< 2 Chronicles 30 >
1 Then sent Hezekiah unto all Israel and Judah, moreover also, letters, wrote he unto Ephraim and Manasseh, that they should come unto the house of Yahweh, in Jerusalem, —to keep a passover unto Yahweh, God of Israel.
Sai Hezekiya ya aika wa dukan Isra’ila da Yahuda, ya kuma rubuta wasiƙu zuwa Efraim da Manasse, yana gayyatarsu su zo haikalin Ubangiji a Urushalima, su kuma yi Bikin Ƙetarewa ga Ubangiji, Allah na Isra’ila.
2 Yea, the king and his rulers and all the convocation in Jerusalem, had taken counsel, —to keep the passover in the second month.
Sarki da fadawansa da dukan taro a Urushalima suka yanke shawara su yi Bikin Ƙetarewa a wata na biyu.
3 For they were unable to keep it at that time, —because, the priests, had not hallowed themselves in sufficient numbers, and, the people, had not gathered themselves unto Jerusalem.
Ba su iya yinsa a daidai lokacinsa ba domin babu isashen firistocin da suka tsarkake kansu, mutane kuma ba su taru a Urushalima ba.
4 And the thing was right, in the eyes of the king, —and in the eyes of all the convocation.
Shirin ya yi kyau ga sarki da kuma dukan taron.
5 So they established a decree, to make proclamation throughout all Israel, from Beer-sheba even unto Dan, that they should come in to keep a passover unto Yahweh the God of Israel, in Jerusalem, —for, not for a long time, had they kept it as written.
Suka yanke shawara su yi shelar a ko’ina a Isra’ila, daga Beyersheba zuwa Dan, suna kiran mutane su zo Urushalima, suka kuma yi Bikin Ƙetarewa ga Ubangiji Allah na Isra’ila. Ba a yi bikin da mutane masu yawa bisa ga abin da aka rubuta ba.
6 The runners, therefore, went with letters from the hand of the king and his rulers, throughout all Israel and Judah, and according to the commandment of the king, saying, —Ye sons of Israel, return ye unto Yahweh, God of Abraham, Isaac and Israel, and he will return unto the remnant, that which is left to you, out of the hand of the kings of Assyria.
Bisa ga umarnin sarki, sai’yan aika suka tafi ko’ina a Isra’ila da Yahuda da wasiƙu daga sarki da kuma daga fadawansa, wasiƙar tana cewa, “Mutanen Isra’ila, ku dawo ga Ubangiji Allah na Ibrahim, Ishaku da Isra’ila, domin yă dawo gare ku, ku da kuka tafi, ku da kuka kuɓuce daga hannun sarakuna Assuriya.
7 And be not ye like your fathers, or like your brethren, who acted unfaithfully with Yahweh, God of your fathers, —who therefore delivered them up for an astonishment, as, ye yourselves, can see.
Kada ku zama kamar iyayenku da’yan’uwanku, waɗanda suka yi rashin aminci ga Ubangiji Allah na kakanninsu, har ya mai da su abin tsoro, yadda kuke gani.
8 Now, do not stiffen your neck, like your fathers, —stretch forth the hand unto Yahweh, and enter into his sanctuary which he hath hallowed unto times age-abiding, and serve Yahweh your God, that he may turn from you the glow of his anger.
Kada ku yi taurinkai, yadda iyayenku suka yi; ku miƙa kai ga Ubangiji. Ku zo wuri mai tsarki, wanda ya tsarkake har abada. Ku bauta wa Ubangiji Allahnku, domin fushi mai zafi yă juye daga gare ku.
9 For, by your returning unto Yahweh, your brethren and your children, shall find compassion before their captors, so as to return unto this land. For, gracious and compassionate, is Yahweh your God, and will not turn away his face from you, if ye will return unto him.
In kuka dawo wurin Ubangiji, sa’an nan waɗanda suka kama’yan’uwanku da’ya’yanku za su nuna musu tausayi, su kuma dawo wannan ƙasa, gama Ubangiji Allahnku mai alheri ne mai jinƙai kuma. Ba zai kau da fuskarsa daga gare ku ba, in kuka dawo gare shi.”
10 So the runners were passing from city to city throughout the land of Ephraim and Manasseh, even unto Zebulun, —but they were laughing them to scorn, and mocking them.
’Yan aika suka tafi gari-gari a cikin Efraim da Manasse, har zuwa Zebulun, amma mutane suka yi musu dariyar reni, suka kuma yi musu ba’a.
11 Howbeit, some, out of Asher and Manasseh and out of Zebulun, humbled themselves, and came to Jerusalem.
Duk da haka, waɗansu mutanen Asher, Manasse da Zebulun suka ƙasƙantar da kansu suka tafi Urushalima.
12 Also, upon Judah, came the hand of God, to give them one heart, —to keep the commandment of the king and the rulers, as the word of Yahweh.
Haka ma a Yahuda, hannun Allah yana a kan mutane don yă ba su zuciya ɗaya su yi abin da sarki da fadawansa suka umarta, suna bin maganar Ubangiji.
13 And there gathered themselves unto Jerusalem much people, to keep the festival of unleavened cakes, in the second month, —an exceeding large convocation.
Taron mutane mai girma ya haɗu a Urushalima don Bikin Burodi Marar Yisti a wata na biyu.
14 Then rose they up, and removed the altars, which were in Jerusalem, -and, all the censers, removed they, and cast them into the Kidron ravine.
Suka kawar da bagadai a Urushalima suka fid da bagadan turare suka zubar da su a Kwarin Kidron.
15 Then slaughtered they the passover, on the fourteenth of the second month, —and, the priests and the Levites, were put to shame, and hallowed themselves, and brought in the ascending-sacrifices of the house of Yahweh.
Suka yanka ɗan ragon Bikin Ƙetarewa a rana ta goma sha huɗu na wata na biyu. Firistoci da Lawiyawa suka ji kunya suka tsarkake kansu, suka kawo hadayun ƙonawa a haikalin Ubangiji.
16 And they stood in their place, according to their regulation, according to the law of Moses the man of God, —the priests, dashing the blood, [which they received] at the hand of the Levites.
Sa’an nan suka ɗauki matsayinsu na kullum yadda yake a Dokar Musa mutumin Allah. Firistoci suka yayyafa jinin da Lawiyawa suka ba su.
17 For there were many in the convocation, who had not hallowed themselves, —but, the Levites, were over the slaughtering of the passover-lambs, for every one who was, not pure, to hallow him unto Yahweh.
Da yake da yawa cikin taron ba su tsarkake kansu ba, dole Lawiyawa su yanka’yan ragunan Bikin Ƙetarewa domin dukan waɗanda ba su da tsarki, ba su kuma iya tsarkake ragunansu ga Ubangiji ba.
18 For, the multitude of the people, many out of Ephraim and Manasseh, Issachar and Zebulun, had not purified themselves, for they did eat the passover, otherwise than as was written, —for Hezekiah prayed for them, saying, May Yahweh the Good, put a propitiatory-covering about
Ko da yake yawancin mutanen da suka zo daga Efraim, Manasse, Issakar da Zebulun ba su tsarkake kansu ba, duk da haka suka ci Bikin Ƙetarewa, ba tare da bin abin da yake a rubuce ba. Amma Hezekiya ya yi addu’a dominsu cewa, “Bari Ubangiji, wanda yake nagari, yă gafarta wa kowa
19 every one who hath prepared, his heart, to seek God, even Yahweh, God of his fathers, —though not according to the purification of the sanctuary!
wanda ya sa zuciyarsa ga neman Allah, Ubangiji Allah na kakanninsa, ko da shi marar tsarki ne bisa ga dokokin wuri mai tsarki.”
20 And Yahweh hearkened unto Hezekiah, and healed the people.
Ubangiji kuwa ya ji Hezekiya ya kuma warkar da mutane.
21 And so the sons of Israel who were found in Jerusalem kept the festival of unleavened cakes seven days, with great rejoicing, —and the Levites and the priests, were offering praise unto Yahweh day by day, with loud instruments, unto Yahweh.
Isra’ilawan da suka kasance a Urushalima suka yi Bikin Burodi Marar Yisti kwana bakwai da farin ciki mai girma, yayinda Lawiyawa da firistoci suke rera ga Ubangiji kowace rana, haɗe da kayan kiɗin yabon Ubangiji.
22 And Hezekiah spake unto the heart of all the Levites who were giving good instruction respecting Yahweh, —and they did eat the appointed feast seven days, sacrificing the peace-offerings, and offering praise unto Yahweh, God of their fathers.
Hezekiya ya yi magana mai ƙarfafawa ga dukan Lawiyawa waɗanda suka nuna ganewar fasaha a hidimar Ubangiji. Kwana bakwai suka ci rabonsu da aka tsara, suka miƙa hadayun salama, suka kuma yabi Ubangiji Allah na kakanninsu.
23 Then all the convocation took counsel, to keep seven days more, —and they kept seven days, with rejoicing.
Dukan mutanen suka yarda su ƙara kwana bakwai kuma, sai suka ci gaba da bikin cikin farin ciki har waɗansu kwana bakwai kuma.
24 For, Hezekiah king of Judah, presented to the convocation, a thousand bullocks and seven thousand sheep, and, the rulers, presented to the convocation, a thousand bullocks and ten thousand sheep, -and, priests in great numbers, hallowed themselves.
Hezekiya sarkin Yahuda ya tanada bijimai dubu ɗaya da tumaki da kuma awaki dubu bakwai wa taron, fadawa kuma suka tanada musu bijimai dubu da kuma tumaki da awaki dubu goma. Firistoci masu yawa suka tsarkake kansu.
25 So all the convocation of Judah, and the priests and the Levites, and all the convocation that came in out of Israel, rejoiced, —also the sojourners who were coming in out of the land of Israel, and the dwellers in Judah.
Taron gaba ɗaya na Yahuda suka yi farin ciki, tare da firistoci da kuma Lawiyawa da dukan waɗanda suka taru daga Isra’ila, har ma da baƙi waɗanda suka zo daga Isra’ila da waɗanda suke zama a Yahuda.
26 Thus was there great rejoicing, in Jerusalem, —for, since the days of Solomon son of David king of Israel, there had not been the like of this, in Jerusalem.
Aka yi farin ciki mai girma a Urushalima, gama tun zamanin Solomon ɗan Dawuda sarkin Isra’ila, ba a taɓa yin wani abu kamar haka a Urushalima ba.
27 Then rose up the priests the Levites, and blessed the people, and there was a hearkening unto their voice, —and their prayer entered into his holy dwelling-place, even into the heavens.
Firistoci da Lawiyawa suka tsaya suka albarkace mutane, Allah kuma ya ji su, gama addu’arsu ya kai sama, mazauninsa mai tsarki.