< 2 Samuel 11 >

1 And it came to pass, at the return of the year, at the time of the going forth of kings, that David sent Joab, and his servants with him, and all Israel, and they destroyed the sons of Ammon, and laid siege to Rabbah, —but, David, was remaining in Jerusalem.
Da bazara, a lokacin da sarakuna sukan fita zuwa yaƙi, sai Dawuda ya aiki Yowab tare da mutanen sarki, da dukan Isra’ila. Suka je suka hallaka Ammonawa, suka kuma yi wa Rabba kwanton ɓauna. Amma Dawuda ya yi zamansa a Urushalima.
2 And it came to pass that, at eventide, David arose from his couch, and walked to and fro on the roof of the king’s house, when, from the roof, he saw a woman bathing herself, —the woman being exceeding beautiful to look upon.
Wata rana da yamma, Dawuda ya tashi daga gadonsa, ya zaga kewaye a rufin fadansa. Daga rufin ya ga wata mace tana wanka. Matar kyakkyawa ce ƙwarai.
3 And David sent and enquired after the woman, —and one said—Is not, this, Bath-sheba, daughter of Eliam, wife of Uriah the Hittite?
Sai Dawuda ya aiki wani yă bincika ko wace ce ita, sai mutumin ya dawo ya ce, “Wannan ba Batsheba ba ce,’yar Eliyam matar Uriya, mutumin Hitti?”
4 And David sent messengers, and fetched her, and she came in unto him, and he lay with her, she having purified herself from her uncleanness, —and she returned unto her own house.
Sa’an nan Dawuda ya aiki manzanni su kawo masa ita. Ta zo wurinsa shi kuma ya kwana da ita (A lokacin kuwa ta gama tsarkake kanta ke nan daga jinin haila.) Sa’an nan ta tafi gida.
5 And the woman, having conceived, sent and told David, and said, I am with child.
Matar ta yi ciki, ta kuwa aika wa Dawuda, tana cewa, “Ina da ciki.”
6 Then sent David unto Joab, Send unto me Uriah the Hittite. So Joab sent Uriah unto David.
Saboda haka Dawuda ya aika saƙo wa Yowab ya ce, “Ka aiko mini da Uriya mutumin Hitti.” Yowab kuwa ya aika da shi wajen Dawuda.
7 And, when Uriah had come in unto him, David asked—how Joab prospered, and how the people prospered, and how the war prospered.
Da Uriya ya zo wurinsa, sai Dawuda ya tambaye shi lafiyar Yowab da sojojin, da kuma yaya yaƙin yake tafiya.
8 Then said David unto Uriah, Go down unto thy house, and bathe thy feet. And, when Uriah went out of the house of the king, there followed him, a present from the king.
Sa’an nan Dawuda ya ce wa Uriya, “Gangara gidanka ka wanke ƙafafunka.” Saboda haka Uriya ya bar fadar, sarki kuma ya aika masa da kyauta.
9 But Uriah slept at the entrance of the king’s house, with all the servants of his lord, —and went not down unto his own house.
Amma Uriya ya kwanta a ƙofar fada tare da dukan bayin maigidansa, bai kuwa tafi gidansa ba.
10 And it was told David, saying, Uriah went not down, unto his own house. So David said unto Uriah—Was it not, from a journey, thou didst come? why, then, hast thou not been down unto thine own house?
Da aka gaya wa Dawuda, “Uriya bai tafi gida ba,” sai Dawuda ya tambaye shi ya ce, “Ba ka zo daga wuri mai nisa ba? Me ya sa ba ka je gida ba?”
11 And Uriah said unto David—The ark, and Israel and Judah, are dwelling in huts and, my lord Joab, and the servants of my lord, on the face of the field, are encamped, Was, I, then, to enter my own house, to eat and to drink and to lie with my wife? By thy life, yea by the life of thy soul, I could not do this thing.
Sai Uriya ya ce wa Dawuda, “Akwatin Alkawari, da Isra’ila, da Yahuda suna zama cikin tentuna, kuma maigidana Yowab da mutanen ranka yă daɗe suna a sansani a fili. Yaya zan je gidana in ci in sha in kuma kwana da matata? Muddin kana a raye, ba zan yi irin wannan abu ba!”
12 Then said David unto Uriah—Abide here to-day also, and, to-morrow, will I let thee go. So Uriah abode in Jerusalem that day, and the morrow.
Sai Dawuda ya ce masa, “Ka ƙara dakata a nan kwana ɗaya, gobe kuwa in sallame ka.” Saboda haka Uriya ya dakata a Urushalima a ranar, da kuma ta biye.
13 And David called him, and he did eat before him, and drank, and he made him drunk, —and he went forth in the evening to lie down on his bed, with the servants of his lord, but, unto his own house, went he not down.
Dawuda ya gayyace shi, ya kuwa ci ya sha tare da shi, Dawuda ya sa ya bugu tilis. Amma da yamma Uriya ya koma ya kwanta a tabarmarsa cikin bayin maigidan sarki; bai je gida ba.
14 And so it was, in the morning, that David wrote a letter unto Joab, —and sent it by the hand of Uriah;
Da safe Dawuda ya rubuta wa Yowab wasiƙa ya ba wa Uriya.
15 and he wrote in the letter, saying, —Set ye Uriah in the forefront of the hottest battle, and retire ye from him, that he be smitten and die.
A ciki wasiƙar ya rubuta, “Tura Uriya a gaba inda yaƙi ya fi zafi. Sa’an nan ka janye daga gare shi don a buge shi yă mutu.”
16 So it came to pass, when Joab was laying siege to the city, that he put Uriah in the place where he knew that the men of valour, were.
Saboda haka yayinda Yowab ya kai yaƙi kusa da birnin, sai tura Uriya a inda ya sani akwai jarumawan Ammon na gaske.
17 And forth sallied the men of the city, and fought with Joab, and there fell some of the people, of the servants of David, —then died also, Uriah the Hittite.
Sa’ad da mutanen garin suka fito suka yaƙi Yowab, sai waɗansu mutane daga sojojin Dawuda suka mutu; Uriya mutumin Hitti ma ya mutu.
18 So Joab sent and told David all the news of the battle;
Yowab ya aika wa Dawuda cikakken labari batun yaƙin.
19 and he charged the messenger saying, —When thou hast ended all the news of the battle, in speaking unto the king,
Ya umarci manzon ya ce, “Da ka gama yin wa sarki wannan batun yaƙin,
20 then shall it be, if the king’s anger arise, and he say unto thee, Why came ye near unto the city, to fight? Knew ye not, that they would shoot from off the wall?
wataƙila sarki yă husata, yă tambaye ka, ‘Me ya sa kuka je kusa da birnin don ku yi yaƙi? Ba ku san cewa za su yi harbi daga katanga ba?
21 Who smote Abimelech son of Jerubbaal? Did not, a woman, cast on him an upper millstone from off the wall, that he died, in Thebez? Wherefore came ye near unto the wall? Then shalt thou say—Moreover, thy servant, Uriah the Hittite, died.
Wane ne ya kashe Abimelek ɗan Yerub-Beshet? Ba mace ce ta jefa dutsen niƙa a kansa daga katanga, ta haka ya mutu a Tebez ba? Me ya sa kuka je kurkusa da katangar?’ In ya tambaye ka wannan, sai ka ce masa, ‘Har bawanka Uriya mutumin Hitti ma ya mutu.’”
22 And the messenger went his way, —and came in, and told David, all that Joab had sent him [to tell].
Manzon ya tashi ya tafi, da ya iso kuwa sai ya gaya wa Dawuda dukan abin da Yowab ya aike shi yă faɗa.
23 And the messenger said unto David, The men were too strong for us, and sallied forth against us, in the field, —so we were drawn against them as far as the opening of the gate.
Manzon ya ce wa Dawuda, “Mutanen sun sha kanmu suka fito suka yaƙe mu a fili, amma muka kore su har ƙofar birni.
24 Then did the archers shoot upon thy servants, from off the wall, and there died some of the servants of the king, —moreover also, thy servant, Uriah the Hittite, died.
Sa’an nan maharba suka yi ta harbi daga katanga har waɗansu mutanen sarki suka mutu. Ban da haka ma, Uriya mutumin Hitti bawan sarki ya mutu.”
25 Then said David unto the messenger—Thus, shalt thou say unto Joab, —Let not this thing be grievous in thine eyes, for, now this one, and then that one, doth the sword devour, —make hot thy battle against the city, and overthrow it; Thus embolden thou him.
Dawuda ya ce wa manzon, “Ka gaya wa Yowab, ‘Kada ka bar wannan yă dame ka; yadda takobi ya lamushe wannan, haka zai lamushe wancan ma. Ku ƙara matsa wa garin lamba, ku hallaka shi.’ Ka faɗa haka don ka ƙarfafa Yowab.”
26 And, when Uriah’s wife heard that Uriah her husband was dead, she made loud lamentation over her lord.
Da matar Uriya ta ji cewa mijinta ya mutu, sai ta yi makoki saboda shi.
27 And, when the time of mourning had passed, David sent and received her into his house, and she became his wife, and bare him a son. But the thing which David had done was wicked in the eyes of Yahweh.
Bayan kwanakin makoki suka ƙare, Dawuda ya sa aka kawo ta gidansa, ta kuwa zama matarsa, ta kuma haifa masa ɗa. Sai dai abin da Dawuda ya yi bai gamshi Ubangiji ba.

< 2 Samuel 11 >