< 2 Samuel 7 >

1 And it came to pass, when the king had taken up his abode in his house, —and Yahweh had given him rest round about, from all his enemies,
Bayan sarki ya kama zama a fadansa Ubangiji kuma ya hutashe shi daga dukan abokan gābansa da suke kewaye da shi,
2 that the king said unto Nathan the prophet, See, I pray thee—I, have my abode in a house, of cedar, but, the ark of God, abideth in, the midst, of curtains.
sai ya ce wa annabi Natan, “Ga ni, ina zama a fadar katakon al’ul, amma akwatin alkawarin Allah yana zaune a tenti.”
3 And Nathan said unto the king, All that is in thy heart, go—do, —for Yahweh is with thee.
Natan ya amsa wa sarki ya ce, “Duk abin da yake a zuciyarka, sai ka yi, gama Ubangiji yana tare da kai.”
4 But so it was, in that night, that the word of Yahweh came unto Nathan, saying:
A daren nan maganar Ubangiji ta zo wa Natan cewa,
5 Go and say unto my servant—unto David: Thus, saith Yahweh, —Shalt, thou, build me a house, for me to dwell in;
“Je ka faɗa wa bawana Dawuda, ‘Ga abin da Ubangiji ya ce, kai ne za ka gina mini gida in zauna?
6 seeing that I have not dwelt in a house, since the day that I brought up the sons of Israel out of Egypt, even unto this day, —but have been wandering in a tent as my habitation?
Ban taɓa zama a gida ba tun daga ranar da na fito da Isra’ilawa daga Masar har yă zuwa yau. Ina dai kai da kawowa a tenti, a matsayin mazaunina.
7 Wheresoever I have wandered with any of the sons of Israel, spake I ever, a word, with any one of the tribes of Israel, whom I charged to shepherd my people Israel, saying, —Wherefore have ye not built me a house, of cedar?
A cikin kaiwa da kawowar da nake yi cikin dukan Isra’ilawa, na taɓa ce wa wani shugabanninsu wanda na umarta su lura da mutanena Isra’ila, “Don me ba ku gina mini mazauni da katakon al’ul ba?”’
8 Now, therefore, thus, shalt thou say unto my servant, unto David: Thus, saith Yahweh of hosts, I myself, took thee away from the pasture, from after the flock, —to become leader over my people, over Israel;
“Yanzu, ka gaya wa bawana Dawuda ‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, na ɗauko ka daga makiyaya, daga kuma garken tumaki ka zama sarki bisan mutane Isra’ila.
9 and was with thee, whithersoever thou didst go, and have cut off all thine enemies, from before thee, —and will make thee a name, like the name of the great ones who are in the earth;
Na kasance tare da kai duk inda ka tafi, na kuma kawar da dukan abokan gābanka a gabanka. Yanzu zan sa sunanka yă shahara kamar sunayen shahararrun mutanen duniya.
10 and will appoint a place for my people, for Israel, and will plant them, and they shall inhabit their place, and be unsettled no more, —neither shall the sons of perversity again humiliate them, as at first;
Zan kuma tanada wa mutanena Isra’ila wuri, in kuma dasa su yadda za su kasance da gida kansu ba tare da an ƙara damunsu ba. Mugayen mutane ba za su ƙara wahalshe su kamar dā ba,
11 even from the day when I put judges in charge over my people Israel, thus will I give thee rest from all thine enemies. And Yahweh must tell thee that, a house, will Yahweh make for thee.
yadda suka yi tun lokacin da na naɗa shugabanni bisan mutanena Isra’ila, zan kuma hutashe ka daga hannun abokan gābanka. “‘Ubangiji ya furta maka cewa Ubangiji kansa zai kafa maka gida.
12 And it shall be that, when thy days shall be fulfilled, and thou shalt sleep with thy fathers, then will I raise up thy seed after thee, which proceedeth from thine own body, —and I will establish his kingdom.
Sa’ad da kwanakinka suka ƙare, za ka huta tare da kakanninka, zan tā da zuriyarka, na cikinka, zan kuma sa mulkinsa ya kahu.
13 He, shall build a house for my name, —and I will establish his kingly throne unto times age-abiding:
Shi zai gina gida domin Sunana, zan kuwa kafa gadon sarautarsa har abada.
14 I, will become his father, And, he, shall become my son: If he commit iniquity, then will I correct him, with the rod of men, and with the stripes of the sons of men;
Zan zama Ubansa, shi kuma yă zama ɗana. Idan ya yi laifi, zan yi amfani da mutane in hukunta shi. Mutane ne za su zama bulalata.
15 But, my lovingkindness, shall not depart from him, —as I caused it to depart from Saul, whom I caused to depart from before thee.
Amma ba za a taɓa ɗauke ƙaunata daga gare shi yadda na ɗauke ta daga wurin Shawulu ba, shi wannan wanda na kawar daga gabanka.
16 So shall thy house and thy kingdom be made steadfast unto times age-abiding, before thee, —thy throne, shall be established unto times age-abiding.
Gidanka da kuma masarautarka za su dawwama har abada a gabana; gadon sarautarka kuma zai kahu har abada.’”
17 According to all these words, and according to all this vision, so, spake Nathan unto David.
Natan ya gaya wa Dawuda dukan abin da Allah ya bayyana masa.
18 Then entered King David, and tarried before Yahweh, —and said—Who am, I, My Lord, Yahweh, and what is my house, that thou hast brought me, hitherto;
Sa’an nan Sarki Dawuda ya je ya zauna a gaban Ubangiji ya ce, “Wane ne ni, ya Ubangiji Mai Iko Duka, ko gidana, har da ka ɗaga mu zuwa wannan matsayi?
19 and hast yet further made this seem little in thine eyes, My Lord, Yahweh, in that thou hast spoken, even of the house, of thy servant, for a great while to come? This, then is the law of manhood, O My Lord, Yahweh!
Har ya zama kamar wannan bai isa ba a gabanka, ya Ubangiji Mai Iko Duka, ka kuma yi magana game da nan gaba na gidan bawanka. Haka ka saba yi da mutane, ya Ubangiji Mai Iko Duka?
20 What more, then, can David yet further speak unto thee, —seeing that, thou thyself knowest thy servant, O My Lord Yahweh?
“Me kuma Dawuda zai ce maka? Gama ka san bawanka, ya Ubangiji Mai Iko Duka.
21 For the sake of thine own word, and according to thine own heart, hast thou done all this great thing, —making it known unto thy servant.
Gama saboda maganarka da kuma bisa ga nufinka, ka aikata wannan babban abu, ka kuma sanar da bawanka.
22 For this cause, hast thou magnified thyself, O Yahweh Elohim, —for there is none like unto, thee, yea there is no God besides thee, according to all that we have heard with our ears.
“Kai mai girma ne, ya Ubangiji Mai Iko Duka! Babu wani kamar ka, babu kuma wani Allah sai kai; kamar yadda muka ji da kunnuwanmu.
23 Who, then, is like thy people, like Israel, a nation alone in the earth? whom God went to redeem for himself as a people, so to make himself a name, and to do for you the great deed, fearful things also for thy land, to make way for thy people, whom thou hadst redeemed for thyself, out of Egypt, [dealing with] nations and their god’s;
Wane ne kuma yake kamar da mutanenka Isra’ila, al’umma guda a duniya wadda Allah ya fita don yă kuɓutar wa kansa, ya kuma yi suna wa kansa, ya kuma aikata manyan abubuwa da kuma al’amuran banmamaki ta wurin korin al’ummai da allolinsu daga gaban mutanenka, waɗanda ka kuɓutar daga Masar?
24 and hast established for thyself thy people Israel—for thyself as a people, unto times age-abiding, —thou thyself, also, O Yahweh, becoming their God.
Ka kafa mutanenka Isra’ila kamar naka na kanka har abada, kai kuma, ya Ubangiji, ka zama Allahnsu.
25 Now, therefore, O Yahweh Elohim, the word which thou hast spoken concerning thy servant, and concerning his house, confirm thou, unto times age-abiding, —and do, as thou hast spoken:
“Yanzu kuwa, ya Ubangiji Allah, ka cika alkawarin da ka yi game da bawanka da gidansa. Ka yi kamar yadda ka alkawarta,
26 that thy name may be age-abidingly magnified, saying, Yahweh of hosts, is God over Israel, and so, the house of thy servant David, be established before thee.
domin sunanka yă kasance da girma har abada. Sa’an nan mutane za su ce, ‘Ubangiji Maɗaukaki, Allah ne a bisa Isra’ila!’ Kuma gidan bawanka Dawuda zai kahu a gabanka.
27 For, thou, O Yahweh of hosts, God of Israel, hast unveiled the ear of thy servant, saying—A house, will I build for thee. For this cause, hath thy servant found in his heart, to pray unto thee, this prayer.
“Ya Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, ka bayyana wa bawanka cewa, ‘Zan gina maka gida.’ Saboda haka bawanka ya sami ƙarfin hali yă miƙa maka wannan addu’a.
28 Now, therefore, O My Lord, Yahweh, thou, art God, and, thy words, shall prove true, —therefore hast thou spoken unto thy servant this goodness.
Ya Ubangiji Mai Iko Duka, kai Allah ne! Maganarka da aminci take, ka kuma yi wa bawanka waɗannan abubuwa masu kyau.
29 Now, therefore, be pleased to bless the house of thy servant, that it may continue age-abidingly before thee, —for, thou, O My Lord, Yahweh, hast spoken, therefore, with thine own blessing, shall the house of thy servant be age-abidingly blessed.
In ya gamshe ka, bari ka albarkaci gidan bawanka don yă dawwama a gabanka har abada; gama kai, ya Ubangiji Mai Iko Duka, ka riga ka yi magana, kuma saboda kai ka sa albarka ga gidan bawanka, lalle zai kasance da albarka har abada.”

< 2 Samuel 7 >