a gefen mashigin kogin nan ya tasar masa da fushi mai zafi.
7 Yea I saw him coming close upon the ram, and he was enraged at him, and smote the ram, and brake in pieces both his horns, and there was no strength in the ram to stand before him, —but he cast him down to the ground, and trampled him underfoot, and there was none could deliver the ram out of his power.
Na ga ya zo kusa da ragon, ya husata da shi ƙwarai, ya kai wa ragon hari. Ya kakkarya ƙahoninsa nan biyu. Ƙarfin ragon ya kāsa, bai iya kāre kansa daga bunsurun ba. Bunsurun ya buge shi ƙasa ya tattake shi. Ba wanda ya iya ceton ragon daga bunsurun.
8 But, the he-goat, shewed himself very great, —and, when he had become mighty, the great horn, was broken in pieces, and there came up afterwards four, in its stead, towards the four winds of the heavens;
Bunsurun kuwa ya ƙasaita, amma a ƙwanƙolin ikonsa sai aka karye babban ƙahonsa, kuma a wurin da ƙahon nan ya kasance waɗansu sanannun ƙahoni huɗu suka tsiro suna fuskantar kusurwoyin nan huɗu.
9 and, out of the first of them, came forth a little horn, —which became exceedingly great, against the south and against the east, and against the beautiful [land];
Daga cikin ɗayansu kuma wani ƙaramin ƙaho ya fito, ya yi girma ya ƙasaita ƙwarai zuwa kudu da kuma gabas da wajen Kyakkyawar Ƙasa.
10 yea it became great as far as the host of the heavens, —and caused to fall, to the earth, some of the host and some of the stars, and trampled them underfoot;
Ya yi girma sai da ya kai rundunar sammai, ya kuma fid da waɗansu rundunar taurari zuwa ƙasa ya kuma tattake su.
11 even as far as the ruler of the host, shewed he his greatness, —and, because of him, was taken away the continual [ascending-sacrifice], and the place of the sanctuary, was cast down;
Sai ya ɗora kansa ya zama mai girma kamar Sarkin runduna; sai aka ɗauke hadaya ta kullayaumi daga gare shi, aka kuma saukar da wurin masujadarsa ƙasa.
12 and, a host, was set over the continual [ascending-sacrifice], by transgression, —and faithfulness, was cast down, to the ground, and so he acted with effect, and succeeded.
Saboda tawaye, sai aka ba da rundunar tsarkaka da kuma hadayar ƙonawa ta kowace rana ga ƙahon. Sai ya yi watsi da gaskiya, ya yi abin da ya ga dama, ya kuwa yi nasara.
13 Then heard I a certain holy one, speaking, —and another holy one said to that certain holy one who was speaking—How long is the vision of the continual [ascending-sacrifice] as taken away, and the transgression which astoundeth, for both sanctuary and host to be given over to be trampled underfoot?
Sa’an nan na ji mai tsarkin nan yana magana, wani mai tsarki kuma ya ce da wancan, “Har yaushe wannan wahayi zai tabbata, wahayi game da hadaya ta kullayaumi, da tawayen da yake kawo lalacewa, da kuma miƙa wuri mai tsarki da kuma na rundunar da za a tattake a ƙarƙashin sawu?”
14 And he said unto him, Until two thousand and three hundred evening-mornings, —then shall the sanctuary, be vindicated.
Sai ya ce mini, “Zai ɗauki safiya da yamma 2,300; sa’an nan za a sāke tsarkake wuri mai tsarki.”
15 And it came to pass, when, I Daniel, had seen the vision, —and had sought discernment, that lo! there was standing before me, as the appearance of a man.
Yayinda ni, Daniyel, nake duban wahayi ina ƙoƙari in fahimce shi, sai ga wani a gabana wanda ya yi kama da mutum.
16 Then heard I a human voice, between [the banks of] the Ulai, —which cried out, and said, Gabriel! cause this man to understand the revelation.
Sai na ji muryar wani mutum daga Ulai tana cewa, “Jibra’ilu, faɗa wa wannan mutum ma’anar wahayin.”
17 So he came near where I stood, and, when he came, I was terrified, and fell upon my face, —but he said unto me, Understand, O son of man, that, to the time of the end, belongeth the vision.
Da ya zo kusa da inda nake tsaye, na firgita na kuma fāɗi rubda ciki. Ya ce da ni “Ɗan mutum, ka gane da cewa wannan wahayi yana magana ne a kan kwanakin ƙarshe.”
18 And, when he spake with me, I fell stunned upon my face, to the earth, —but he touched me, and caused me to stand up where I was.
Yayinda yake magana da ni, barci mai nauyi ya kwashe ni, da nake kwance rubda ciki. Sai ya taɓa ni ya kuma tashe ni tsaye.
19 Then said he, Behold me! causing thee to know, that which shall come to pass in the afterpart of the indignation, —for, at an appointed time, shall be an end.
Sai ya ce, “Zan faɗa maka abin da zai faru a lokacin fushi, saboda wahayin yana magana ne a kan lokacin da aka ƙayyade na ƙarshe.
20 The ram which thou sawest, having the two horns, representeth the kings of Media and Persia;
Rago mai ƙahoni biyu da ka gani, yana a madadin sarakunan Medes da Farisa ne.
21 and, the he-goat, is the king of Greece, —and, the great horn which was between his eyes, the same, is the first king.
Bunsurun kuwa sarkin Girka ne, kuma babban ƙahon da yake tsakanin idanunsa, sarki na farko ne.
22 Now, as for its being broken in pieces, whereupon there stood up four in its stead, four kingdoms, out of his nation, shall stand up, but not with his strength;
Ƙahoni huɗu da suka maya wannan da ya karye yana a madadin masarautu huɗu da za su tashi daga cikin al’ummarsa amma ba za su sami irin ikonsa ba.
23 but, in the aftertime of their kingdom, when transgressions, have filled up their measure, —there will stand up a king of mighty presence, and skilful in dissimulation;
“Can wajen ƙarshe mulkinsu, sa’ad da muguntarsu ta kai intaha, wani mugun sarki mai rashin hankali, uban makirci, zai fito.
24 and his strength, will be mighty, but not through his own strength, and, wonderfully, will he destroy, and succeed and act with effect, —and will destroy mighty ones, and the people of holy ones;
Zai yi ƙarfi ƙwarai da gaske, amma ba da ikonsa ba. Zai jawo mummunar hallakarwa kuma zai yi nasara a duk abin da ya sa gaba. Zai hallakar da majiya ƙarfi da kuma tsarkaka.
25 and, by his cunning, will he both cause deceit to succeed in his hand, and, in his own heart, will he shew himself to be great, and, by their careless security, will he destroy many, —and, against the ruler of rulers, will he stand up, but, without hand, shall be broken in pieces.
Zai sa yaudara ta ƙara yin yawa, zai ɗaukaka kansa. Sa’ad da suke ji sun sami mafaka, zai hallaka mutane da yawa sa’an nan kuma yă fara gāba da Sarkin sarakuna. Duk da haka za a hallaka shi, amma ba da ikon mutum ba.
26 Now, the revelation of the evening and the morning which hath been told, faithful, indeed it is, —but, thou, close up the vision, because it is for many days.
“Wahayin nan na safiya da yamma da aka nuna maka gaskiya ne, amma ka ɓoye wahayin, gama ya shafi nan gaba mai tsawo ne.”
27 Now, as for me Daniel, then was I sick for days, but I arose and did the business of the king, —and, though I was confounded concerning the revelation, yet could no one discern it.
Ni, Daniyel, na gaji matuƙa na kuma yi rashin lafiya na kwanaki masu yawa. Sa’an nan sai na tashi na ci gaba da hidimar sarki. Wahayin ya shige mini duhu, ya fi ƙarfin fahimtata.

< Daniel 8 >