< Matthew 26 >
1 And it came to pass, when Jesus had finished all these words, he said unto his disciples,
Yayin da Yesu ya gama fadi masu wadannan maganganu, sai ya cewa almajiransa,
2 Ye know that after two days the passover cometh, and the Son of man is delivered up to be crucified.
“Kun sani sauran kwana biyu idin ketarewa ya zo, kuma za'a bada Dan mutum domin a gicciye shi.
3 Then were gathered together the chief priests, and the elders of the people, unto the court of the high priest, who was called Caiaphas;
Sa'annan manyan firistoci da dattawan jama'a suka taru a fadar babban firist, mai suna Kayafa.
4 and they took counsel together that they might take Jesus by subtilty, and kill him.
Suka shirya yadda zasu kama Yesu a boye su kuma kashe shi.
5 But they said, Not during the feast, lest a tumult arise among the people.
Amma suna cewa, “Ba a lokacin idin ba, domin kada tarzoma ta tashi daga cikin mutane.”
6 Now when Jesus was in Bethany, in the house of Simon the leper,
Sa'adda Yesu yake Baita'anya a gidan Saminu Kuturu,
7 there came unto him a woman having an alabaster cruse of exceeding precious ointment, and she poured it upon his head, as he sat at meat.
daidai lokacin da ya zauna a gefen teburin cin abinci, sai wata mata ta shigo da kwalbar mai, mai tsada, ta zuba wa Yesu a kansa.
8 But when the disciples saw it, they had indignation, saying, To what purpose is this waste?
Amma da almajiransa suka ga haka, sai suka ji haushi suka ce, “Ina dalilin yin irin wannan asara?
9 For this [ointment] might have been sold for much, and given to the poor.
Ai da an sayar da wannan mai da kudi mai yawa a rabawa talakawa.”
10 But Jesus perceiving it said unto them, Why trouble ye the woman? for she hath wrought a good work upon me.
Amma da yake Yesu ya san tunaninsu, sai yace masu, “Don me kuke damun matar nan? Ta yi abu mai kyau domina.
11 For ye have the poor always with you; but me ye have not always.
Kuna da talakawa tare da ku koyaushe, amma ni ba zan kasance da ku ba koyaushe.
12 For in that she poured this ointment upon my body, she did it to prepare me for burial.
Don a sa'adda ta zuba man nan a jikina, ta yi haka ne don jana'iza ta.
13 Verily I say unto you, Wheresoever this gospel shall be preached in the whole world, that also which this woman hath done shall be spoken of for a memorial of her.
Hakika Ina gaya maku, duk inda za ayi wannan bishara a dukan duniya, abin da matar nan tayi za'a rika ambatar da shi don tunawa da ita.”
14 Then one of the twelve, who was called Judas Iscariot, went unto the chief priests,
Sai daya daga cikin sha biyun, mai suna Yahuza Iskariyoti, ya tafi wurin manyan firistocin,
15 and said, What are ye willing to give me, and I will deliver him unto you? And they weighed unto him thirty pieces of silver.
yace, ''Me kuke da niyyar bani idan na mika maku shi?” Suka auna masa azurfa talatin.
16 And from that time he sought opportunity to deliver him [unto them].
Daga wannan lokacin yayi ta neman zarafi da zai bada shi a wurinsu.
17 Now on the first [day] of unleavened bread the disciples came to Jesus, saying, Where wilt thou that we make ready for thee to eat the passover?
To a rana ta fari na idin ketarewa almajiran suka zo wurin Yesu suka ce, ''Ina kake so mu shirya maka da zaka ci abincin idin ketarewa?”
18 And he said, Go into the city to such a man, and say unto him, The Master saith, My time is at hand; I keep the passover at thy house with my disciples.
Yace, “Ku shiga cikin birnin zaku sami wani mutum sai kuce masa, 'Mallam yace, “lokaci na ya kusa. Zan ci idin ketarewa a gidanka, da almajiraina.”'''
19 And the disciples did as Jesus appointed them; and they made ready the passover.
Almajiran suka yi kamar yadda Yesu ya umarce su, suka shirya abincin idin ketarewar.
20 Now when even was come, he was sitting at meat with the twelve disciples;
Da yamma ta yi, sai ya zauna domin ya ci tare da almajiransa goma sha biyu.
21 and as they were eating, he said, Verily I say unto you, that one of you shall betray me.
Sa'adda suke ci, yace, “Hakika ina gaya maku, daya daga cikin ku zai bada ni.”
22 And they were exceeding sorrowful, and began to say unto him every one, Is it I, Lord?
Suka yi bakin ciki, suka fara tambayarsa daya bayan daya, ''Na tabbata ba ni bane ko, Ubangiji?”
23 And he answered and said, He that dipped his hand with me in the dish, the same shall betray me.
Sai ya amsa, “Wanda ke sa hannu tare da ni cikin kwano daya shi ne zai bada ni.
24 The Son of man goeth, even as it is written of him: but woe unto that man through whom the Son of man is betrayed! good were it for that man if he had not been born.
Dan mutum zai tafi, kamar yadda aka rubuta akan sa. Amma kaiton mutumin da ta wurin sa za'a bada Dan mutum! Gwamma da ba'a haifi mutumin nan ba.”
25 And Judas, which betrayed him, answered and said, Is it I, Rabbi? He saith unto him, Thou hast said.
Yahuza da zai bada shi yace, “Mallam ko ni ne?” Yace masa, “Ka fada da kanka.”
26 And as they were eating, Jesus took bread, and blessed, and brake it; and he gave to the disciples, and said, Take, eat; this is my body.
Yayin da suke ci, sai Yesu ya dauki gurasa, ya sa albarka, ya karya. Ya ba almajiran yace, “Ku karba, ku ci, wannan jiki nane.”
27 And he took a cup, and gave thanks, and gave to them, saying, Drink ye all of it;
Sai ya dauki kokon yayi godiya, Ya ba su yace, “Ku sha, dukanku.
28 for this is my blood of the covenant, which is shed for many unto remission of sins.
“Gama wannan jinina ne na alkawari wanda aka zubar domin gafarar zunuban mutane da yawa.
29 But I say unto you, I will not drink henceforth of this fruit of the vine, until that day when I drink it new with you in my Father’s kingdom.
Amma ina gaya maku, ba zan kara shan ruwan inabin nan ba, sai ranar da zan sha shi sabo tare da ku a cikin mulkin Ubana.”
30 And when they had sung a hymn, they went out unto the mount of Olives.
Da suka raira waka, sai suka ka tafi dutsen zaitun.
31 Then saith Jesus unto them, All ye shall be offended in me this night: for it is written, I will smite the shepherd, and the sheep of the flock shall be scattered abroad.
Sai Yesu yace masu, “Dukan ku zaku yi tuntube a wannan dare sabili da ni, gama a rubuce yake, ''Zan bugi makiyayin, garken tumakin kuma za su watse.'
32 But after I am raised up, I will go before you into Galilee.
Amma bayan an tashe ni, zan riga ku zuwa Galili.”
33 But Peter answered and said unto him, If all shall be offended in thee, I will never be offended.
Amma Bitrus yace masa, “Ko dama duka zasu fadi sabili da kai, ni kam bazan fadi ba.”
34 Jesus said unto him, Verily I say unto thee, that this night, before the cock crow, thou shalt deny me thrice.
Yesu yace masa, ''Hakika ina gaya maka, a wannan daren kafin carar zakara, za ka yi musun sani na sau uku.”
35 Peter saith unto him, Even if I must die with thee, [yet] will I not deny thee. Likewise also said all the disciples.
Bitrus yace masa, koda zan mutu tare da kai, bazan yi musunka ba.” Sai sauran almajiran suma suka fadi haka.
36 Then cometh Jesus with them unto a place called Gethsemane, and saith unto his disciples, Sit ye here, while I go yonder and pray.
Sa'anna Yesu ya tafi tare da su, wurin da ake kira Getsaimani sai yace wa almajiransa, ''Ku zauna a nan ni kuma zan je gaba in yi addu'a.”
37 And he took with him Peter and the two sons of Zebedee, and began to be sorrowful and sore troubled.
Ya dauki Bitrus da kuma 'ya'ya biyu na Zabadi tare da shi, sai ya fara damuwa da juyayi.
38 Then saith he unto them, My soul is exceeding sorrowful, even unto death: abide ye here, and watch with me.
Sai yace masu, “Raina na cikin damuwa sosai har ga mutuwa. Ku kasance anan kuna tsaro tare da ni.”
39 And he went forward a little, and fell on his face, and prayed, saying, O my Father, if it be possible, let this cup pass away from me: nevertheless, not as I will, but as thou wilt.
Ya dan taka zuwa gaba kadan, sai ya fadi a fuskarsa, yayi addu'a. Yace, “Ya Ubana, in zai yiwu, bari kokon nan ya wuce ni. Duk da haka, ba nufina za'a bi ba, amma naka nufin.”
40 And he cometh unto the disciples, and findeth them sleeping, and saith unto Peter, What, could ye not watch with me one hour?
Ya koma wurin almajiran ya same su suna barci, sai ya cewa Bitrus, “Kai, ba zaku yi tsaro tare da ni ba koda sa'a daya?
41 Watch and pray, that ye enter not into temptation: the spirit indeed is willing, but the flesh is weak.
Ku yi tsaro kuma, kuyi addu'a domin kada ku fada cikin jaraba. Ruhu dai ya yarda amma, jiki ba karfi.”
42 Again a second time he went away, and prayed, saying, O my Father, if this cannot pass away, except I drink it, thy will be done.
Sai ya koma karo na biyu yayi addu'a, Yace, “Ya Ubana, in wannan kokon ba zai wuce ba sai na sha shi, bari nufinka ya kasance.”
43 And he came again and found them sleeping, for their eyes were heavy.
Ya sake dawowa, ya same su suna barci, domin idanunsu sun yi nauyi.
44 And he left them again, and went away, and prayed a third time, saying again the same words.
Sai ya sake barinsu ya tafi. Ya koma karo na uku yana addu'a yana fadin kalmomi iri daya.
45 Then cometh he to the disciples, and saith unto them, Sleep on now, and take your rest: behold, the hour is at hand, and the Son of man is betrayed into the hands of sinners.
Sai Yesu ya koma wurin almajiran yace masu, “Har yanzu barci kuke kuna hutawa? Duba, lokaci ya kusato, kuma an bada Dan mutum ga hannun masu zunubi.
46 Arise, let us be going: behold, he is at hand that betrayeth me.
Ku tashi mu tafi. Duba, wanda zai badani ya kusato.”
47 And while he yet spake, lo, Judas, one of the twelve, came, and with him a great multitude with swords and staves, from the chief priests and elders of the people.
Sa'adda yana cikin magana Yahuza, daya daga cikin sha biyun, ya zo. Babban taro ya zo tare da shi daga wurin manyan firistoci da dattawan jama'a. Suna rike da takubba da kulake.
48 Now he that betrayed him gave them a sign, saying, Whomsoever I shall kiss, that is he: take him.
To mutumin da zai bada Yesu ya rigaya ya basu alama, cewa, ''Duk wanda na sumbata, shine. Ku kama shi.''
49 And straightway he came to Jesus, and said, Hail, Rabbi; and kissed him.
Nan da nan ya kaiga Yesu ya ce, “Gaisuwa, Mallam!” sai ya sumbace shi.
50 And Jesus said unto him, Friend, [do] that for which thou art come. Then they came and laid hands on Jesus, and took him.
Yesu kuwa yace masa, “Aboki, kayi abin da ya kawo ka.” Sai suka iso suka sa hannuwansu kan Yesu suka kama shi.
51 And behold, one of them that were with Jesus stretched out his hand, and drew his sword, and smote the servant of the high priest, and struck off his ear.
Nan take, daya daga cikin wadanda suke tare da Yesu ya mika hannunsa, ya zare takobinsa, ya sare wa bawan babban firist din kunne.
52 Then saith Jesus unto him, Put up again thy sword into its place: for all they that take the sword shall perish with the sword.
Sai Yesu yace, masa, “Ka maida takobinka cikin kubensa, domin duk wadanda suka dauki takobi su ma ta wurin takobi za su hallaka.
53 Or thinkest thou that I cannot beseech my Father, and he shall even now send me more than twelve legions of angels?
Ko kana tunanin ba zan iya kiran Ubana ba, ya kuma aiko da rundunar Mala'iku fiye da goma sha biyu?
54 How then should the scriptures be fulfilled, that thus it must be?
Amma to tayaya za'a cika nassi, cewa dole wannan ya faru?''
55 In that hour said Jesus to the multitudes, Are ye come out as against a robber with swords and staves to seize me? I sat daily in the temple teaching, and ye took me not.
A wannan lokacin Yesu yace wa taron, “Kun zo da takubba da kulake ku kama ni kamar dan fashi? Ina zaune kowace rana a haikali ina koyarwa, amma baku kama ni ba.
56 But all this is come to pass, that the scriptures of the prophets might be fulfilled. Then all the disciples left him, and fled.
Amma duk wannan ya faru ne don a cika abinda annabawa suka rubuta.” Bayan haka sai dukkan almajiran suka bar shi suka gudu.
57 And they that had taken Jesus led him away to [the house of] Caiaphas the high priest, where the scribes and the elders were gathered together.
Wadanda suka kama Yesu, suka kai shi wurin Kayafa babban firist, inda marubuta da duttawan jama'a suka taru.
58 But Peter followed him afar off, unto the court of the high priest, and entered in, and sat with the officers, to see the end.
Amma Bitrus ya bi shi daga nesa, har zuwa farfajiyar babban firist din. Ya shiga ya zauna da masu tsaro domin ya ga abinda zai faru.
59 Now the chief priests and the whole council sought false witness against Jesus, that they might put him to death;
A wannan lokaci manyan firistoci da duk 'yan majalisar suka fara neman shaidar karya akan Yesu, domin su samu su kashe shi.
60 and they found it not, though many false witnesses came. But afterward came two,
Amma ba su samu ko daya ba, ko dayake an samu shaidun karya dayawa da suka gabata. Amma daga baya sai wasu su biyu suka fito
61 and said, This man said, I am able to destroy the temple of God, and to build it in three days.
sukace ''Wannan mutum yace zan iya rushe haikalin Allah, in kuma gina shi cikin kwana uku.'''
62 And the high priest stood up, and said unto him, Answerest thou nothing? what is it which these witness against thee?
Babban Firist din ya tashi tsaye yace masa, “Ba zaka ce komai ba? Wace irin shaida ce ake yi akanka?”
63 But Jesus held his peace. And the high priest said unto him, I adjure thee by the living God, that thou tell us whether thou be the Christ, the Son of God.
Amma Yesu yayi shiru. Babban Firist ya ce, “Na umarce ka da sunan Allah mai rai, ka gaya mana ko kai Almasihu ne, Dan Allah.''
64 Jesus saith unto him, Thou hast said: nevertheless I say unto you, Henceforth ye shall see the Son of man sitting at the right hand of power, and coming on the clouds of heaven.
Yesu ya amsa masa, “Ka fada da bakin ka. Amma ina gaya maka, daga yanzu zaka ga Dan mutun na zaune a hannun dama na iko, ya na zuwa akan gizagizai na sama.”
65 Then the high priest rent his garments, saying, He hath spoken blasphemy: what further need have we of witnesses? behold, now ye have heard the blasphemy:
Sai babban firist din ya yayyaga rigarsa, yana cewa, “Yayi sabo! don me ku ke neman wata shaida kuma? Duba, yanzu kun ji sabon.
66 what think ye? They answered and said, He is worthy of death.
Menene tunaninku?” Suka amsa sukace, “Ya cancanci mutuwa.”
67 Then did they spit in his face and buffet him: and some smote him with the palms of their hands,
Sai suka tofa masa yawu a fuska, suka kuma yi masa duka, suka kuma mammare shi da tafin hannuwansu,
68 saying, Prophesy unto us, thou Christ: who is he that struck thee?
sukace, ''Ka yi mana anabci, kai Almasihu. Wanene wanda ya dokeka.
69 Now Peter was sitting without in the court: and a maid came unto him, saying, Thou also wast with Jesus the Galilaean.
To Bitrus kuwa na zaune a farfajiyar, sai wata yarinya baiwa ta zo wurinsa tana cewa, “Kaima kana tare da Yesu na Galili.”
70 But he denied before them all, saying, I know not what thou sayest.
Amma ya yi musun haka a gaban su duka, yace, “Ban ma san abinda kike magana akai ba.”
71 And when he was gone out into the porch, another [maid] saw him, and saith unto them that were there, This man also was with Jesus the Nazarene.
Da ya fita zuwa bakin kofa, nan ma wata yarinyar baiwa ta gan shi tace wa wadanda suke wurin, “Wannan mutumin ma yana tare da Yesu Banazare.”
72 And again he denied with an oath, I know not the man.
Sai yayi musun haka kuma, har da rantsuwa, yace, “Ban san mutumin nan ba.”
73 And after a little while they that stood by came and said to Peter, Of a truth thou also art [one] of them; for thy speech bewrayeth thee.
Bayan dan lokaci kadan wadanda suke a tsaye suka zo wurin Bitrus suka ce masa, “Hakika kai daya daga cikin su ne, gama harshen ka ya tonaka.”
74 Then began he to curse and to swear, I know not the man. And straightway the cock crew.
Sai ya fara rantsuwa irin ta la'ana, yana cewa, ''Ban san wannan mutumin ba,” nan da nan zakara yayi cara.
75 And Peter remembered the word which Jesus had said, Before the cock crow, thou shalt deny me thrice. And he went out, and wept bitterly.
Bitrus ya tuna da maganar da Yesu ya fada, “Kafin carar zakara zaka yi musun sani na sau uku.” Sai ya fita waje yayi kuka mai zafi.''