< Job 11 >
1 Then answered Zophar the Naamathite, and said,
Sa’an nan Zofar mutumin Na’ama ya amsa,
2 Should not the multitude of words be answered? and should a man full of talk be justified?
“Duk surutun nan ba za a amsa maka ba? Ko mai surutun nan marar laifi ne?
3 Should thy boastings make men hold their peace? and when thou mockest, shall no man make thee ashamed?
Ko maganganun nan naka marasa amfani za su sa mutane su yi maka shiru? Ba wanda zai kwaɓe ka lokacin da kake faɗar maganar da ba daidai ba?
4 For thou sayest, My doctrine is pure, and I am clean in thine eyes.
Ka ce wa Allah, ‘Abin da na gaskata ba laifi ba ne kuma ni mai tsabta ne a gabanka.’
5 But Oh that God would speak, and open his lips against thee;
Da ma Allah zai yi magana, yă buɗe baki yă faɗi wani abin da ka yi da ba daidai ba
6 And that he would shew thee the secrets of wisdom, that is manifold in effectual working! Know therefore that God exacteth of thee less than thine iniquity deserveth.
yă kuma buɗe maka asirin hikima, gama hikima ta gaskiya tana da gefe biyu. Ka san wannan, Allah ya riga ya manta da waɗansu zunubanka.
7 Canst thou by searching find out God? canst thou find out the Almighty unto perfection?
“Ko za ka iya gane al’amuran Allah? Ko za ka iya gane girman asirin Maɗaukaki?
8 It is high as heaven; what canst thou do? deeper than Sheol; what canst thou know? (Sheol )
Sun fi nisan sama tudu, me za ka iya yi? Sun fi zurfin kabari zurfi, me za ka sani? (Sheol )
9 The measure thereof is longer than the earth, and broader than the sea.
Tsayinsu ya fi tsawon duniya da kuma fāɗin teku.
10 If he pass through, and shut up, and call unto judgment, then who can hinder him?
“In ya zo ya kulle ka a kurkuku ya ce kai mai laifi ne, wa zai hana shi?
11 For he knoweth vain men: he seeth iniquity also, even though he consider it not.
Ba shakka yana iya gane mutanen da suke marasa gaskiya; kuma in ya ga abin da yake mugu, ba ya kula ne?
12 But vain man is void of understanding, yea, man is born as a wild ass’s colt.
Amma daƙiƙin mutum ba ya taɓa zama mai hikima kamar dai a ce ba a taɓa haihuwar ɗan aholaki horarre.
13 If thou set thine heart aright, and stretch out thine hands toward him;
“Duk da haka in ka miƙa masa zuciyarka, ka kuma miƙa hannuwanka gare shi,
14 If iniquity be in thine hand, put it far away, and let not unrighteousness dwell in thy tents;
in ka kawar da zunubin da yake hannunka, ba ka bar zunubi ya kasance tare da kai ba
15 Surely then shalt thou lift up thy face without spot; yea, thou shalt be stedfast, and shalt not fear:
shi ne za ka iya ɗaga fuskarka ba tare da jin kunya ba; za ka tsaya da ƙarfi kuma ba za ka ji tsoro ba.
16 For thou shalt forget thy misery; thou shalt remember it as waters that are passed away:
Ba shakka za ka manta da wahalolinka, za ka tuna da su kamar yadda ruwa yake wucewa.
17 And [thy] life shall be clearer than the noonday; though there be darkness, it shall be as the morning.
Rayuwarka za tă fi hasken rana haske, duhu kuma zai zama kamar safiya.
18 And thou shalt be secure, because there is hope; yea, thou shalt search [about thee], and shalt take thy rest in safety.
Za ka zauna lafiya, domin akwai bege; za ka duba kewaye da kai ka huta cikin kwanciyar rai.
19 Also thou shalt lie down, and none shall make thee afraid; yea, many shall make suit unto thee.
Za ka kwanta, ba wanda zai sa ka ji tsoro, da yawa za su zo neman taimako a wurinka.
20 But the eyes of the wicked shall fail, and they shall have no way to flee, and their hope shall be the giving up of the ghost.
Amma idanun mugaye ba za su iya gani ba, kuma ba za su iya tserewa ba; begensu zai zama na mutuwa.”