< Isaiah 24 >
1 Behold, the LORD maketh the earth empty, and maketh it waste, and turneth it upside down, and scattereth abroad the inhabitants thereof.
Duba, Ubangiji zai wofinta duniya ya kuma yi kaca-kaca da ita; zai ɓata fuskarta ya watsar da mazaunanta,
2 And it shall be, as with the people, so with the priest; as with the servant, so with his master; as with the maid, so with her mistress; as with the buyer, so with the seller; as with the lender, so with the borrower; as with the taker of usury, so with the giver of usury to him.
zai zama abu ɗaya ga firist kamar yadda yake ga mutane, ga maigida kamar yadda yake ga bawa, ga uwargijiya kamar yadda yake ga baiwa, ga mai sayarwa kamar yadda yake ga mai saya, ga mai karɓan rance kamar yadda yake ga mai ba da rance, ga mai karɓan bashi kamar yadda yake ga mai ba da bashi.
3 The earth shall be utterly emptied, and utterly spoiled; for the LORD hath spoken this word.
Za a wofinta duniya ƙaƙaf a kuma washe ta sarai. Ubangiji ne ya faɗa haka.
4 The earth mourneth and fadeth away, the world languisheth and fadeth away, the lofty people of the earth do languish.
Duniya ta bushe ta kuma yanƙwane, duniya tana shan azaba ta kuma raunana, masu daraja na duniya suna shan azaba.
5 The earth also is polluted under the inhabitants thereof; because they have transgressed the laws, changed the ordinance, broken the everlasting covenant.
Duniya ta ƙazantu ta wurin mutanenta sun ƙi yin biyayya da dokoki, sun keta farillai suka kuma karya madawwamin alkawari.
6 Therefore hath the curse devoured the earth, and they that dwell therein are found guilty: therefore the inhabitants of the earth are burned, and few men left.
Saboda haka la’ana za tă auko wa duniya; dole mutanenta su ɗauki hakkin laifinsu. Saboda haka aka ƙone mazaunan duniya, kuma kaɗan ne kurum suka rage.
7 The new wine mourneth, the vine languisheth, all the merryhearted do sigh.
Sabon ruwan inabi ya bushe kuringar inabi kuma sun yanƙwane; dukan masu farin ciki suna nishi.
8 The mirth of tabrets ceaseth, the noise of them that rejoice endeth, the joy of the harp ceaseth.
Kaɗe-kaɗen garayu sun yi shiru, surutun masu murna ya daina, garayan farin ciki ya yi shiru.
9 They shall not drink wine with a song; strong drink shall be bitter to them that drink it.
Babu sauran shan ruwan inabi suna rera waƙa; barasa ya zama da ɗaci ga masu shanta.
10 The city of confusion is broken down: every house is shut up, that no man may come in.
Birnin da aka birkice ta zama kango; an kulle ƙofar shiga kowane gida.
11 There is a crying in the streets because of the wine; all joy is darkened, the mirth of the land is gone.
A tituna suna kukan neman ruwan inabi; dukan farin ciki ya dawo baƙin ciki, an hana dukan kaɗe-kaɗe a duniya.
12 In the city is left desolation, and the gate is smitten with destruction.
An bar birnin kango, aka yi kaca-kaca da ƙofofinta.
13 For thus shall it be in the midst of the earth among the peoples, as the shaking of an olive tree, as the grape gleanings when the vintage is done.
Haka zai zama a duniya da kuma a cikin al’ummai, kamar sa’ad da akan karkaɗe itacen zaitun, ko kuma kamar sa’ad da ake barin kala bayan an girbe inabi.
14 These shall lift up their voice, they shall shout; for the majesty of the LORD they cry aloud from the sea.
Sun daga muryoyinsu, sun yi sowa ta farin ciki; daga yamma sun furta darajar Ubangiji.
15 Wherefore glorify ye the LORD in the east, even the name of the LORD, the God of Israel, in the isles of the sea.
Saboda haka a gabas sun ɗaukaka Ubangiji, a ɗaukaka sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila, a cikin tsibiran teku.
16 From the uttermost part of the earth have we heard songs, glory to the righteous. But I said, I pine away, I pine away, woe is me! the treacherous dealers have dealt treacherously; yea, the treacherous dealers have dealt very treacherously.
Daga iyakokin duniya mun ji waƙoƙi, “Ɗaukaka ga Mai Adalcin nan.” Amma na ce, “Na lalace, na lalace! Kaitona! Munafukai sun ci amana! Da munafunci munafukai sun ci amana!”
17 Fear, and the pit, and the snare, are upon thee, O inhabitant of the earth.
Razana da rami da tarko suna jiranku, Ya mutanen duniya.
18 And it shall come to pass, that he who fleeth from the noise of the fear shall fall into the pit; and he that cometh up out of the midst of the pit shall be taken in the snare: for the windows on high are opened, and the foundations of the earth do shake.
Duk wanda ya yi ƙoƙarin tserewa daga ƙarar razana zai fāɗa cikin rami; wanda kuma ya tsere daga rami za a kama shi a tarko. An buɗe ƙofofin ambaliyar ruwan sama, harsashen ginin duniya suna rawa.
19 The earth is utterly broken, the earth is clean dissolved, the earth is moved exceedingly.
An tsage duniya, duniya ta farfashe ta wage, an girgiza duniya ƙwarai.
20 The earth shall stagger like a drunken man, and shall be moved to and fro like a hut; and the transgression thereof shall be heavy upon it, and it shall fall, and not rise again.
Duniya tana tangaɗi kamar mashayi, tana lilo kamar rumfa a cikin iska; laifin tayarwarta ya yi nauyi sosai har ta fāɗi ba kuwa za tă ƙara tashi ba.
21 And it shall come to pass in that day, that the LORD shall punish the host of the high ones on high, and the kings of the earth upon the earth.
A wannan rana Ubangiji zai hukunta ikokin da suke cikin sama da kuma sarakunan da suke a duniya.
22 And they shall be gathered together, as prisoners are gathered in the pit, and shall be shut up in the prison, and after many days shall they be visited.
Za a tattara su tare kamar ɗaurarru a kurkuku; za a rufe su a kurkuku a kuma hukunta su bayan kwanaki masu yawa.
23 Then the moon shall be confounded, and the sun ashamed; for the LORD of hosts shall reign in mount Zion, and in Jerusalem, and before his ancients gloriously.
Sa’an nan wata zai ruɗe, rana ta ji kunya; gama Ubangiji Maɗaukaki zai yi mulki a kan Dutsen Sihiyona da kuma a cikin Urushalima, da kuma a gaban dattawanta, da ɗaukaka.