< Daniel 12 >

1 And, at that time, will Michael, the great ruler who standeth for the sons of thy people, make a stand, and there will be a time of trouble, such as never was since there was a nation, up to that time, —and, at that time, shall thy people, be delivered, every one found written in the book;
“A wannan lokaci Mika’ilu, babban mai mulki wanda yake kāre mutanenka, zai tashi. Za a yi lokacin matsananciyar wahala wanda ba a taɓa yi tun farkon ƙasashe har zuwa yanzu. Amma a lokacin da mutanenka, kowane mutum wanda aka sami sunansa a rubuce a cikin littafin, za a cece shi.
2 and, many of the sleepers in the dusty ground, shall awake, —these, [shall be] to age-abiding life, but, those, to reproach, and age-abiding abhorrence;
Ɗumbun mutanen da suka yi barci cikin turɓayar duniya za su farka, waɗansu zuwa ga rai madawwami, waɗansu zuwa ga madawwamiyar kunya da kuma madawwamin ƙasƙanci.
3 and, they who make wise, shall shine like the shining of the expanse, —and, they who bring the many to righteousness, like the stars to times age-abiding and beyond.
Waɗanda suke da hikima za su haskaka kamar hasken samaniya, waɗanda kuma suka jagoranci waɗansu da yawa zuwa adalci, za su zama kamar taurari har abada abadin.
4 But, thou, Daniel, close up the words, and seal the book, until the time of the end, —many will run to and fro, and knowledge, shall abound.
Amma kai, Daniyel, ka rufe zancen nan ka kuma liƙe kalmomin littafin nan har sai ƙarshe. Mutane da yawa za su yi ta kai komo don neman sani.”
5 Then, I, Daniel, looked, and lo! two others, standing, —one on this side of the bank of the river, and one on that side of the bank of the river.
Sa’an nan ni, Daniyel, na duba, a gabana kuwa ga waɗansu mutum biyu tsaye, ɗaya a wannan hayen kogi ɗaya kuma a ƙetaren kogin.
6 And one said to the man clothed with linen, who was upon the waters of the river, How long shall be the end of the wonders?
Ɗayansu ya ce wa mutumin da yake sanye da tufafin lilin, wanda yake a saman ruwan kogin, “Har yaushe waɗannan abubuwan banmamakin za su cika?”
7 And I heard the man clothed with linen who was upon the waters of the river, when he held up his right hand and his left unto the heavens, and sware by him that liveth unto times age-abiding, —For a set time and times and a half, and, when the dispersion of a part of the holy people, is brought to an end, then shall come to an end all these things.
Mutumin da yake sanye da tufafin lilin, wanda yake a saman ruwan kogin, ya ɗaga hannun damansa da kuma na hagunsa sama, sai na ji yana rantsuwa da wannan da yake raye har abada, yana cewa, “Zai kasance na ɗan lokaci, lokuta da rabin lokaci. Za a kammala waɗannan abubuwa, sa’ad da aka gama ragargaje ikon tsarkakan mutane.”
8 And, I, heard, but could not understand, —so I said, O my lord! what shall be the issue of these things?
Na kuma ji, amma ban fahimta ba. Don haka sai na yi tambaya, “Ranka yă daɗe, mene ne ƙarshen waɗannan abubuwa?”
9 Then said he, Go thy way, Daniel; for closed up and sealed are the words, until the time of the end.
Sai ya amsa ya ce, “Ka kama hanyarka, Daniyel, domin a rufe kalmomin aka kuma liƙe su har sai ƙarshen lokaci.
10 Many, will purify themselves and be made white and be refined, but the lawless, will act lawlessly, and none of the lawless, shall understand, —but, they who make wise, shall understand;
Za a tsarkake mutane da yawa, za a maishe su marasa aibi a kuma tace su; amma mugaye za su ci gaba da mugunta. Babu wani mugun da zai fahimta, amma waɗanda za su zama masu hikima za su fahimta.
11 and, from the time of the taking away of the continual [ascending-sacrifice], and the placing of the horrid abomination that astoundeth, [shall be] one thousand two hundred and ninety days.
“Daga lokacin da za a hana miƙa hadayar ƙonawa ta yau da kullum, a kuma kafa abin banƙyama, wanda yake lalatarwa, za a yi kwana 1,290.
12 Happy! is he that waiteth, and attaineth to one thousand three hundred and thirty-five days.
Mai albarka ne wanda ya jira har yă zuwa ƙarshen kwanakin nan 1,335.
13 But, thou, go thy way to the end, —and thou shalt rest, and shalt rise to thy lot at the end of the days.
“Gare ka dai, ka yi tafiyarka har zuwa ƙarshe. Za ka huta, sa’an nan a ƙarshen kwanaki za ka tashi don karɓi sashen gadon da aka ba ka.”

< Daniel 12 >