< Deuteronomy 14 >
1 Ye are the children of the LORD your God: ye shall not cut yourselves, nor make any baldness between your eyes for the dead.
Ku’ya’yan Ubangiji Allahnku ne. Kada ku yi wa kanku zāne, ko ku yi wa kanku aski irin da akan bar sanƙo, saboda wanda ya mutu,
2 For thou art an holy people unto the LORD thy God, and the LORD hath chosen thee to be a peculiar people unto himself, above all peoples that are upon the face of the earth.
gama ku jama’a ce mai tsarki ga Ubangiji Allahnku. Daga dukan mutane a fuskar duniya, Ubangiji ya zaɓe ku, ku zama abin mallakarsa.
3 Thou shalt not eat any abominable thing.
Kada ku ci wani haramtaccen abu.
4 These are the beasts which ye shall eat: the ox, the sheep, and the goat,
Waɗannan su ne dabbobin da za ku iya ci, saniya, tunkiya, akuya,
5 the hart, and the gazelle, and the roebuck, and the wild goat, and the pygarg, and the antelope, and the chamois.
mariri, barewa, mariya, makwarna, mazo, gada da kuma tunkiyar dutse.
6 And every beast that parteth the hoof, and hath the hoof cloven in two, [and] cheweth the cud, among the beasts, that ye shall eat.
Za ku iya cin duk dabbar da take da rababben kofato, wadda kuma take sāke tona abin da suka riga suka haɗiye.
7 Nevertheless these ye shall not eat of them that chew the cud, or of them that have the hoof cloven: the camel, and the hare, and the coney, because they chew the cud but part not the hoof, they are unclean unto you:
Amma, cikin waɗanda suke sāke tona abin da suka riga suka haɗiye ɗin, ko suke da rababben kofato, ba za ku ci raƙumi, zomo ko rema ba. Ko da yake suna sāke tona abin da suka riga suka haɗiye, suna kuma da rababben kofato, su ɗin marar tsarki ne gare ku.
8 and the swine, because he parteth the hoof but cheweth not the cud, he is unclean unto you: of their flesh ye shall not eat, and their carcases ye shall not touch.
Alade ma marar tsarki ne; ko da yake yana da rababben kofato, shi ba ya sāke tona abin da ya riga ya haɗiye. Ba za ku ci namansu ko ku taɓa gawarsu ba.
9 These ye shall eat of all that are in the waters: whatsoever hath fins and scales shall ye eat:
Cikin dukan halittun da suke cikin ruwa, za ku iya cin duk wani da yake da ƙege da ɓamɓaroki.
10 and whatsoever hath not fins and scales ye shall not eat; it is unclean unto you.
Amma duk wani abin da ba shi da ƙege da ɓamɓaroki, ba za ku ci ba; gama marar tsarki ne gare ku.
11 Of all clean birds ye may eat.
Za ku iya cin kowane tsuntsu mai tsabta.
12 But these are they of which ye shall not eat: the eagle, and the gier eagle, and the ospray;
Amma waɗannan ba za ku ci ba, gaggafa, ungulu, ungulun kwakwa,
13 and the glede, and the falcon, and the kite after its kind;
duki, buga zaɓi, kowace irin shirwa,
14 and every raven after its kind;
kowane irin hankaka,
15 and the ostrich, and the night hawk, and the seamew, and the hawk after its kind;
jimina, ƙururu, bubuƙuwa, kowane irin shaho,
16 the little owl, and the great owl, and the horned owl;
da mujiya, da babbar mujiya, ɗuskwi,
17 and the pelican, and the vulture, and the cormorant;
kwasakwasa, ungulu, da babba da jaka,
18 and the stork, and the heron after its kind, and the hoopoe, and the bat.
zalɓe, kowane irin jinjimi, katutu, da kuma jamage.
19 And all winged creeping things are unclean unto you: they shall not be eaten.
Dukan’yan ƙwari masu fikafikai masu rarrafe, haram ne a gare ku, kada ku ci su.
20 Of all clean fowls ye may eat.
Amma duk wata halitta mai fikafikai mai tsabta ce, za ku iya ci.
21 Ye shall not eat of any thing that dieth of itself: thou mayest give it unto the stranger that is within thy gates, that he may eat it; or thou mayest sell it unto a foreigner: for thou art an holy people unto the LORD thy God. Thou shalt not seethe a kid in its mother’s milk.
Kada ku ci abin da kun samu ya riga ya mutu. Za ku iya ba wa baren da yake zama a cikin wani daga biranenku, zai kuwa iya cinsa, ko kuwa za ku iya sayar da shi wa baƙo. Amma ku jama’a ce mai tsarki ga Ubangiji Allahnku. Kada ku dafa ɗan akuya a cikin madara mamansa.
22 Thou shalt surely tithe all the increase of thy seed, that which cometh forth of the field year by year.
Ku tabbata kun keɓe kashi ɗaya bisa goma na amfanin gonakinku kowace shekara.
23 And thou shalt eat before the LORD thy God, in the place which he shall choose to cause his name to dwell there, the tithe of thy corn, of thy wine, and of thine oil, and the firstlings of thy herd and of thy flock; that thou mayest learn to fear the LORD thy God always.
Ku ci zakkar hatsinku, da na sabon ruwan inabinku, da na manku, da kuma na’ya’yan fari na garkunanku na shanu da na tumaki a gaban Ubangiji Allahnku, a wurin da ya zaɓa a matsayin mazauni don Sunansa, don ku koyi girmama Ubangiji Allahnku kullum.
24 And if the way be too long for thee, so that thou art not able to carry it, because the place is too far from thee, which the LORD thy God shall choose to set his name there, when the LORD thy God shall bless thee:
Amma in wurin nan yana da nisa sosai, Ubangiji Allahnku kuma ya albarkace ku, ba za ku kuwa iya riƙe zakkarku ba (Saboda wurin da Ubangiji ya zaɓa yă sa Sunansa ya yi nisa sosai),
25 then shalt thou turn it into money, and bind up the money in thine hand, and shalt go unto the place which the LORD thy God shall choose:
to, sai ku sayar da zakkar, ku tafi da kuɗin wurin da Ubangiji Allahnku ya zaɓa.
26 and thou shalt bestow the money for whatsoever thy soul desireth, for oxen, or for sheep, or for wine, or for strong drink, or for whatsoever thy soul asketh of thee: and thou shalt eat there before the LORD thy God, and thou shalt rejoice, thou and thine household:
Yi amfani da kuɗin ku saya duk abin da kuke so, ko shanu, ko tumaki, ko ruwan inabi, ko dai wani abin shan da ya yi tsami, ko kuwa duk abin da kuke so. Sai ku da gidanku, ku ci a can, a gaban Ubangiji Allahnku, ku kuma yi farin ciki.
27 and the Levite that is within thy gates, thou shalt not forsake him; for he hath no portion nor inheritance with thee.
Kada dai ku manta da Lawiyawan da suke zama a biranenku, gama ba su da rabo, ko gādo na kansu.
28 At the end of every three years thou shalt bring forth all the tithe of thine increase in the same year, and shalt lay it up within thy gates:
A ƙarshen kowace shekara uku, ku kawo dukan zakkarku na amfanin gona na wannan shekara, ku ajiye su a cikin birane,
29 and the Levite, because he hath no portion nor inheritance with thee, and the stranger, and the fatherless, and the widow, which are within thy gates, shall come, and shall eat and be satisfied; that the LORD thy God may bless thee in all the work of thine hand which thou doest.
saboda Lawiyawa (waɗanda ba su da rabo ko gādo na kansu) da baƙo, da marayu, da kuma gwauraye, waɗanda suke zama a biranenku, su zo su ci su ƙoshi, ta haka Ubangiji Allahnku zai albarkace ku cikin dukan ayyukan hannuwanku.