< Job 23 >

1 Then Job answered and said,
Sa’an nan Ayuba ya amsa,
2 Even today is my complaint rebellious: my stroke is heavier than my groaning.
“Ko a yau, ina kuka mai zafi; hannunsa yana da nauyi duk da nishin da nake yi.
3 Oh that I knew where I might find him, that I might come even to his seat!
Da a ce na san inda zan same shi; da a ce zan iya zuwa wurin da yake zama!
4 I would order my cause before him, and fill my mouth with arguments.
Zan kai damuwata wurinsa in yi gardama da shi.
5 I would know the words which he would answer me, and understand what he would say unto me.
Zan nemi in san abin da zai ce mini, in kuma auna abin da zai ce mini.
6 Would he contend with me in the greatness of his power? Nay; but he would give heed unto me.
Zai yi gardama da ni da ikonsa mai girma? Babu, ba zai zarge ni da laifi ba.
7 There the upright might reason with him; so should I be delivered for ever from my judge.
Mai adalci ne zai kawo ƙara a wurinsa, kuma zan samu kuɓuta daga wurin mai shari’an nan har abada.
8 Behold, I go forward, but he is not [there]; and backward, but I cannot perceive him:
“Amma in na je gabas, ba ya wurin; in na je yamma, ba zan same shi ba.
9 On the left hand, when he doth work, but I cannot behold him: he hideth himself on the right hand, that I cannot see him.
Sa’ad da yake aiki a arewa, ba ni ganinsa; sa’ad da ya juya zuwa kudu, ba na ganinsa.
10 But he knoweth the way that I take; when he hath tried me, I shall come forth as gold.
Amma ya san hanyar da nake bi; sa’ad da ya gwada ni zan fito kamar zinariya.
11 My foot hath held fast to his steps; his way have I kept, and turned not aside.
Ƙafafuna suna bin ƙafafunsa kurkusa; na bi hanyarsa ba tare da na juya ba.
12 I have not gone back from the commandment of his lips; I have treasured up the words of his mouth more than my necessary food.
Ban fasa bin dokokin da ya bayar ba; na riƙe maganarsa da muhimmanci fiye da abincin yau da gobe.
13 But he is in one [mind], and who can turn him? and what his soul desireth, even that he doeth.
“Amma ya tsaya shi kaɗai, kuma wa ya isa yă ja da shi? Yana yin abin da yake so.
14 For he performeth that which is appointed for me: and many such things are with him.
Yana yi mini abin da ya shirya yă yi mini, kuma yana da sauran irinsu a ajiye.
15 Therefore am I troubled at his presence; when I consider, I am afraid of him.
Shi ya sa na tsorata a gabansa; sa’ad da na yi tunanin wannan duka, nakan ji tsoronsa.
16 For God hath made my heart faint, and the Almighty hath troubled me:
Allah ya sa zuciyata ta yi sanyi; Maɗaukaki ya tsorata ni.
17 Because I was not cut off before the darkness, neither did he cover the thick darkness from my face.
Duk da haka duhun bai sa in yi shiru ba, duhun da ya rufe mini fuska.

< Job 23 >