< 1 Kings 1 >
1 Now, King David, was old, advanced in days, —and they covered him with clothes, but he gat no heat.
Sa’ad da Sarki Dawuda ya tsufa ya kuma ƙara shekaru, ba ya iya jin ɗumi ko an rufe shi da abin rufuwa.
2 Wherefore his servants said unto him—Let there be sought for my lord the king, a young woman—a virgin, so shall she stand before the king, that she may become his companion, —and she shall lie in thy bosom, and my lord the king shall get, heat.
Saboda haka bayinsa suka ce masa, “Bari mu nemi wata budurwa wadda za tă yi wa ranka yă daɗe, sarki hidima, tă kuma kula da shi. Za tă dinga kwanta kusa da ranka yă daɗe, yă ji ɗumi.”
3 So they sought a fair young woman, throughout all the bounds of Israel, —and found Abishag, the Shunammite, and brought her in, unto the king.
Suka nemi kyakkyawar yarinya cikin fāɗin Isra’ila, sai suka sami Abishag, mutuniyar Shunam, suka kawo ta wa sarki.
4 Now, the young woman, was exceeding fair, —so she became unto the king a companion, and ministered unto him, but, the king, knew her not.
Yarinyar kuwa kyakkyawa ce ƙwarai; ta kuwa lura da sarki, ta kuma yi masa hidima, amma sarki bai yi jima’i da ita ba.
5 And, Adonijah son of Haggith, exalted himself, saying—I, will be king. Therefore prepared he for himself chariots and horsemen, and fifty men to run before him.
Adoniya, wanda mahaifiyarsa ce Haggit, ya fito ya ce, “Zan zama sarki.” Saboda haka ya nemi kekunan yaƙi, ya kuma shirya dawakai, tare da mutane hamsin da za su sha gabansa.
6 Now his father had not displeased him all his days, by saying—Why, thus, hast thou done? Moreover also, he, was of exceeding handsome appearance, and, him, did his mother bear, after Absolom.
(A duk rayuwarsa mahaifinsa bai taɓa tsawata masa yă ce, “Me ya sa kake yin haka ba?” Shi kuwa mai kyan gani ne ƙwarai, shi ne aka haifa bayan Absalom.)
7 So then he had speech with Joab, son of Zeruiah, and with Abiathar the priest, —and they gave help, following Adonijah.
Adoniya ya haɗa baƙi da Yowab ɗan Zeruhiya da kuma Abiyatar firist, suka kuma ba shi goyon baya.
8 But, Zadok the priest, and Benaiah son of Jehoiada, and Nathan the prophet, and Shimei, and Rei, and the mighty men who belonged to David, were not with Adonijah.
Amma Zadok firist, Benahiya ɗan Yehohiyada, annabi Natan, Shimeyi, Reyi da kuma matsara na musamman na Dawuda ba su bi Adoniya ba.
9 And Adonijah sacrificed sheep and oxen and heifers, near the stone of Zoheleth, which is beside En-rogel, —and invited all his brethren, sons of the king, and all the men of Judah, servants of the king;
Wata rana Adoniya ya tafi Dutsen Zohelet kusa da En Rogel, inda ya yi hadayar tumaki, da shanun noma, da shanun da ake kiwo a gida. Ya kuma gayyaci’yan’uwansa, wato, sauran’ya’yan Sarki Dawuda, tare da dukan dattawan sarki da suka fito daga Yahuda,
10 but, Nathan the prophet, and Benaiah, and the mighty men, and Solomon his brother, he invited not.
amma bai gayyaci annabi Natan, ko Benahiya, ko wani daga matsara na musamman, ko kuwa ɗan’uwansa Solomon ba.
11 Then spake Nathan unto Bath-sheba mother of Solomon, saying—Hast thou not heard that Adonijah son of Haggith hath become king, and, our lord David, knoweth it not?
Sai Natan ya ce wa Batsheba, mahaifiyar Solomon, “Ki san cewa Adoniya, ɗan Haggit, ya zama sarki ba tare da sanin ranka yă daɗe, sarkinmu Dawuda ba?
12 Now, therefore, come; let me give thee counsel, I pray thee, —so shalt thou rescue thine own life, and the life of thy son, Solomon.
Yanzu bari in ba ki shawara yadda za ki cece ranki da kuma ran ɗanki Solomon.
13 Go, and get thee in unto King David, and thou shalt say unto him—Didst not, thou thyself, my lord O king, swear unto thy handmaid, saying—Solomon thy son, shall become king after me, yea, he, shall sit upon my throne? Why, then, hath, Adonijah, become king?
Ki shiga wurin Sarki Dawuda ki ce masa, ‘Ranka yă daɗe sarki, ba ka rantse mini ni baiwarka cewa, “Tabbatacce Solomon ɗanka ne zai zama sarki bayana, yă kuma zauna a kujerar sarautar ba”? To, me ya sa Adoniya ya zama sarki?’
14 Lo! while thou art yet speaking there with the king, I also, will come in after thee, and confirm thy words.
Yayinda kike can kina magana da sarki, zan shiga in kuma tabbatar da abin da kika faɗa.”
15 So Bath-sheba went in unto the king, into the chamber, now, the king, was very old, —and Abishag the Shunammite, was ministering unto the king.
Saboda haka Batsheba ta je don tă ga sarki. A yanzu dai sarki ya tsufa, yana nan kuma a cikin ɗakinsa, inda Abishag mutuniya Shunam take masa hidima.
16 And Bath-sheba bowed, and did homage unto the king, —and the king said—What aileth thee?
Batsheba ta rusuna ta kuma durƙusa a gaban sarki. Sai sarki ya tambaye ta ya ce, “Me kike so?”
17 And she said unto him—My lord, thou thyself, didst swear by Yahweh thy God, unto thy handmaid, Assuredly, Solomon thy son, shall become king after me, —yea, he, shall sit upon my throne.
Ta ce masa, “Ranka yă daɗe, kai kanka ka rantse mini ni baiwarka da sunan Ubangiji Allahnka cewa, ‘Solomon ɗanka zai zama sarki bayana, zai kuma zauna a kujerar sarautata.’
18 But, now, lo! Adonijah, hath become king; now, therefore, my lord, O king, thou knowest it not:
Amma yanzu Adoniya ya zama sarki, kai kuwa ranka yă daɗe sarki, ba ka san wani abu game da shi ba.
19 and he hath sacrificed oxen and heifers and sheep, in abundance, and hath invited all the sons of the king, and Abiathar the priest, and Joab general of the army, —but, Solomon thy servant, hath he not invited.
Ya miƙa hadayun shanu, da shanun da ake kiwo a gida, da tumaki masu yawa, ya kuma gayyaci dukan’ya’yan sarki maza, da Abiyatar firist, da Yowab shugaban mayaƙa, amma bai gayyaci Solomon bawanka ba.
20 Thou, therefore, my lord, O king, the eyes of all Israel, are upon thee, —to tell them, who shall sit upon the throne of my lord the king, after him.
Ranka yă daɗe sarki, idanun dukan Isra’ila suna a kanka, domin su san wa zai zauna a kujerar ranka yă daɗe sarkina, a bayanka.
21 Otherwise it shall come to pass, when my lord the king shall sleep with his fathers, then shall I and my son Solomon be counted, offenders.
In ba haka, bayan an binne ranka yă daɗe sarki, tare da kakanninsa, za a wulaƙance ni da Solomon ɗana, kamar masu laifi.”
22 And lo! while yet she was speaking with the king, Nathan the prophet, came in.
Yayinda take cikin magana tare da sarki, sai annabi Natan ya iso.
23 So they told the king, saying, Lo! Nathan the prophet! And, when he had come in before the king, he bowed himself down to the king with his face to the ground.
Sai aka faɗa wa sarki, “Ga annabi Natan.” Da Natan ya je gaban sarki, sai ya rusuna da fuskarsa har ƙasa.
24 Then said Nathan—My lord, O king, hast, thou, said, Adonijah, shall become king after me, —yea, he, shall sit upon my throne?
Natan ya ce, “Ranka yă daɗe, sarki, ko ka furta cewa Adoniya ne zai zama sarki a bayanka, yă kuma zauna a kujerar sarautarka?
25 For he hath gone down to-day, and hath sacrificed oxen and heifers and sheep, in abundance, and hath invited all the sons of the king, and the generals of the army, and Abiathar the priest, and, there they are—eating and drinking before him, —and they have said—Long live King Adonijah!
Yau ya gangara, ya kuma miƙa hadayun shanu, da shanun da ake kiwo a gida, da tumaki masu yawa. Ya gayyaci dukan’ya’yan sarki maza, da shugaban mayaƙa, da kuma Abiyatar firist. A yanzu haka suna ci, suna sha, tare da shi, suna cewa, ‘Ran Sarki Adoniya yă daɗe!’
26 But, me, even me thy servant, and Zadok the priest, and Benaiah son of Jehoiada, and Solomon thy servant, hath he not invited.
Amma bai gayyace ni bawanka, da Zadok firist, da Benahiya ɗan Yehohiyada, da kuma bawanka Solomon ba.
27 If, of my lord the king, this thing had been brought to pass, then wouldest thou not have made known unto thy servant, who should sit upon the throne of my lord the king, after him?
Ranka yă daɗe, sarki, ko ka tabbatar da haka, amma ba ka ko faɗa wa fadawanka, cewa ga wanda zai gāje Ranka yă daɗe, sarki ba?”
28 Then responded King David, and said, Call me Bath-sheba. So she came in before the king, and stood before the king.
Sai Dawuda ya ce, “Kira Batsheba tă shiga.” Sai ta zo gaban sarki ta kuma tsaya a gabansa.
29 And the king sware, and said, —By the life of Yahweh, who hath redeemed my life out of every strait,
Sai sarki ya yi rantsuwa, “Muddin Ubangiji yana a raye, wanda ya cece ni daga kowace damuwa,
30 even as I sware unto thee by Yahweh, God of Israel, saying, Assuredly, Solomon thy son, shall become king after me, yea, he, shall sit upon my throne, in my stead, even so, will I do this day.
tabbatacce a yau zan aikata abin da na yi miki rantsuwa da sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila; Solomon ɗanki zai zama sarki bayana, kuma shi zai zauna a kan kujerar sarautata a maimakona.”
31 Then Bath-sheba bowed with her face to the ground, and did homage unto the king, —and said—Let my lord, King David, live to times age-abiding!
Sai Batsheba ta rusuna da fuskarta har ƙasa, ta kuma durƙusa a gaban sarki ta ce, “Bari ran Sarkina Dawuda yă daɗe, har abada!”
32 Then said King David—Call me Zadok the priest, and Nathan the prophet, and Benaiah son of Jehoiada. And they came in before the king.
Sarki Dawuda ya ce, “Ku kira mini Zadok firist, annabi Natan, da Benahiya ɗan Yehohiyada.” Da suka zo gaban sarki,
33 Then said the king unto them—Take ye with you the servants of your lord, and cause Solomon my son to ride upon the mule which pertaineth unto myself, —and bring him down unto Gihon;
sai ya ce musu, “Ku ɗauki bayin sarki tare da ku, ku kuma sa ɗana Solomon a kan dokina, ku gangara da shi zuwa Gihon.
34 then shall Zadok the priest and Nathan the prophet anoint him there as king over Israel, —and ye shall blow with the horn, and say—Long live King Solomon!
A can ku sa Zadok firist, da annabi Natan su shafe shi sarki a bisa Isra’ila. Ku busa ƙaho, ku kuma yi ihu, kuna cewa, ‘Ran Sarki Solomon yă daɗe!’
35 Then shall ye come up after him, and he shall enter, and sit upon my throne, yea, he, shall become king in my stead; even, him, have I charged to become leader, over Israel, and over Judah.
Sa’an nan ku haura tare da shi, zai kuwa zo yă zauna a kujera sarautata, yă yi mulki a maimakona. Na naɗa shi mai mulki a bisa Isra’ila da Yahuda.”
36 Then did Benaiah son of Jehoiada make response unto the king, and say—Amen! so, say Yahweh, God of my lord the king.
Benahiya ɗan Yehohiyada ya amsa wa sarki, ya ce, “Amin! Bari Ubangiji Allah na ranka yă daɗe sarkina, yă tabbatar da haka.
37 As Yahweh hath been with my lord the king, so, let him he with Solomon, —and make his throne greater than the throne of my lord, King David.
Kamar yadda Ubangiji ya kasance da ranka yă daɗe, sarki, haka ma bari yă kasance da Solomon, yă kuma mai da kujerar sarautarsa tă fi kujerar sarautar ranka yă daɗe, Sarki Dawuda, girma!”
38 So Zadok the priest, and Nathan the prophet, and Benaiah son of Jehoiada, with the Cherethites and the Pelethites, went down, and caused Solomon to ride upon the mule of King David, —and they escorted him to Gihon.
Sai Zadok firist, annabi Natan, Benahiya ɗan Yehohiyada, Keretawa, da Feletiyawa suka gangara, suka sa Solomon a kan dokin Sarki Dawuda, suka raka shi zuwa Gihon.
39 Then took Zadok the priest, the horn of oil out of the Tent, and anointed Solomon, —and they blew with a [ram’s] horn, and all the people said, Long live King Solomon!
Zadok firist ya ɗauki ƙahon mai daga tenti mai tsarki, ya shafe Solomon. Sa’an nan suka busa ƙaho, sai dukan mutane suka yi ihu, suna cewa “Ran Sarki Solomon yă daɗe!”
40 And all the people came up after him, the people themselves also, playing with flutes, and rejoicing with great joy, —so that the earth rent with the sound of them.
Dukan mutane kuwa suka haura suka bi shi, suna busan sarewa, suna farin ciki sosai, har ƙasa ta girgiza saboda sowa.
41 And Adonijah, and all the guests who were with him, heard it, just as, they, had made an end of eating, —and, when Joab heard the sound of a horn, he said—Wherefore the noise of the city, in tumult?
Adoniya tare da dukan baƙin da suke tare da shi kuwa suka ji wannan sa’ad da suke gama bikinsu. Da jin busan ƙaho, sai Yowab ya yi tambaya, ya ce, “Me ya jawo surutu haka a birni?”
42 While yet he was speaking, lo! Jonathan son of Abiathar the priest, came in, —and Adonijah said—Come in, for, a worthy man, thou art, and, good tidings, dost thou bring.
Tun yana cikin magana, sai Yonatan ɗan Abiyatar ya iso. Adoniya ya ce, “Shigo! Ai, mutumin kirki irinka, lalle ka kawo labari mai daɗi ne.”
43 But Jonathan responded and said to Adonijah, —Of a truth, our lord, King David, hath made, Solomon, king.
Yonatan ya ce wa Adoniya, “A ina! Ranka yă daɗe, Sarkinmu Dawuda ya naɗa Solomon sarki.
44 And the king hath sent with him—Zadok the priest, and Nathan the prophet, and Benaiah son of Jehoiada, with the Cherethites, and the Pelethites, —and they have caused him to ride upon the mule of the king;
Sarki ya aika shi tare da Zadok firist, annabi Natan, Benahiya ɗan Yehohiyada, Keretawa, da Feletiyawa, suka sa shi a kan dokin sarki,
45 and Zadok the priest and Nathan the prophet have anointed him king, in Gihon, and they went up from thence rejoicing, so that the city rang again, —That, is the noise ye have heard.
Zadok firist kuwa da annabi Natan sun shafe shi sarki a Gihon. Daga can suka haura suna kirari, birni kuwa ta ɓarke da sowa. Surutun da kake ji ke nan.
46 Moreover also, Solomon hath taken his seat upon the throne of the kingdom.
Ban da haka ma, Solomon ne sarki yanzu.
47 Moreover also, the servants of the king have been in, to bless our lord King David, saying—Thy God make the name of Solomon better than thy name, and make his throne greater than thy throne, —And the king bowed himself upon his bed.
Yanzu haka, fadawa sun zo suna wa ranka yă daɗe, Sarki Dawuda, sam barka, suna cewa, ‘Bari Allahnka yă sa sunan Solomon yă zama sananne fiye da naka, bari kuma sarautarsa tă fi taka girma!’ Sarki kuwa ya rusuna, ya yi sujada a kan gadonsa
48 Moreover also, thus and thus, hath said the king, —Blessed be Yahweh, God of Israel, who hath given, to-day, one to sit upon my throne, mine own eyes also beholding it.
ya ce, ‘Yabo ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, wanda ya bar idanuna suka ga magāji a kan kujerar sarautata a yau.’”
49 Then trembled and rose up, all Adonijah’s guests, —and departed, every man his own way.
A nan fa, dukan baƙin Adoniya suka taso da rawar jiki suka watse.
50 Adonijah also, feared because of Solomon, —and rose and went, and caught hold of the horns of the altar.
Amma Adoniya, don tsoron Solomon, ya je ya kama ƙahon bagade ya riƙe.
51 And it was told Solomon, saying, Lo! Adonijah, feareth King Solomon, —lo! therefore, he hath laid hold of the horns of the altar, saying, Let King Solomon swear unto me at once that he will not put his servant to death with the sword.
Sa’ad da aka faɗa wa Solomon cewa, “Adoniya yana tsoron Sarki Solomon, kuma ya manne wa ƙahonin bagade. Yana cewa, ‘Bari Sarki Solomon yă rantse mini a yau cewa ba zai kashe bawansa da takobi ba.’”
52 Then said Solomon, If he will be a man of worth, there shall not one hair of him fall to the earth, —but, if mischief be found in him, then shall he die.
Solomon ya amsa ya ce, “In ya nuna kansa mai biyayya, ba gashin kansa da zai fāɗi ƙasa; amma in aka same mugunta a cikinsa, zai mutu.”
53 So King Solomon sent, and brought him down from the altar, and he came in, and bowed himself down to King Solomon, —and Solomon said unto him—Go to thine own house.
Sai Sarki Solomon ya aiki mutane, suka kuma sauko da shi daga bagade. Adoniya kuwa ya zo, ya rusuna wa Sarki Solomon, sai Solomon ya ce, “Tafi gidanka.”