< 1 Chronicles 12 >

1 Now these, are they who came unto David, to Ziklag, he yet being shut up, because of Saul son of Kish, —and, they, were among the heroes, helpers in the war;
Waɗannan su ne mutanen da suka zo wurin Dawuda a Ziklag, yayinda aka kore shi daga gaban Shawulu ɗan Kish (suna cikin jarumawan da suka taimake shi a yaƙi;
2 armed with the bow, using right hand or left with stones, and with arrows in the bow, —of the brethren of Saul, out of Benjamin:
suna da baka suna kuma iya harba kibiya, ko majajjawa da hannun dama ko na hagu; su’yan’uwan Shawulu ne daga kabilar Benyamin):
3 the chief, Ahiezer, and Joash, sons of Shemaah the Gibeathite, and Jeziel and Pelet, sons of Azmaveth, —and Beracah, and Jehu the Anathothite;
Ahiyezer babbansu da Yowash’ya’yan Shema’a maza daga Gibeya; Yeziyel da Felet’ya’yan Azmawet; Beraka, Yehu daga Anatot,
4 and Ishmaiah, the Gibeonite, a hero among the thirty, and over the thirty, —and Jeremiah and Jahaziel, and Johanan, and Jozabad, the Gederathite;
da Ishmahiya daga Gibeyon, wani jarumi a cikin Talatin nan, wanda shi ne shugaban Talatin; Irmiya, Yahaziyel, Yohanan, Yozabad daga Gedera,
5 Eluzai and Jerimoth and Bealiah and Shemariah, and Shephatiah, the Haruphite;
Eluzai, Yerimot, Beyaliya, Shemariya da Shefatiya daga Haruf;
6 Elkanah and Isshiah, and Azarel, and Joezer and Jashobeam, the Korahites;
Elkana, Isshiya, Azarel, Yoyezer da Yashobeyam daga Kora;
7 and Joelah and Zebadiah, sons of Jeroham, of Gedor.
da Yoyela da Zebadiya’ya’yan Yeroham maza daga Gedor.
8 And, of the Gadites, there separated themselves unto David, to the stronghold towards the desert, heroes of valour, men of war, for battle, men that could handle shield and spear, —and, faces of lions, were their faces, and, like gazelles upon the mountains, were they, for swiftness:
Sai waɗansu mutanen Gad suka koma suna goyon bayan Dawuda suka kuma haɗa kai da shi a kagararsa a hamada. Su ƙwararrun mayaƙa ne, a shirye don yaƙi, kuma suna iya riƙe garkuwa da māshi. Fuskokinsu kamar fuskoki zakoki, kuma suna da sauri kamar bareyi a kan duwatsu.
9 Ezer, the chief, Obadiah, the second, —Eliab, the third;
Ezer shi ne babba, Obadiya shi ne mai binsa a shugabanci, Eliyab na uku,
10 Mashmannah, the fourth, Jeremiah, the fifth;
Mismanna na huɗu, Irmiya na biyar,
11 Attai, the sixth, Eliel the seventh;
Attai na shida, Eliyel na bakwai,
12 Johanan, the eighth, Elzabad, the ninth;
Yohanan na takwas, Elzabad na tara,
13 Jeremiah, the tenth, Machbannai, the eleventh.
Irmiya na goma da kuma Makbannai na goma sha ɗaya.
14 These, were of the sons of Gad, chiefs of the host, —one to a hundred, the least, and, the greatest, to a thousand.
Waɗannan mutanen Gad shugabannin mayaƙa ne; ƙarami a cikinsu zai iya ƙara da mutum ɗari, kuma babba a cikin zai iya ƙara da dubu.
15 These, are they who passed over the Jordan, in the first month, when, it, was full, over all its banks, —and they put to flight all them of the vales, to the east and to the west.
Su ne suka haye Urdun a wata na farko sa’ad da kogin ya yi ambaliya, suka kuma kori duk mai rai a kwarin, na wajen gabas da na wajen yamma.
16 And there came, of the sons of Benjamin, and Judah, as far as the stronghold, unto David.
Sauran mutanen Benyamin da waɗansu mutanen Yahuda su ma suka zo wurin Dawuda a kagararsa.
17 And David went forth to meet them, and responded, and said to them, If, peaceably, ye are come unto me, to help me, I shall have towards you, a heart for unity, —but, if to betray me to mine adversaries, there being no violence in my hands, may the God of our fathers see and rebuke!
Sai Dawuda ya fita don yă tarye su, ya kuma ce musu, “In kun zo wurina da salama, don ku taimake ni, to, ina a shirye in bar ku ku haɗa kai tare da ni. Amma in kun zo don ku bashe ni ga abokan gābana sa’ad da hannuwana ba su da laifi a rikici, bari Allah na kakanninmu yă duba yă kuma shari’anta ku.”
18 Then, the spirit, clothed Amasai, chief of the thirty, Thine, O David, Yea, with, thee, O son of Jesse! Prosperity, prosperity to thee, And prosperity to thy helpers, For thy God, hath helped thee: So David accepted them, and set them among the chiefs of the band.
Sai Ruhu ya sauko a kan Amasai, shugaban Talatin nan, sai ya ce, “Mu naka ne, ya Dawuda! Muna tare da kai, ya ɗan Yesse! Nasara, nasara gare ka, nasara kuma ga waɗanda suke taimakonka. Gama Allahnka zai taimake ka.” Saboda haka Dawuda ya karɓe su ya kuma mai da su shugabannin ƙungiyoyin maharansa.
19 And, of Manasseh, there fell away unto David, when he came with the Philistines against Saul to battle, but they helped them not, —for the lords of the Philistines advisedly sent him away, saying, At the price of our heads, he might fall away to his master, Saul.
Waɗansu mutanen Manasse suka haɗa kai da Dawuda sa’ad da ya tafi tare da Filistiyawa don yă yaƙi Shawulu (Shi da mutanensa ba su taimaki Filistiyawa ba domin bayan shawarwari, shugabanninsu suka salame shi. Sun ce, “Za mu biya da kawunanmu in ya koma ga maigidansa Shawulu.”)
20 When he went into Ziklag, there fell away unto him, of Manasseh, Adnah and Jozabad, and Jediael and Michael and Jozabad, and Elihu and Zillethai, —chiefs of the thousands that pertained to Manasseh;
Da Dawuda ya tafi Ziklag, waɗannan mutanen Manasse ne suka haɗa kai da shi. Adna, Yozabad, Yediyayel, Mika’ilu, Yozabad, Elihu da Zilletai, shugabannin ƙungiyoyi na dubu a cikin Manasse.
21 and, they, helped with David, against the [marauding] band, for, heroes of valour, were they all, —and they became captains in the host;
Suka taimaki Dawuda a kan ƙungiyoyin hari, gama dukansu jarumawa ne sosai, kuma su shugabanni ne a cikin mayaƙansa.
22 for, from day to day, there came unto David, to help him, —until it was a great camp, like a camp of God.
Kowace rana mutane suka riƙa zuwa don su taimaki Dawuda, sai da ya kasance da runduna mai girma, kamar mayaƙan Allah.
23 And, these, are the numbers of the chiefs armed for war, they came unto David, to Hebron, —to turn round the kingdom of Saul unto him, according to the bidding of Yahweh:
Ga yawan mutanen shiryayyu don yaƙi waɗanda suka zo wurin Dawuda a Hebron don su mai da mulkin Shawulu gare shi, yadda Ubangiji ya faɗa.
24 Sons of Judah, bearers of shield and spear, six thousand and eight hundred, armed for war.
Mutanen Yahuda, masu riƙe garkuwa da māshi, su 6,800 shiryayyu don yaƙi;
25 Of sons of Simeon, heroes of valour for the war, seven thousand, and one hundred.
mutanen Simeyon, jarumawa shiryayyu don yaƙi, su 7,100;
26 Of the sons of Levi, four thousand, and six hundred.
mutanen Lawi, su 4,600,
27 And Jehoiada, was chief ruler for Aaron, —and, with him, three thousand and seven hundred;
haɗe da Yehohiyada, shugaban iyalin Haruna tare da mutane 3,700,
28 and Zadok, a young man, a hero of valour, —and the house of his father, captains twenty and two.
da Zadok, matashi jarumi sosai, tare da shugabanni su 22 daga iyalinsa;
29 And, of the sons of Benjamin, brethren of Saul, three thousand, —and, hitherto, the greater part of them, had been keeping the charge of the house of Saul.
mutanen Benyamin,’yan’uwan Shawulu, su 3,000, yawanci waɗanda suke biyayya ga gidan Shawulu sai lokacin;
30 And, of the sons of Ephraim, twenty thousand, and eight hundred, —heroes of valour, men of renown, to their ancestral house.
mutanen Efraim, jarumawa, sanannu cikin gidajensu, su 20 800;
31 And, of the half tribe of Manasseh, eighteen thousand, who were distinguished by name, coming in to make David king.
mutanen rabin kabilar Manasse, sanannu da sunaye suka zo suka mai da Dawuda sarki, su 18,000;
32 And, of the sons of Issachar, such as were of good understanding of the times, to know what Israel, should do, their chiefs, were two hundred, and, all their brethren, were at their bidding.
mutanen Issakar, masu fahimtar lokuta suka kuma san abin da ya kamata Isra’ila ya yi, manya 200, tare da danginsu a ƙarƙashin shugabancinsu;
33 Of Zebulun—such as were ready to go forth in host, expert for battle with all weapons of war, fifty thousand, —and for setting in array, not of two minds!
mutanen Zebulun, ƙwararru sojoji shiryayyu don yaƙi da kowane irin makami, suka zo don su taimaki Dawuda da zuciya ɗaya, su 50,000;
34 And, of Naphtali, a thousand captains, —and, with them, with shield and spear, thirty-seven thousand.
mutanen Naftali su 1,000 shugabanni, tare da mutane 37,000 masu riƙe garkuwa da masu;
35 And, of the Danite, expert for war, twenty-eight thousand, and six hundred.
mutanen Dan, shiryayyu don yaƙi, su 28,600;
36 And, of Asher, such as were ready to go forth in host to set in array for battle, forty thousand.
mutanen Asher, ƙwararrun sojoji shiryayyu don yaƙi, su 40,000;
37 And, from over the Jordan, of the Reubenites and Gadites and half tribe of Manasseh, with all manner of weapons of war for battle, a hundred and twenty thousand.
kuma daga gabashin Urdun, mutanen Ruben, Gad da kuma rabin kabilar Manasse, masu kayan yaƙi iri-iri, su 120,000.
38 All these, being men of war, expert in setting in battle-array, with a perfect heart, came to Hebron, to make David king over all Israel, —moreover also, all the rest of Israel, were of one heart to make David king.
Dukan waɗannan mayaƙa ne waɗanda suka ba da kansu da yardar rai su yi hidima. Suka zo Hebron da cikakken niyya don su naɗa Dawuda sarki a bisa dukan Isra’ila. Duka sauran Isra’ilawa su ma suka goyi baya a naɗa Dawuda sarki.
39 So they were there, with David, three days, eating and drinking, —for their brethren had made preparation for them.
Mutanen suka yi kwana uku a can tare da Dawuda, suna ci suna sha, gama iyalansu sun yi musu tanadi.
40 Moreover also, they who were near of kin unto them, as far as Issachar and Zebulun and Naphtali, were bringing bread, on asses and on camels and on mules and on oxen, meal-food, cakes of figs and cakes of raisins, and wine, and oil, and oxen, and sheep—in abundance, —for there was joy Israel.
Haka ma, maƙwabtansu daga nesa har Issakar, Zebulun da Naftali suka zo suka kawo abinci a kan jakuna, raƙuma, alfadarai da shanu. Akwai tanadin mai yawa na gari, kauɗar ɓaure, nonnan busassun’ya’yan inabi, ruwan inabi, mai, shanu da tumaki. Duk an yi haka don a nuna farin ciki ƙwarai a cikin dukan ƙasar Isra’ila.

< 1 Chronicles 12 >