< 1 Corinthians 1 >
1 Paul, a called apostle of Jesus Christ, through God’s will, —and Sosthenes the brother, —
Bulus, wanda aka kira domin yă zama manzon Kiristi Yesu, bisa ga nufin Allah, da kuma ɗan’uwanmu Sostenes,
2 Unto the assembly of God which is in Corinth, sanctified in Christ Jesus, called saints, —with all who call upon the name of our Lord Jesus Christ, in every place, —their Lord and ours:
Zuwa ga ikkilisiyar Allah da take a Korint, da waɗanda aka tsarkake cikin Kiristi Yesu, aka kuma kira domin su zama masu tsarki, tare da dukan waɗanda suke ko’ina da suke kiran sunan Ubangijinmu Yesu Kiristi, Ubangijinsu da kuma namu.
3 Favour unto you, and peace, from God our Father, and Lord Jesus Christ.
Alheri da salama daga Allah Ubanmu, da Ubangiji Yesu Kiristi, su kasance tare da ku.
4 I give thanks unto my God, at all times, concerning you, by reason of the favour of God given unto you in Christ Jesus, —
Ina gode wa Allah kullum dominku, saboda alherinsa da aka ba ku a cikin Kiristi Yesu.
5 That, in everything, ye have been enriched in him—in all discourse and in all knowledge;
Gama a cikinsa kuka sami wadata ta kowace hanya, a cikin dukan maganarku, da kuma cikin dukan saninku
6 Even as, the witness of the Christ, hath been confirmed in you,
gama shaidarmu game da Kiristi ta tabbata a cikinku.
7 So that ye come short in no gift of favour, —ardently awaiting the revelation of our Lord Jesus Christ:
Saboda haka, ba ku rasa kowace baiwa ta ruhaniya ba, yayinda kuke jira da marmari, saboda bayyanuwar Ubangijinmu Yesu Kiristi.
8 Who will also confirm you unto the end, unaccusable in the day of our Lord Jesus [Christ]:
Zai ƙarfafa ku har zuwa ƙarshe, domin ku zama marasa aibi a ranar Ubangijinmu Yesu Kiristi.
9 Faithful, is God, through whom ye have been called into the fellowship of his Son Jesus Christ our Lord.
Allah, wanda ya kira ku zuwa ga zumunci tare da Ɗansa Yesu Kiristi Ubangijinmu, shi mai aminci ne.
10 But I beseech you, brethren, through the name of our Lord Jesus Christ, —that, the same thing, ye, all, be saying, and that there be not, among you, divisions; but that ye be fitly joined together—in the same mind, and in the same judgment.
Ina roƙonku’yan’uwa, a cikin sunan Ubangijinmu Yesu Kiristi, dukanku ku yarda da juna, domin kada a sami tsattsaguwa a cikinku, domin kuma ku zama ɗaya, cikakku a cikin halinku da tunaninku.
11 For it hath been signified unto me, concerning you, my brethren, —by them who are of [the household of] Chloe, —that there are strifes among you,
’Yan’uwana, waɗansu daga iyalin gidan Kulos sun gaya mini cewa, akwai faɗa a cikinku.
12 Now I mean this, —that, each one of you, is saying—I, indeed, am of Paul, but, I, of Apollos, but, I, of Cephas, but, I, of Christ:
Abin da nake nufi shi ne, ɗaya daga cikinku na cewa, “Ni ina bin Bulus,” wani na cewa, “Ni ina bin Afollos,” wani kuma, “Ni ina bin Kefas,” har wa yau wani kuma, “Ni ina bin Kiristi.”
13 The Christ is divided! Was, Paul, crucified for you? Or, into the name of Paul, were ye immersed?
Kiristi a rabe ne? Bulus ne aka gicciye dominku? An yi muku baftisma a cikin sunan Bulus ne?
14 I give thanks, that, none of you, did I immerse—save Crispus and Gaius,
Ina godiya domin ban yi wa wani baftisma a cikinku ba, sai dai Kirisbus da Gayus kaɗai.
15 Lest any should say—into my own name, I immersed:
Don haka, ba wanda na iya cewa an yi muku baftisma a cikin sunana.
16 Yea! I immersed the house of Stephanas also, —besides, I know not whether, anyone else, I immersed.
(I, na kuma yi wa iyalin gidan Istifanas baftisma, ban da wannan, ban tuna da wani da na yi masa baftisma ba.)
17 For Christ sent me not, to be immersing, but to be telling the good news, —not with wisdom of discourse, lest, void should be made, the cross of the Christ.
Gama Kiristi bai aike ni yin baftisma ba, sai dai wa’azin bishara ba da kalmomin hikimar mutum ba, domin kada gicciyen Kiristi ya rasa ikonsa.
18 For, the discourse which concerneth the cross, unto them, indeed, who are perishing, is, foolishness; but, unto them who are being saved—unto us, it is, God’s power.
Gama saƙon gicciye wauta ne ga waɗanda suke hallaka, amma a gare mu, mu da ake ceto, ikon Allah ne.
19 For it is written—I will destroy the wisdom of the wise, and, the discernment of the discerning, will I set aside.
Gama a rubuce yake cewa, “Zan rushe hikimar mai hikima, basirar mai azanci kuma zan rikita shi.”
20 Where is the wise? Where is the scribe? Where is the disputer of this age? Hath not God made foolish the wisdom of the world? (aiōn )
Ina mai hikima? Ina mai zurfin bincike? Ina masana na wannan zamani? Ashe, Allah bai wofinta hikimar duniya ba? (aiōn )
21 For, seeing that, in the wisdom of God, the world, through its wisdom, did not get to knew God, God was well-pleased—through the foolishness of the thing proclaimed, to save them that believe.
Gama tun da a cikin hikimar Allah, duniya a cikin hikimarta ba tă san shi ba, Allah ya ji daɗin ceton waɗanda suka ba da gaskiya ta wurin wautar wa’azin bishara.
22 Seeing that both, Jews for signs, do ask, and, Greeks for wisdom, do seek,
Yahudawa suna so su ga alama, Hellenawa kuma suna neman hikima,
23 Whereas, we, proclaim a Christ who hath been crucified, —unto Jews, indeed, an occasion of stumbling, and, unto Gentiles, foolishness;
amma mu, muna wa’azin Kiristi wanda aka gicciye ne, wanda ya zama dutsen tuntuɓe ga Yahudawa, wauta kuma ga Al’ummai,
24 But, unto the called themselves—both Jews and Greeks, Christ, God’s power, and, God’s wisdom.
amma ga su waɗanda Allah ya kira, Yahudawa da Hellenawa, Kiristi ikon Allah ne, da kuma hikimar Allah.
25 Because, God’s foolish thing, is, wiser than men, and, God’s weak thing, mightier than men.
Gama wautar Allah ta fi hikimar mutum, kuma rashin ƙarfin Allah ya fi ƙarfin mutum.
26 For be looking at the calling of you, brethren, —that [there were] not many wise, according to flesh. Not many powerful, not many high-born:
’Yan’uwa, ku tuna yadda kuke sa’ad da aka kira ku. Babu masu hikima da yawa a cikinku, bisa ga ganin mutum; babu masu iko da yawa, babu masu martaba da yawa bisa ga haihuwa.
27 On the contrary—the foolish things of the world, hath God chosen, that he might put to shame them who are wise, and, the weak things of the world, hath God chosen, that he might put to shame the things that are mighty,
Amma Allah ya zaɓi abubuwa masu wautata duniya, don yă kunyata masu hikima. Allah ya zaɓi abubuwa marasa ƙarfi na duniya, domin ya ba wa masu ƙarfi kunya.
28 And, the low-born things of the world, and the things that are despised, hath God chosen, —[and] the things that are not, —that, the things that are, he might bring to nought;
Ya zaɓi abubuwa marasa martaba na wannan duniya da kuma abubuwan da aka rena da abubuwan da ba a ɗauka a bakin kome ba, domin a wofinta abubuwan da ake ganinsu da daraja,
29 So that no flesh should boast before God.
domin kada wani ya yi taƙama a gabansa.
30 But, of him, are, ye, in Christ Jesus, who hath been made wisdom unto us, from God, —both righteousness, and sanctification, and redemption:
Saboda Allah ne kuke cikin Kiristi Yesu, shi wanda ya zama hikima a gare mu daga Allah. Kiristi shi ne adalcinmu, da tsarkinmu, da kuma fansarmu.
31 In order that, even as it is written—He that boasteth, in the Lord, let him boast.
Saboda haka, kamar yadda yake a rubuce cewa, “Duk wanda yake taƙama, ya yi taƙama a cikin Ubangiji.”