< Job 8 >
1 Then answered Bildad the Shuhite, and said,
Sai Bildad mutumin Shuwa ya amsa,
2 How long wilt thou speak these things? and [how long] shall the words of thy mouth be [like] a mighty wind?
“Har yaushe za ka gama faɗa waɗannan abubuwa? Maganganunka ba su da amfani.
3 Doth God pervert judgment? or doth the Almighty pervert justice?
Allah ba mai shari’ar gaskiya ba ne? Ko Maɗaukaki yakan yi abin da ba daidai ba?
4 If thy children have sinned against him, and he have delivered them into the hand of their transgression:
Lokacin da’ya’yansa suka yi masa zunubi, yakan bar su su sha wahalar da zunubi yake kawowa.
5 If thou wouldest seek diligently unto God, and make thy supplication to the Almighty;
Amma in za ka dubi Allah ka roƙi Maɗaukaki,
6 If thou wert pure and upright; surely now he would awake for thee, and make the habitation of thy righteousness prosperous.
in kai mai tsarki ne, kuma mai adalci, ko yanzu ma zai taimake ka, yă mayar maka iyalinka da farin cikinka.
7 And though thy beginning was small, yet thy latter end should greatly increase.
Ko da yake za ka fara da kaɗan, duk da haka za ka gama da samu mai yawa.
8 For inquire, I pray thee, of the former age, and apply thyself to that which their fathers have searched out:
“Tambayi na gaba da kai ka ji abin da iyayenka suka koya
9 (For we are but of yesterday, and know nothing, because our days upon earth are a shadow: )
gama jiya kaɗai aka haife mu ba mu san kome ba, kuma kwanakinmu a duniya masu wucewa ne.
10 Shall not they teach thee, and tell thee, and utter words out of their heart?
Ba za su bishe ka su kuma gaya maka abin da za ka yi ba? Ba za su yi magana daga cikin hikimar da suke da ita ba?
11 Can the rush grow up without mire? can the flag grow without water?
Ko kyauro zai iya yi girma a wurin da ba ruwa? Ko za tă taɓa iya yin girma ba tare da ruwa ba?
12 Whilst it is yet in its greenness, [and] not cut down, it withereth before any [other] herb.
Yayinda take girma ba a yanka ta, takan mutu da sauri fiye da ciyawa.
13 So are the paths of all that forget God; and the hope of the godless man shall perish:
Abin da yake faruwa ke nan da duk wanda yake mantawa da Allah; waɗanda ba su da Allah, ba su da bege.
14 Whose confidence shall break in sunder, and whose trust is a spider’s web.
Abin da yake dogara a kai ba shi da ƙarfi; abin da yake dogara a kai yanar gizo ce.
15 He shall lean upon his house, but it shall not stand: he shall hold fast thereby, but it shall not endure.
Ya jingina ga yanar gizo, amma ba ta tare shi, sun kama ta, amma ba za tă taimake su tsayawa ba.
16 He is green before the sun, and his shoots go forth over his garden.
Yana kama da shukar da aka ba ta ruwa sosai lokacin da akwai rana sosai, tana yaɗuwa da kyau;
17 His roots are wrapped about the heap, he beholdeth the place of stones.
shukar tana bin yaɗuwa, jijiyoyinta suna nannaɗe duwatsu, suna neman wurin da za su kama sosai a cikin duwatsu.
18 If he be destroyed from his place, then it shall deny him, [saying], I have not seen thee.
Amma lokacin da aka tuge shukar daga wurin da take, wurin ba zai san da ita kuma ba, wurin zai ce, ‘Ban taɓa ganin ki ba.’
19 Behold, this is the joy of his way, and out of the earth shall others spring.
Ba shakka shukar ta mutu ke nan, kuma waɗansu za su tsiro a wurin.
20 Behold, God will not cast away a perfect man, neither will he uphold the evil-doers.
“Ba shakka, Allah ba ya ƙin marar laifi, ko kuma yă ƙarfafa masu aikata mugunta.
21 He will yet fill thy mouth with laughter, and thy lips with shouting.
Sai dai yă cika bakinka da dariya, yă sa ka yi sowa ta murna.
22 They that hate thee shall be clothed with shame; and the tent of the wicked shall be no more.
Maƙiyanka za su sha kunya, za a kawar da tentin mugaye.”