< 1 Samuel 29 >
1 Now the Philistines gathered together all their hosts, towards Aphek, —and, the Israelites, were encamping by the fountain, that is in Jezreel.
Filistiyawa suka tattara dukan rundunoninsu a Afek. Isra’ila kuwa suka yi sansani kusa da maɓulɓular da take Yezireyel.
2 And, the lords of the Philistines, were passing on by hundreds, and by thousands, —but, David and his men, were passing on in the rear, with Achish.
Sa’ad da sarakuna Filistiyawa suke wucewa da rundunarsu na mutum ɗari-ɗari da na dubu-dubu. Dawuda da mutanensa suna biye a baya tare da Akish.
3 Then said the princes of the Philistines, What are these Hebrews [doing]? And Achish said unto the princes of the Philistines—Is not this David, servant of Saul king of Israel, who hath been with me this year, or two, and I have found in him nothing, from the day of his coming over unto me unto this day?
Komandodin Filistiyawa suka ce, “Waɗannan Ibraniyawa kuma fa?” Akish ya ce, “Wannan shi ne Dawuda hafsan Shawulu, sarkin Isra’ila. Yana nan tare da ni shekara guda ke nan. Ban kuwa taɓa samunsa da wani lahani ba tun daga ranar da ya bar Shawulu.”
4 But the princes of the Philistines raged against him, and the princes of the Philistines said unto him—Let the man go back, that he may return unto the place which thou didst appoint him, and let him not go down with us, into battle, so shall he not become to us a traitor, in the battle, —for, wherewith, should this fellow gain favour with his lord? Would it not be with the heads of those men?
Amma komandodin Filistiyawa suka yi fushi, suka ce, “Ka sa mutumin nan yă koma zuwa wurin da ka ba shi yă zauna. Ba zai bi mu zuwa wurin yaƙi ba. Yana iya juya a kanmu lokacin yaƙin. Zai iya yin amfani da wannan zarafi yă ciccire kawunanmu don yă faranta wa maigidansa rai?
5 Is not this David, of whom they made responses in the dances, saying, —Saul, hath smitten, his thousands, But, David, his, tens of thousands?
Tuna fa, ba shi ne Dawuda ɗin da ake girmama da rawa da waƙoƙi ana cewa, “‘Shawulu ya kashe dubbai, Dawuda kuwa dubbun dubbai ba’?”
6 So Achish called for David, and said unto him—By the life of Yahweh, surely, upright, thou art, and, pleasing in mine eyes, have been thy going out and thy coming in with me, in the host, for I have found in thee no wrong, from the day of thy coming in unto me, until this day, —but, in the eyes of the lords, displeasing, thou art.
Saboda haka Akish ya kira Dawuda ya ce masa, “Muddin Ubangiji yana a raye, na amince da kai tun daga ranar da ka zo wurina har yă zuwa yau, ban same ka da wani laifi ba, na kuma yi farin ciki in sa ka a cikin sojojina don ka yi mini aiki. Amma masu mulki nawa ba su yarda da kai ba.
7 Now, therefore, return, and go in peace, —so shalt thou not do wrong in the eyes of the lords of the Philistines.
Sai ka juya ka koma ka isa lafiya ba tare da ɓata wa masu mulkin Filistiyawa rai ba.”
8 Then said David unto Achish—But what have I done? and what hast thou found in thy servant, from the day that I came before thee, unto this day, —that I may not go in and fight, with the enemies of my lord the king.
Dawuda ya ce wa Akish, “Me na yi? Ka taɓa samun bawanka da laifi tun daga ranar da na zo har zuwa yanzu? Ina dalilin da ba zan tafi tare da kai in yaƙi maƙiyin ranka yă daɗe, sarki ba?”
9 Then answered Achish, and said unto David, I acknowledge that, pleasing, thou art in mine eyes, as a messenger of God, —notwithstanding, the princes of the Philistines, have said, He shall not go up with us, into the battle.
Akish ya ce, “A ganina kai marar laifi ne kamar mala’ikan Allah, duk da haka shugabannin sojojin Filistiyawa sun ce, ‘Ba zai tafi yaƙi tare da mu ba.’
10 Now, therefore, rise up early in the morning, thou and the servants of thy lord who have come with thee, —yea, as soon as ye have risen early in the morning, and have light, then depart.
Ka tashi da sassafe, kai da bayin shugabanka da suka zo tare da kai. Da gari ya waye sai ku kama hanya.”
11 So David rose up early, he and his men, to depart in the morning, to return into the land of the Philistines, —but, the Philistines, went up to Jezreel.
Gari na wayewa tun da sassafe Dawuda da mutanensa suka tashi suka kama hanyar komawa ƙasar Filistiyawa. Filistiyawa kuwa suka haura zuwa Yezireyel.