< Leviticus 2 >
1 And when any one offereth an oblation of a meal offering unto the LORD, his oblation shall be of fine flour; and he shall pour oil upon it, and put frankincense thereon:
“‘Sa’ad da wani ya kawo hadaya ta gari ga Ubangiji, hadayarsa za tă zama gari mai laushi ne. Zai zuba mai a kai, yă sa turare a kansa
2 and he shall bring it to Aaron’s sons the priests: and he shall take thereout his handful of the fine flour thereof, and of the oil thereof, with all the frankincense thereof; and the priest shall burn [it as] the memorial thereof upon the altar, an offering made by fire, of a sweet savour unto the LORD:
yă kai wa’ya’yan Haruna maza waɗanda suke firistoci. Firist zai ɗiba gari mai laushin a tafin hannu da kuma man, tare da dukan turaren, yă ƙone wannan a sashen tunawa a kan bagade, hadaya ce da aka yi da wuta, mai daɗin ƙanshi ga Ubangiji.
3 and that which is left of the meal offering shall be Aaron’s and his sons’: it is a thing most holy of the offerings of the LORD made by fire.
Sauran hadaya ta garin zai zama na Haruna da’ya’yansa; sashe mafi tsarki ne na hadayar da aka yi ga Ubangiji ta wuta.
4 And when thou offerest an oblation of a meal offering baken in the oven, it shall be unleavened cakes of fine flour mingled with oil, or unleavened wafers anointed with oil.
“‘In kuka kawo toyayyen hadayar gari da aka yi daga matoya, zai ƙunshi gari mai laushi, toyayye ba tare da yisti ba, gauraye kuma da mai, ko kuwa ƙosai da aka yi ba tare da yisti ba, aka kuma kwaɓa da mai.
5 And if thy oblation be a meal offering of the baking pan, it shall be of fine flour unleavened, mingled with oil.
In an toya hadaya ta garinku a kasko, sai a yi shi da gari mai laushi haɗe da mai, ba kuwa da yisti ba.
6 Thou shalt part it in pieces, and pour oil thereon: it is a meal offering.
A gutsuttsura shi, a zuba mai a kansa, hadaya ce ta hatsi.
7 And if thy oblation be a meal offering of the frying pan, it shall be made of fine flour with oil.
In hadayarku ta hatsin da aka dafa ne a tukunya, sai a yi shi da gari mai laushi da kuma mai.
8 And thou shalt bring the meal offering that is made of these things unto the LORD: and it shall be presented unto the priest, and he shall bring it unto the altar.
A kawo hatsin da aka yi da waɗannan abubuwa ga Ubangiji; a ba wa firist wanda zai ɗauka yă kai bagade.
9 And the priest shall take up from the meal offering the memorial thereof, and shall burn it upon the altar: an offering made by fire, of a sweet savour unto the LORD.
Zai fid da sashen tunawa daga hadaya ta gari, yă ƙone shi a kan bagade kamar hadayar da ka yi da wuta, mai daɗin ƙanshi ga Ubangiji.
10 And that which is left of the meal offering shall be Aaron’s and his sons’: it is a thing most holy of the offerings of the LORD made by fire.
Sauran hadaya ta garin za tă zama ta Haruna da’ya’yansa; sashe mafi tsarki ne na hadayun da aka yi ga Ubangiji ta wuta.
11 No meal offering, which ye shall offer unto the LORD, shall be made with leaven: for ye shall burn no leaven, nor any honey, as an offering made by fire unto the LORD.
“‘Kowace hadaya ta garin da kuka kawo ga Ubangiji, dole a yi shi ba tare da yisti ba, gama ba za ku ƙone wani yisti, ko zuma a cikin hadayar da aka yi ga Ubangiji ta wuta ba.
12 As an oblation of first[fruits] ye shall offer them unto the LORD: but they shall not come up for a sweet savour on the altar.
Za ku iya kawo su ga Ubangiji kamar hadaya ta’ya’yan fari, amma ba za a miƙa su a bagade kamar turare mai ƙanshi ba.
13 And every oblation of thy meal offering shalt thou season with salt; neither shalt thou suffer the salt of the covenant of thy God to be lacking from thy meal offering: with all thine oblations thou shalt offer salt.
A sa gishiri a dukan hadayunku na hatsi. Kada a rasa sa gishirin alkawari na Allahnku a hadayunku na hatsi, a sa gishiri a dukan hadayunku.
14 And if thou offer a meal offering of firstfruits unto the LORD, thou shalt offer for the meal offering of thy firstfruits corn in the ear parched with fire, bruised corn of the fresh ear.
“‘In kuka kawo hadaya ta gari na’ya’yan fari ga Ubangiji, sai ku miƙa ɓarzajjen kawunan sabon hatsin da aka gasa a wuta.
15 And thou shalt put oil upon it, and lay frankincense thereon: it is a meal offering.
A sa mai da turare a kansa, hadaya ce ta hatsi.
16 And the priest shall burn the memorial of it, part of the bruised corn thereof, and part of the oil thereof, with all the frankincense thereof: it is an offering made by fire unto the LORD.
Firist zai ƙone sashe na ɓarzajjen hatsin da kuma mai, tare da turare don tunawa, gama hadaya ce da aka ƙone da wuta ga Ubangiji.