< 1 Samuel 13 >
1 Saul was [thirty] years old when he began to reign; and, when he had reigned two years over Israel,
Shawulu yana da shekara talatin sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi sarautar Isra’ila shekara arba’in da biyu.
2 Saul chose him three thousand men out of Israel, of whom there were with Saul, two thousand in Michmash and in the hill-country of Bethel, and, a thousand, were with Jonathan, in Gibeah of Benjamin, —but, the rest of the people, he let go, every man to his own home.
Sai ya zaɓi sojoji dubu uku daga jama’ar Isra’ila. Ya keɓe dubu biyu su kasance tare da shi a Mikmash da kuma a tuddan yankin Betel. Ya kuma bar dubu ɗaya tare da ɗansa Yonatan a Gibeya a yankin zuriyar Benyamin. Sauran sojojin kuwa Shawulu ya sallame su su koma gidajensu.
3 Then did Jonathan smite the garrison of Philistines that was in Geba, and the Philistines heard of it, —and, Saul, blew with a horn throughout all the land saying, Let the Hebrews hear!
Yonatan ya kai wa Filistiyawa hari a Geba, sai Filistiyawa suka sami labarin. Sai Shawulu ya sa aka busa ƙaho ko’ina a ƙasar ya ce, “Bari Ibraniyawa su ji!”
4 And, all Israel, heard say—Saul hath smitten the garrison of the Philistines, Moreover, also, Israel have made themselves odious among the Philistines, —so the people were called together to follow Saul, to Gilgal.
Haka kuwa dukan Isra’ila suka ji labari cewa, “Shawulu ya kai hari a ƙasar Filistiyawa, yanzu Isra’ila ta zama abin ƙi ga Filistiyawa.” Aka kira mutane su haɗu da Shawulu a Gilgal.
5 And, the Philistines, gathered themselves together to fight with Israel, thirty thousand chariots, and six thousand horsemen, a people also like the sand that is on the sea-shore for multitude, —and they came up, and encamped in Michmash, east of Beth-aven.
Sai Filistiyawa suka taru don su yi yaƙi da Isra’ilawa. Suka fito da kekunan-dawakan yaƙi dubu talatin, da masu hawan dawakai dubu shida, da sojoji masu yawa kamar yashi a bakin teku. Suka tafi Mikmash a gabashin Bet-Awen, suka kafa sansani a can.
6 So, the men of Israel, saw they were in a strait, for the people had been harassed, —and the people had hidden themselves in caves, and in thickets, and among cliffs, and in holes, and in pits.
Sa’ad da Filistiyawa suka fāɗa wa Isra’ilawa da yaƙi mai tsanani, suka sa su cikin wani hali mai wuya, sai Isra’ilawa suka ɓuya a kogwanni, da ciyayi, da duwatsu, da ramummuka, da rijiyoyi.
7 And, Hebrews, had passed over the Jordan, to the land of Gad, and Gilead, —but, Saul, was yet in Gilgal, and all the people, trembled after him.
Waɗansunsu ma suka haye Urdun zuwa ƙasar Gad da Gileyad. Shawulu ya zauna Gilgal, dukan ƙungiyoyi sojojin da suke tare da shi suka yi rawan jiki don tsoro.
8 And he waited seven days, by the set time that Samuel had named, but Samuel came not to Gilgal, —and the people were scattered from him.
Ya jira har kwana bakwai bisa ga lokacin da Sama’ila ya bayar. Amma Sama’ila bai zo Gilgal ba, mutanen Shawulu suka fara watsewa.
9 Then said Saul, Bring near unto me, the ascending-sacrifice and the peace-offerings. And he offered up the ascending-sacrifice.
Sai ya ce, “Ku kawo mini hadaya ta ƙonawa da hadaya ta salama.” Sai Shawulu ya miƙa hadaya ta ƙonawa.
10 And it came to pass, as he had made an end of offering up the ascending-sacrifice, lo! Samuel, had come, —and Saul went out to meet him, that he might bless him.
Daidai yana gama miƙa hadaya ke nan sai Sama’ila ya iso. Shawulu kuma ya fito domin yă yi masa maraba.
11 Then said Samuel—What hast thou done? And Saul said—Because I saw that the people had been scattered from me, and, thou, hadst not come within the appointed days, and, the Philistines, had gathered themselves together to Michmash,
Sama’ila ya ce, “Me ke nan ka yi?” Shawulu ya ce, “Sa’ad da na ga mutane suna watsewa, kai kuwa ba ka zo cikin lokaci ba, ga Filistiyawa kuma suna taruwa a Mikmash,
12 therefore I said—Now, will the Philistines come down against me, at Gilgal, but, the face of Yahweh, have I not appeased: So I forced myself, and offered up the ascending-sacrifice.
sai na yi tunani cewa, ‘Yanzu Filistiyawa za su gangaro su fāɗa mini a Gilgal, ga ni kuma ban riga na nemi nufin Ubangiji ba.’ Shi ya sa ya zama mini tilas in miƙa hadaya ta ƙonawa.”
13 And Samuel said unto Saul—Thou hast shewn thyself foolish, —thou hast not kept the commandment of Yahweh thy God, which he commanded thee, for, now, would Yahweh have established thy kingdom unto Israel until times age-abiding;
Sama’ila ya ce, “Ka yi wauta da ba ka bi umarnin da Ubangiji Allahnka ya ba ka ba. Da ka yi haka da Ubangiji ya tabbatar maka da sarautar Isra’ila har abada.
14 Whereas, now, shall thy kingdom not be established, —Yahweh hath sought out for him a man after his own heart, and Yahweh hath commanded him to be leader over his people, because thou hast not kept that which Yahweh commanded thee.
Amma yanzu, masarautarka ba za tă dawwama ba, Ubangiji ya riga ya sami wani wanda zuciyarsa ke ƙauna, ya naɗa shi shugaban mutanensa gama ba ka bi umarnin Ubangiji ba.”
15 And Samuel arose, and ascended from Gilgal unto Gibeah of Benjamin. And Saul numbered the people who were found with him, about six hundred men.
Sama’ila ya tashi daga Gilgal ya tafi Gibeya a ƙasar Benyamin. Shawulu kuma ya ƙidaya mutanen da suke tare da shi, yawansu ya kai wajen mutum ɗari shida.
16 Now, Saul, and Jonathan his son, and the people that were found with him, were abiding in Geba of Benjamin, —but, the Philistines, had encamped in Michmash.
Shawulu da ɗansa Yonatan da mutanen da suke tare da shi suka zauna a Geba ta Benyamin. Sa’an nan Filistiyawa suka yi sansani a Mikmash.
17 And the spoilers came forth out of the camp of the Philistines, in three companies, the first company, turned unto the way of Ophrah, unto the land of Shual;
Rundunar mayaƙa uku suka fito daga sansani Filistiyawa. Ɗaya ta nufi Ofra, zuwa ƙasar Shuwal.
18 and, the second company, turned unto the way of Beth-horon, —and, the third company, turned unto the way of the boundary that overlooketh the valley of Zeboim, towards the wilderness.
Runduna guda kuma ta nufi Bet-Horon, ɗayan kuwa ta nufi iyakar da take fuskantar Kwarin Ziboyim wajen jeji.
19 Now, a smith, could not be found, throughout all the land of Israel—for the Philistines had said, Lest the Hebrews make sword or spear.
Ba a sami maƙeri ɗaya a dukan ƙasar Isra’ila ba domin Filistiyawa sun ce, “In ba haka ba Ibraniyawa za su ƙera wa kansu takuba ko māsu.”
20 So all Israel went down to the Philistines, —to sharpen every man his share, and his mattock, and his axe, and his sickle.
Saboda haka dukan Isra’ila sukan gangara zuwa wajen Filistiyawa domin su gyara bakin garemaninsu, da fartanansu, da gaturansu, da kuma laujunansu.
21 Howbeit they had a file for the sickles, and the mattocks, and the three-pronged forks, and the axes, —and for setting the goads.
Duk lokacin da za su gyara bakin garmansu da fartanyarsu sai sun biya tsabar azurfa biyu. Haka ma idan za su gyara gatari ko bakunan abin korar shanun noma sai sun biya tsabar azurfa ɗaya.
22 Thus would it come to pass, in the day of battle, that there was found—neither sword nor spear, in the hand of any of the people, that were with Saul and Jonathan, but such were found belonging to Saul and to Jonathan his son.
A ranar da yaƙi ya tashi, ba a sami wanda yake da takobi ko māshi ba a cikin mutanen da suke tare da Shawulu da Yonatan. Sai dai Shawulu da ɗansa Yonatan kaɗai.
23 Now the garrison of the Philistines had come out to the pass of Michmash.
Ana nan sai sojojin Filistiyawa suka fita zuwa mashigin Mikmash.