< Psalms 33 >

1 Rejoice in the LORD, O ye righteous: praise is comely for the upright.
Ku rera da farin ciki ga Ubangiji ku adalai; daidai ne masu gaskiya su yabe shi.
2 Give thanks unto the LORD with harp: sing praises unto him with the psaltery of ten strings.
Ku yabi Ubangiji da garaya; ku yi kiɗi gare shi da molo mai tsirkiya goma.
3 Sing unto him a new song; play skilfully with a loud noise.
Ku rera masa sabuwar waƙa; ku yi kiɗi da gwaninta, ku kuma yi sowa don farin ciki.
4 For the word of the LORD is right; and all his work is [done] in faithfulness.
Gama maganar Ubangiji daidai ne da kuma gaskiya; yana da aminci cikin kome da yake yi.
5 He loveth righteousness and judgment: the earth is full of the lovingkindness of the LORD.
Ubangiji yana ƙaunar adalci duniya ta cika da ƙaunarsa marar ƙarewa.
6 By the word of the LORD were the heavens made; and all the host of them by the breath of his mouth.
Ta wurin maganar Ubangiji aka yi sammai, rundunar taurarinsu kuwa da numfashin bakinsa.
7 He gathereth the waters of the sea together as an heap: he layeth up the deeps in storehouses.
Ya tattara ruwan teku cikin tuluna; ya sa zurfafa cikin gidajen ajiya.
8 Let all the earth fear the LORD: let all the inhabitants of the world stand in awe of him.
Bari dukan duniya ta ji tsoron Ubangiji; bari dukan mutanen duniya su girmama shi.
9 For he spake, and it was done; he commanded, and it stood fast.
Gama ya yi magana, abu ya kuwa kasance; ya umarta, ya kuwa tsaya daram.
10 The LORD bringeth the counsel of the nations to nought: he maketh the thoughts of the peoples to be of none effect.
Ubangiji yakan soke shirye-shiryen al’ummai; yakan wofintar da manufofin mutane.
11 The counsel of the LORD standeth fast for ever, the thoughts of his heart to all generations.
Amma shirye-shiryen Ubangiji kan tsaya daram har abada, manufofin zuciyarsa kuwa har dukan zamanai.
12 Blessed is the nation whose God is the LORD; the people whom he hath chosen for his own inheritance.
Mai farin ciki ce al’ummar da Allah ne Ubangijinta, mutanen da ya zaɓa don gādonsa.
13 The LORD looketh from heaven; he beholdeth all the sons of men;
Daga sama Ubangiji ya duba ya kuwa ga dukan’yan adam;
14 From the place of his habitation he looketh forth upon all the inhabitants of the earth;
daga mazauninsa yana lura da dukan waɗanda suke zama a duniya,
15 He that fashioneth the hearts of them all, that considereth all their works.
shi da ya yi zukatan duka, wanda yake kula da kome da suke yi.
16 There is no king saved by the multitude of an host: a mighty man is not delivered by great strength.
Babu sarkin da ake ceto ta wurin yawan mayaƙansa; ba jarumin da kan kuɓuta ta wurin yawan ƙarfinsa.
17 An horse is a vain thing for safety: neither shall he deliver any by his great power.
Dogara a kan doki don ceto banza ne; duk da yawan ƙarfinsa ba ya ceto.
18 Behold, the eye of the LORD is upon them that fear him, upon them that hope in his mercy;
Amma idanun Ubangiji suna a kan wanda yake tsoronsa, a kan waɗanda suke sa zuciya cikin ƙaunarsa marar ƙarewa,
19 To deliver their soul from death, and to keep them alive in famine.
don yă cece su daga mutuwa ya bar su da rai a lokacin yunwa.
20 Our soul hath waited for the LORD: he is our help and our shield.
Muna jiran Ubangiji da bege; shi ne taimakonmu da garkuwarmu.
21 For our heart shall rejoice in him, because we have trusted in his holy name.
A cikinsa zukatanmu na farin ciki, gama mun dogara cikin sunansa mai tsarki.
22 Let thy mercy, O LORD, be upon us, according as we have hoped in thee.
Bari ƙaunarka marar ƙarewa ta zauna a kanmu, ya Ubangiji, ko ma da muke sa begenmu a gare ka.

< Psalms 33 >