< 1 Chronicles 26 >

1 To the courses of the door-keepers, pertained, —of the Korahites, Meshelemiah son of Kore, of the sons of Asaph;
Ɓangarorin Matsaran Ƙofofi su ne, Daga Korayawa, Meshelemiya ɗan Kore, ɗaya daga cikin’ya’yan Asaf maza.
2 and, Meshelemiah, had sons, —Zechariah the firstborn, Jediael the second, Zebadiah the third, Jathniel the fourth;
Meshelemiya yana da’ya’ya maza. Zakariya ɗan fari, Yediyayel na biyu, Zebadiya na uku, Yatniyel na huɗu,
3 Elam the fifth, Jehohanan the sixth, Eliehoenai the seventh.
Elam na biyar, Yehohanan na shida da Eliyehoyenai na bakwai.
4 And, Obed-edom, had sons, —Shemaiah the firstborn, Jehozabad the second, Josh the third, and Sacar the fourth, and Nethanel the fifth;
Obed-Edom shi ma yana da’ya’ya maza. Shemahiya ɗan fari, Yehozabad na biyu, Yowa na uku, Sakar na huɗu Netanel na biyar,
5 Ammiel the sixth, Issachar the seventh, Peullethai, the eighth, —for God had blessed him.
Ammiyel na shida, Issakar na bakwai da Feyuletai na takwas. (Gama Allah ya albarkace Obed-Edom.)
6 And, to Shemaiah his son, were born sons, who bare rule to their ancestral house, —for, heroes of valour, were they.
Ɗan Obed-Edom, wato, Shemahiya shi ma yana da’ya’ya maza, waɗanda suke shugabanni a cikin iyalin mahaifinsu, gama su jarumawa ne ƙwarai.
7 the sons of Shemaiah, were Othni and Rephael, and Obed, Elzabad, whose brethren were sons of valour, —Elihu, and Semachiah.
’Ya’yan Shemahiya maza su ne, Otni, Rafayel, Obed da Elzabad; danginsa Elihu da Shemahiya su ma jarumawa ne.
8 All these, were of the sons of Obed-edom, they and their sons and their brethren, able men in strength for the service, —sixty-two, pertaining to Obed-edom.
Ɗaukan waɗannan zuriyar Obed-Edom ne; su da’ya’yansu maza da danginsu, jarumawa ne masu ƙarfin yin aiki. Zuriyar Obed-Edom, mutum 62 ne duka.
9 And, Meshelemiah, had sons, and brethren, sons of valour, eighteen.
Meshelemiya yana da’ya’ya maza da kuma’yan’uwa, waɗanda jarumawa ne, su 18 ne duka.
10 And, Hosah of the sons of Merari, had sons, —Shimri the chief, for though he was not the firstborn, yet his father, made him, chief.
Hosa dangin Merari yana da’ya’ya maza. Shimri na fari (ko da yake ba shi ne ɗan fari ba, mahaifinsa ya sa shi na fari),
11 Hilkiah the second, Tebaliah the third, Zechariah the fourth, —all the sons and brethren of Hosah, were thirteen.
Hilkiya ne na biyu, Tabaliya ne na uku sai kuma Zakariya na huɗu.’Ya’ya da dangin Hosa su 13 ne duka.
12 To these, belonged the courses of door-keepers, to the chiefs of the strong men, belonged charges, equally with their brethren, —to be in attendance in the house of Yahweh.
Waɗannan ɓangarori na matsaran ƙofofi, ta wurin manyansu, suna da ayyukan yin hidima a haikalin Ubangiji, kamar yadda danginsu suke da shi.
13 Yea they cast lots, as the small so the great, by their ancestral house, for every several gate.
Aka jefa ƙuri’u don kowace ƙofa bisa ga iyalansu, ƙarami da babba.
14 And the lot eastward fell to Shelemiah. And, for Zechariah his son, a discreet counsellor, they cast lots, and his lot came out, northward.
Ƙuri’a don Ƙofar Gabas ta fāɗo a kan Shelemiya. Sai aka jefa ƙuri’u don ɗansa Zakariya, mai ba da shawara mai ma’ana, sai ƙuri’a ta ƙofar arewa ta fāɗo a kansa.
15 To Obed-edom, southward, —and, to his sons, the storehouse.
Ƙuri’a don Ƙofar Kudu ta fāɗo a kan Obed-Edom, ƙuri’a don ɗakin ajiya kuwa ta fāɗo a kan’ya’yansa maza.
16 To Shuppim and to Hosah, westward, near the refuse-gate, in the causeway that goeth up, —one ward as well as another.
Ƙuri’u don Ƙofar Yamma da kuma Ƙofar Shalleket a hanyar bisa suka fāɗo a kan Shuffim da Hosa. Aikin tsaro bisa ga mai tsaro.
17 Eastward—daily, were six, —northward—daily, four, southward—daily, four, and, for the stores, two and two.
Akwai Lawiyawa shida da suke tsaron ƙofar gabas, huɗu a ƙofar kudu, huɗu kuma a ƙofar arewa, biyu-biyu suke tsaron ɗakunan ajiya.
18 For the precinct—westward, four, at the causeway, two—by the precinct.
Game da filin waje ta yamma kuwa, akwai masu tsaro huɗu a hanya da kuma biyu a filin kansa.
19 These, were the courses of the door-keepers, of the sons of the Korahites, and of the sons of Merari.
Waɗannan su ne ɓangarori na matsaran ƙofofi waɗanda suke zuriyar Kora da Merari.
20 And, the Levites, their brethren, were over the treasuries of the house of God, even to the treasuries of hallowed things.
’Yan’uwansu Lawiyawa kuwa su ne suke lura da ma’ajin gidan Allah da kuma baitulmali don kayayyakin da aka keɓe.
21 The sons of Ladan—the sons of the Gershonites belonging to Ladan—the ancestral chiefs belonging to Ladan the Gershonite, were Jehieli;
Ladan ɗan Gershon ne, kuma kaka ga iyalai masu yawa, har ma da iyalin ɗansa Yehiyeli,
22 the sons of Jehieli, Zetham and Joel his brother who were over the treasuries of the house of Yahweh.
’ya’yan Yehiyeli maza su ne, Zetam da ɗan’uwansa Yowel. Su ne suke kula da ma’ajin haikalin Ubangiji.
23 Then came certain of the Amramites, of the Izharites, of the Hebronites, of the Uzzielites.
Daga zuriyar Amram, Izhar, mutanen Hebron da kuma Uzziyel, su ma aka ba su aiki.
24 And, Shebuel, son of Gershom, son of Moses, was chief ruler over the treasuries.
Shebuwel ɗan Gershom, daga zuriyar Musa, shi ne babban jami’i mai lura da baitulmali.
25 And, his brethren pertaining to Eliezer, were Rehabiah his son, and Jeshaiah his son, and Joram his son, and Zichri his son, and Shelomoth his son.
Danginsa na wajen Eliyezer su ne, Rehabiya, Yeshahiya, Yoram, Zikri da Shelomit.
26 The same Shelomoth and his brethren, were over all the treasuries of the hallowed things, which David the king and the ancestral chiefs, with the captains of thousands and hundreds and the captains of the army, had hallowed:
Shelomit da danginsa su ne suke lura da dukan baitulmali don kayayyakin da Sarki Dawuda ya keɓe, ta wajen kawunan iyalai waɗanda suke shugabannin dubu-dubu da shugabannin ɗari-ɗari, da kuma wajen sauran shugabannin mayaƙa.
27 out of the battles and out of the spoil, had they hallowed [them], —to strengthen [the provision] for the house of Yahweh.
Sun keɓe waɗansu ganimar da aka kwaso a yaƙi don gyaran haikalin Ubangiji.
28 And, all that Samuel the seer, and Saul son of Kish, and Abner son of Ner, and Joab son of Zeruiah, had hallowed, whosoever had hallowed anything, it was under the direction of Shelomoth, and his brethren.
Shelomit da’yan’uwansa suka lura da dukan abubuwan da annabi Sama’ila da Shawulu ɗan Kish, da Abner ɗan Ner, da Yowab ɗan Zeruhiya suka keɓe.
29 Of the Izharites, Chenaniah and his sons, were for the outward business over Israel, —as officers, and as judges.
Daga mutanen Izhar, Kenaniya da’ya’yansa maza su aka sa a ayyukan da ba na haikali ba, su suka zama manya da kuma alƙalai a bisa Isra’ila.
30 Of the Hebronites, Hashabiah and his brethren, sons of valour, one thousand seven hundred, had the oversight of Israel, across the Jordan westward, —for all the business of Yahweh, and for the service of the king.
Daga zuriyar Hebron, Hashabiya da danginsa, su jarumawa dubu ɗaya da ɗari bakwai ne, su suke lura da Isra’ila yamma da Urdun don dukan aikin Ubangiji da kuma hidimar sarki.
31 Of the Hebronites, Jerijah, was chief, [he was] of the Hebronites by his generations, by his fathers, —in the fortieth year of the reign of David, were they sought out, and there were found among them heroes of valour, in Jazer of Gilead;
Game da zuriyar Hebron kuwa, Yeriya ne babba bisa ga tarihin zuriyar iyalansu. A shekara ta arba’in ta sarautar Dawuda, sai aka yi binciken tarihi, aka tarar jarumawa cikin zuriyar Hebron suna zama a Yazer cikin Gileyad ne.
32 and, his brethren that were heroes of valour, were two thousand and seven hundred, ancestral chiefs, —so David the king gave them oversight, over the Reubenites and the Gadites and the half tribe of Manassites, in all the affairs of God, and the affairs of the king.
Yeriya yana da’yan’uwa guda dubu biyu da ɗari bakwai, jarumawa da kuma kawunan iyalai, sai Sarki Dawuda ya sa su lura da mutanen Ruben, Gad da rabin kabilar Manasse game da kome da ya shafi Allah da kuma al’amuran sarki.

< 1 Chronicles 26 >