< Psalms 37 >
1 [A Psalm] of David. Fret not thyself because of evil-doers, neither be thou envious against them that work unrighteousness.
Ta Dawuda. Kada ka tsorata saboda mugayen mutane ko ka yi kishin waɗanda suka aikata mugunta;
2 For they shall soon be cut down like the grass, and wither as the green herb.
gama kamar ciyawa za su bushe, kamar ɗanyun ganyaye za su mutu.
3 Trust in the LORD, and do good; dwell in the land, and follow after faithfulness.
Ka dogara ga Ubangiji ka kuma aikata alheri; yi zama cikin ƙasar ka kuma more makiyaya mai lafiya.
4 Delight thyself also in the LORD; and he shall give thee the desires of thine heart.
Ka ji daɗinka a cikin Ubangiji zai kuwa biya bukatun zuciyarka.
5 Commit thy way unto the LORD; trust also in him, and he shall bring it to pass.
Ka sa kanka a hanyar Ubangiji; ka kuma dogara gare shi zai kuwa yi wannan.
6 Add he shall make thy righteousness to go forth as the light, and thy judgment as the noonday.
Zai sa adalcinka yă haskaka kamar hasken safiya, gaskiyarka kuma kamar rana a tsaka.
7 Rest in the LORD, and wait patiently for him: fret not thyself because of him who prospereth in his way, because of the man who bringeth wicked devices to pass.
Ka natsu a gaban Ubangiji ka kuma jira da haƙuri gare shi; kada ka tsorata sa’ad da mutane ke nasara a hanyoyinsu, sa’ad da suke aikata mugayen shirye-shiryensu.
8 Cease from anger, and forsake wrath: fret not thyself, [it tendeth] only to evil-doing.
Kada ka yi fushi kada kuma ka yi hasala; kada ka tsorata, wannan yakan kai ga mugunta ne kawai.
9 For evil-doers shall be cut off: but those that wait upon the LORD, they shall inherit the land.
Gama za a datse mugayen mutane, amma waɗanda suke sa zuciya ga Ubangiji za su gāji ƙasar.
10 For yet a little while, and the wicked shall not be: yea, thou shalt diligently consider his place, and he shall not be.
A ɗan ƙanƙanen lokaci, mugaye za su shuɗe; ko ka neme su, ba za a same su ba.
11 But the meek shall inherit the land; and shall delight themselves in the abundance of peace.
Amma masu tawali’u za su gāji ƙasar su kuma zauna da cikakkiyar salama.
12 The wicked plotteth against the just, and gnasheth upon him with his teeth.
Mugaye sukan shirya wa adalai maƙarƙashiya su ciji baki a kansu;
13 The Lord shall laugh at him: for he seeth that his day is coming.
amma Ubangiji yakan yi dariyar mugaye, gama ya sani ranarsu tana zuwa.
14 The wicked have drawn out the sword, and have bent their bow; to cast down the poor and needy, to slay such as be upright in the way:
Mugaye sukan zare takobi su ja baka don su kashe matalauta da masu bukata, don su kashe waɗanda hanyoyinsu daidai suke.
15 Their sword shall enter into their own heart, and their bows shall be broken.
Amma takubansu za su soki zukatansu, kuma bakkunansu za su kakkarye.
16 Better is a little that the righteous hath than the abundance of many wicked.
Ƙanƙanen abin da mai adalci yake da shi ya fi arzikin mugaye yawa;
17 For the arms of the wicked shall be broken: but the LORD upholdeth the righteous.
gama za a kakkarya ikon mugaye, amma Ubangiji zai riƙe mai adalci.
18 The LORD knoweth the days of the perfect: and their inheritance shall be for ever.
Kwanakin marasa zarge suna sane ga Ubangiji, kuma gādonsu zai dawwama har abada.
19 They shall not be ashamed in the time of evil: and in the days of famine they shall be satisfied.
A lokutan masifu ba za su yanƙwane ba; a kwanakin yunwa za su sami a yalwace.
20 But the wicked shall perish, and the enemies of the LORD shall be as the excellency of the pastures: they shall consume; in smoke shall they consume away.
Amma mugaye za su hallaka, Abokan gāban Ubangiji za su zama kamar kyan gonaki, za su ɓace, za su ɓace kamar hayaƙi.
21 The wicked borroweth, and payeth not again: but the righteous dealeth graciously, and giveth.
Mugaye kan yi rance ba sa kuma biya, amma masu adalci suna bayar hannu sake;
22 For such as be blessed of him shall inherit the land; and they that be cursed of him shall be cut off.
waɗanda Ubangiji ya sa wa albarka za su gāji ƙasar, amma waɗanda ya la’anta, za a kore su.
23 A man’s goings are established of the LORD; and he delighteth in his way.
In Ubangiji ya ji daɗin hanyar da mutum yake bi, zai sa sawu su kahu;
24 Though he fall, he shall not be utterly cast down: for the LORD upholdeth him with his hand.
ko ya yi tuntuɓe, ba zai fāɗi ba, gama Ubangiji yakan riƙe shi da hannunsa.
25 I have been young, and now am old; yet have I not seen the righteous forsaken, nor his seed begging [their] bread.
Dā ni yaro ne amma yanzu na tsufa, duk da haka ban taɓa ganin an yashe masu adalci ba ko a ce’ya’yansu suna roƙon burodi.
26 All the day long he dealeth graciously, and lendeth; and his seed is blessed.
Kullum suna bayar hannu sake suna kuma ba da bashi ba da wahala ba, za a yi wa’ya’yansu albarka.
27 Depart from evil, and do good; dwell for evermore.
Ku juyo daga mugunta ku yi alheri; sa’an nan za ku zauna a ƙasar har abada.
28 For the LORD loveth judgment, and forsaketh not his saints; they are preserved for ever: but the seed of the wicked shall be cut off.
Gama Ubangiji yana ƙaunar masu aikata daidai kuma ba zai yashe amintattunsa ba. Za a hallaka masu aikata mugunta gaba ɗaya,’ya’yan mugaye za su hallaka.
29 The righteous shall inherit the land, and dwell therein for ever.
Masu adalci za su gāji ƙasar su kuma zauna a cikinta har abada.
30 The mouth of the righteous talketh of wisdom, and his tongue speaketh judgment.
Bakin mutum mai adalci yakan yi magana da hikima, harshensa kuwa yakan yi maganar abin da yake daidai.
31 The law of his God is in his heart; none of his steps shall slide.
Dokar Allahnsa tana a cikin zuciyarsa; ƙafafunsa ba sa santsi.
32 The wicked watcheth the righteous, and seeketh to slay him.
Mugaye suna fako suna jira masu adalci, suna ƙoƙari neman ransu;
33 The LORD will not leave him in his hand, nor condemn him when he is judged.
amma Ubangiji ba zai bar su a ikonsu ba ko ya bari a hukunta su sa’ad da aka kawo su shari’a ba.
34 Wait on the LORD, and keep his way, and he shall exalt thee to inherit the land: when the wicked are cut off, thou shalt see it.
Ku sa zuciya ga Ubangiji ku kuma kiyaye hanyarsa. Zai ɗaukaka ku ku ci gādon ƙasar, sa’ad da aka kawar da mugaye, za ka gani.
35 I have seen the wicked in great power, and spreading himself like a green tree in its native soil.
Na ga wani mugu, azzalumi, yana yaɗuwa kamar ɗanyen itace a asalin ƙasarsa,
36 But one passed by, and, lo, he was not: yea, I sought him, but he could not be found.
amma yakan mutu nan da nan kuma ba ya ƙara kasancewa; ko an neme shi, ba za a same shi ba.
37 Mark the perfect man, and behold the upright: for the latter end of [that] man is peace.
Ka dubi marasa zargi, ka lura da adali; akwai sa zuciya domin mutum mai salama.
38 As for transgressors, they shall be destroyed together: the latter end of the wicked shall be cut off.
Amma za a hallaka dukan masu zunubi; za a yanke sa zuciya ta mugaye.
39 But the salvation of the righteous is of the LORD: he is their strong hold in the time of trouble.
Ceton adalai kan zo daga Ubangiji; shi ne mafaka a lokacin wahala.
40 And the LORD helpeth them, and rescueth them: he rescueth them from the wicked, and saveth them, because they have taken refuge in him.
Ubangiji yakan taimake su yă kuma cece su; yakan kuɓutar da su daga mugaye yă kuma cece su, domin sukan nemi mafaka daga gare shi.