< Psalms 42 >

1 For the Chief Musician; Maschil of the sons of Korah. As the hart panteth after the water brooks, so panteth my soul after thee, O God.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Maskil ne na’Ya’yan Kora maza. Kamar yadda barewa take marmarin ruwan rafuffuka, haka raina yake marmarinka, ya Allah.
2 My soul thirsteth for God, for the living God: when shall I come and appear before God?
Raina yana ƙishin Allah, Allah mai rai. Yaushe zan tafi in sadu da Allah ne?
3 My tears have been my meat day and night, while they continually say unto me, Where is thy God?
Hawayena ne sun zama abincina dare da rana, yayinda mutane suke ce da ni dukan yini, “Ina Allahnka ɗin?”
4 These things I remember, and pour out my soul within me, how I went with the throng, and led them to the house of God, with the voice of joy and praise, a multitude keeping holyday.
Waɗannan abubuwa ne nakan tuna sa’ad da nake faɗin abin da yake a raina, yadda dā nakan tafi tare da taron jama’a, ina bishe su a jere zuwa gidan Allah, da sowa ta farin ciki da kuma godiya a cikin taron biki.
5 Why art thou cast down, O my soul? and [why] art thou disquieted within me? hope thou in God: for I shall yet praise him [for] the health of his countenance.
Me ya sa kake baƙin ciki, ya raina? Me ya sa ka damu a cikina? Ka dogara ga Allah, gama zai sāke yabe shi, Mai Cetona da kuma Allahna.
6 O my God, my soul is cast down within me: therefore do I remember thee from the land of Jordan, and the Hermons, from the hill Mizar.
Raina yana baƙin ciki a cikina; saboda haka zan tuna da kai daga ƙasar Urdun, a ƙwanƙolin Hermon, daga Dutsen Mizar.
7 Deep calleth unto deep at the noise of thy waterspouts: all thy waves and thy billows are gone over me.
Zurfi kan kira zurfi cikin rurin matsirgar ruwanka; dukan raƙuma da igiyoyi sun sha kaina.
8 [Yet] the LORD will command his lovingkindness in the day-time, and in the night his song shall be with me, [even] a prayer unto the God of my life.
Da rana Ubangiji yakan nuna ƙaunarsa, da dare waƙarsa tana tare da ni, addu’a ga Allah na raina.
9 I will say unto God my rock, Why hast thou forgotten me? why go I mourning because of the oppression of the enemy?
Na ce wa Allah Dutsena, “Me ya sa ka manta da ni? Me zai sa in yi ta yawo ina makoki, a danne a hannun abokin gāba?”
10 As with a sword in my bones, mine adversaries reproach me; while they continually say unto me, Where is thy God?
Ƙasusuwana suna jin jiki da wahala yayinda maƙiyana suna mini ba’a, suna ce mini dukan yini, “Ina Allahnka ɗin?”
11 Why art thou cast down, O my soul? and why art thou disquieted within me? hope thou in God: for I shall yet praise him, [who is] the health of my countenance, and my God.
Me ya sa kake baƙin ciki, ya raina? Me ya sa ka damu a cikina? Ka dogara ga Allah, gama zai sāke yabe shi, Mai Cetona da kuma Allahna.

< Psalms 42 >