< Ezekiel 27 >
1 The word of the LORD came again unto me, saying,
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 And thou, son of man, take up a lamentation for Tyre;
“Ɗan mutum, ka yi makoki domin Taya.
3 and say unto Tyre, O thou that dwellest at the entry of the sea, which art the merchant of the peoples unto many isles, thus saith the Lord GOD: Thou, O Tyre, hast said, I am perfect in beauty.
Ka ce wa Taya, wadda take zaune a hanyar shiga zuwa teku, kasuwar masu yawa mutane a bakin teku, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Kin ce, ya Taya, “Ni kyakkyawa ce cikakkiya.”
4 Thy borders are in the heart of the seas, thy builders have perfected thy beauty.
Manyan tekuna ne wurin zamanki; maginanki sun sa kyanki ya zama cikakke.
5 They have made all thy planks of fir trees from Senir: they have taken cedars from Lebanon to make a mast for thee.
Sun yi dukan katakanki daga itatuwan fir daga Senir; sun kwaso itatuwan al’ul daga Lebanon don su yi miki jigon jirgin ruwa.
6 Of the oaks of Bashan have they made thine oars; they have made thy benches of ivory inlaid in boxwood, from the isles of Kittim.
Da oak daga Bashan suka yi sandunan tuƙan jirgin ruwa da itatuwan kasharina daga bakin tekun Saifurus suka yi daɓe jirgin ruwanki, suka kuma manne masa hauren giwa.
7 Of fine linen with broidered work from Egypt was thy sail, that it might be to thee for an ensign; blue and purple from the isles of Elishah was thine awning.
Lilin mai kyau mai ado daga Masar ne filafilan jirgin ruwanki suka kuma zama tutarki; an yi tutarki da shuɗi da shunayya daga bakin tekun Elisha.
8 The inhabitants of Zidon and Arvad were thy rowers: thy wise men, O Tyre, were in thee, they were thy pilots.
Mutanen Sidon da Arfad su ne matuƙan jirgin ruwanki; gwanayenki, ya Taya, suna ciki a matsayi matuƙan jiragen ruwa.
9 The ancients of Gebal and the wise men thereof were in thee thy calkers: all the ships of the sea with their mariners were in thee to occupy thy merchandise.
Masu hikima na Gebal suna ciki a matsayin masu tattoshe mahaɗan katakon jirginki. Dukan jiragen ruwa da matuƙansu sukan zo wurinki don kasuwanci.
10 Persia and Lud and Put were in thine army, thy men of war: they hanged the shield and helmet in thee; they set forth thy comeliness.
“‘Mutanen Farisa, Lidiya da Fut su ne suka zama sojoji a cikin mayaƙanki. Sun rataye garkuwoyinsu da hulunan kwano a katangarki, suna kawo miki daraja.
11 The men of Arvad with thine army were upon thy walls round about, and the Gammadim were in thy towers: they hanged their shields upon thy walls round about; they have perfected thy beauty.
Mutanen Arfad da Helek sun yi tsaron katangar a kowace gefe; mutanen Gammad su ne a hasumiyoyinki. Sun rataye garkuwoyinsu kewaye da katangarki; sun sa kyanki ya zama cikakke.
12 Tarshish was thy merchant by reason of the multitude of all kinds of riches; with silver, iron, tin, and lead, they traded for thy wares.
“‘Tarshish ta yi ciniki da ke saboda yawan wadatar kayayyakinki; sun sayi kayan cinikinki da azurfa, ƙarfe, kuza da dalma.
13 Javan, Tubal, and Meshech, they were thy traffickers: they traded the persons of men and vessels of brass for thy merchandise.
“‘Girka, Tubal da Meshek sun yi kasuwanci da ke; sun sayi kayanki suka biya da bayi da kuma abubuwan da aka yi da tagulla.
14 They of the house of Togarmah traded for thy wares with horses and war-horses and mules.
“‘Mutanen Bet Togarma sun sayi kayan cinikinki da dawakai, dawakan yaƙi da alfadarai.
15 The men of Dedan were thy traffickers: many isles were the mart of thine hand: they brought thee in exchange horns of ivory and ebony.
“‘Mutanen Dedan sun yi kasuwanci da ke, bakin teku masu yawa abokan cinikinki ne; sun biya ki da hauren giwa da katakon kanya.
16 Syria was thy merchant by reason of the multitude of thy handyworks: they traded for thy wares with emeralds, purple, and broidered work, and fine linen, and coral, and rubies.
“‘Mutanen Aram sun yi ciniki da ke saboda yawan kayanki; suka sayi kayan cinikinki da zumurrudu, da shunayya, da kayan ado, da lilin mai taushi, da murjani, da yakutu.
17 Judah, and the land of Israel, they were thy traffickers: they traded for thy merchandise wheat of Minnith, and pannag, and honey, and oil, and balm:
“‘Yahuda da Isra’ila sun yi kasuwanci da ke; sun sayi kayanki da alkama da Minnit da alawa, da zuma, da mai, da ganyaye masu ƙanshi.
18 Damascus was thy merchant for the multitude of thy handyworks, by reason of the multitude of all kinds of riches; with the wine of Helbon, and white wool.
“‘Mutanen Damaskus sun ga abin da za ki iya bayarwa sai suka yi ciniki da ke, ta sayi kayanki da ruwan inabi daga Helbon, da ulu daga Zahar.
19 Vedan and Javan traded with yarn for thy wares: bright iron, cassia, and calamus, were among thy merchandise.
Wedan da Yaban kusa da Uzal, suka sayi kayanki; wato gyararren ƙarfe da kayan yaji.
20 Dedan was thy trafficker in precious cloths for riding.
“‘Mutanen Dedan sun sayi kayanki da sirdin zama a kan dawakai.
21 Arabia, and all the princes of Kedar, they were the merchants of thy hand; in lambs, and rams, and goats, in these were they thy merchants.
“‘Mutanen Arabiya da dukan sarakunan Kedar abokan cinikinki ne; sun yi ciniki da ke suka sayi kayanki da’yan raguna, da raguna, da awaki.
22 The traffickers of Sheba and Raamah, they were thy traffickers: they traded for thy wares with chief of all spices, and with all precious stones, and gold.
“‘’Yan kasuwan Sheba da Ra’ama sun yi ciniki da ke; suka sayi kayanki da kayan yaji mafi kyau iri-iri, da duwatsu masu daraja iri-iri, da zinariya.
23 Haran and Canneh and Eden, the traffickers of Sheba, Asshur [and] Chilmad were they traffickers.
“‘Haran, Kanne da Eden da kuma’yan kasuwan Sheba, Assuriya da Kilmad sun yi ciniki da ke.
24 These were thy traffickers in choice wares, in wrappings of blue and broidered work, and in chests of rich apparel, bound with cords and made of cedar, among thy merchandise.
A kasuwarki sun yi ciniki da ke suka sayar miki tufafi masu tsada, da na shuɗi, da masu ado, da dardumai masu ƙyalƙyali da kirtani, da igiyoyi waɗanda aka tuƙa da kyau.
25 The ships of Tarshish were thy caravans for thy merchandise: and thou wast replenished, and made very glorious in the heart of the seas.
“‘Jiragen ruwan Tarshish sun zama masu jigilar kayanki. Kin cika da kaya masu nauyi a tsakiyar teku.
26 Thy rowers have brought thee into great waters: the east wind hath broken thee in the heart of the seas.
Matuƙan jiragenki sun kai ki can cikin manyan tekuna. Amma iskar gabas za tă farfasa ki kucu-kucu a tsakiyar teku.
27 Thy riches, and thy wares, thy merchandise, thy mariners, and thy pilots, thy calkers, and the occupiers of thy merchandise, and all thy men of war, that are in thee, with all thy company which is in the midst of thee, shall fall into the heart of the seas in the day of thy ruin.
Dukiyarki, cinikinki da kayan kasuwarki, ma’aikatanki na jirgi, matuƙan jiragenki da masu tattoshe mahaɗan katakan jiragenki,’yan kasuwarki da dukan sojojinki, da kuma kowa da yake cikin jirgi zai nutsa a tsakiyar teku a ranar da jirginki zai nutse.
28 At the sound of the cry of thy pilots the suburbs shall shake.
Ƙasashen bakin teku za su girgiza sa’ad da matuƙan jirginki suka yi kuka.
29 And all that handle the oar, the mariners, [and] all the pilots of the sea, shall come down from their ships, they shall stand upon the land,
Dukan waɗanda suke riƙe da matuƙi za su ƙyale jiragensu; ma’aikatan jirage da dukan matuƙan jirage za su tsaya a bakin teku.
30 and shall cause their voice to be heard over thee, and shall cry bitterly, and shall cast up dust upon their heads, they shall wallow themselves in the ashes:
Za su tā da muryarsu su yi kuka mai zafi a kanki; za su yayyafa ƙura a kawunansu, su yi ta birgima a cikin toka.
31 and they shall make themselves bald for thee, and gird them with sackcloth, and they shall weep for thee in bitterness of soul with bitter mourning.
Za su aske kawunansu saboda ke za su kuma sa tufafin makoki. Za su yi kuka dominki su yi ɓacin rai da kuma kuka mai zafi.
32 And in their wailing they shall take up a lamentation for thee, and lament over thee, [saying], Who is there like Tyre, like her that is brought to silence in the midst of the sea?
Yayinda suke kuka a kanki kuwa, za su yi makoki dominki suna cewa, “Wa ya taɓa yin shiru kamar Taya, kewaye da teku?”
33 When thy wares went forth out of the seas, thou filledst many peoples; thou didst enrich the kings of the earth with the multitude of thy riches and of thy merchandise.
Sa’ad da kayan cinikinki suka tafi ƙasashen hayi, kin gamsar da al’ummai masu yawa; da dukiyarki masu yawa da kuma kayan cinikinki kin azurtar da sarakunan duniya.
34 In the time that thou wast broken by the seas in the depths of the waters, thy merchandise and all thy company did fall in the midst of thee.
Yanzu teku ta farfashe ki cikin zurfafan ruwaye; kayan cinikinki da dukan kamfaninki sun nutse tare da ke.
35 All the inhabitants of the isles are astonished at thee, and their kings are horribly afraid, they are troubled in their countenance.
Dukan mazaunan bakin teku sun giggice saboda masifarki; sarakunansu sun tsorata ƙwarai fuskokinsu kuwa sun yamutse don tsoro.
36 The merchants among the peoples hiss at thee; thou art become a terror, and thou shalt never be any more.
’Yan kasuwa a cikin al’ummai suna yin miki tsaki; kin zo ga mummunar ƙarshe ba za ki ƙara kasancewa ba har abada.’”