< 1 Kings 4 >
1 And king Solomon was king over all Israel.
Sai Sarki Solomon ya yi mulki a bisa dukan Isra’ila.
2 And these were the princes which he had; Azariah the son of Zadok, the priest;
Waɗannan su ne manyan shugabanninsa. Azariya ɗan Zadok shi ne firist;
3 Elihoreph and Ahijah, the sons of Shisha, scribes; Jehoshaphat the son of Ahilud, the recorder;
Elihoref da Ahiya,’ya’yan Shisha maza, su ne marubuta. Yehoshafat ɗan Ahilud, shi ne mai lura da takardu.
4 and Benaiah the son of Jehoiada was over the host; and Zadok and Abiathar were priests;
Benahiya ɗan Yehohiyada, shi ne shugaban mayaƙa. Zadok da Abiyatar, su ne firistoci.
5 and Azariah the son of Nathan was over the officers; and Zabud the son of Nathan was priest, [and] the king’s friend;
Azariya ɗan Natan, shi ne mai lura da shugabannin yanki. Zabud ɗan Natan, shi ne firist da kuma mai wa sarki shawara.
6 and Ahishar was over the household; and Adoniram the son of Abda was over the levy.
Ahishar, shi ne sarkin fada. Adoniram ɗan Abda, shi ne mai lura da aikin gandu.
7 And Solomon had twelve officers over all Israel, which provided victuals for the king and his household: each man had to make provision for a month in the year:
Solomon yana da gwamnoni yankuna goma sha biyu a bisa dukan Isra’ila, waɗanda suke tanaji abinci domin sarki da kuma gidan sarauta. Kowanne yakan tanada abinci na wata ɗaya a shekara.
8 And these are their names: Ben-hur, in the hill country of Ephraim:
Ga sunayensu, Ben-Hur, shi ne a ƙasar tudun Efraim;
9 Ben-deker, in Makaz, and in Shaalbim, and Beth-shemesh, and Elon-beth-hanan:
Ben-Deker, shi ne a Makaz, Sha’albim, Bet-Shemesh da Elon Bet-Hanan;
10 Ben-hesed, in Arubboth; to him [pertained] Socoh, and all the land of Hepher:
Ben-Hesed, shi ne a Arubbot (Soko da dukan ƙasar Hefer);
11 Ben-abinadab, in all the height of Dor; he had Taphath the daughter of Solomon to wife:
Ben-Abinadab, shi ne a Nafot Dor (ya auri Tafat’yar Solomon);
12 Baana the son of Ahilud, in Taanach and Megiddo, and all Beth-shean which is beside Zarethan, beneath Jezreel, from Beth-shean to Abel-meholah, as far as beyond Jokmeam:
Ba’ana ɗan Ahilud, shi ne a Ta’anak da Megiddo, da kuma dukan Bet-Sheyan biye da Zaretan ƙasa da Yezireyel, daga Bet-Sheyan zuwa Abel-Mehola a ƙetaren Yokmeyam;
13 Ben-geber, in Ramoth-gilead; to him [pertained] the towns of Jair the son of Manasseh, which are in Gilead; [even] to him [pertained] the region of Argob, which is in Bashan, threescore great cities with walls and brasen bars:
Ben-Geber, shi ne a Ramot Gileyad (Mazaunan Yayir ɗan Manasse a Gileyad suna a ƙarƙashinsa, haka ma yankin Argob a Bashan tare da manyan biranen sittin masu katanga da suke da ƙyamare na tagulla);
14 Ahinadab the son of Iddo, in Mahanaim:
Ahinadab ɗan Iddo, shi ne a Mahanayim;
15 Ahimaaz, in Naphtali; he also took Basemath the daughter of Solomon to wife:
Ahimawaz, shi ne a Naftali (ya auri Basemat’yar Solomon);
16 Baana the son of Hushai, in Asher and Bealoth:
Ba’ana ɗan Hushai, shi ne a Asher da Bayelot;
17 Jehoshaphat the son of Paruah, in Issachar:
Yehoshafat ɗan Faruwa, shi ne a Issakar;
18 Shimei the son of Ela, in Benjamin:
Shimeyi ɗan Ela, shi ne a Benyamin;
19 Geber the son of Uri, in the land of Gilead, the country of Sihon king of the Amorites and of Og king of Bashan; and [he was] the only officer which was in the land.
Geber ɗan Uri, shi ne a Gileyad (ƙasar Sihon sarkin Amoriyawa da kuma Og sarkin Bashan). Shi ne kaɗai gwamna a bisa yankin.
20 Judah and Israel were many, as the sand which is by the sea in multitude, eating and drinking and making merry.
Mutanen Yahuda da na Isra’ila sun yi yawa sai ka ce yashi a bakin teku. Suka ci, suka sha, suka kuma yi farin ciki.
21 And Solomon ruled over all the kingdoms from the River unto the land of the Philistines, and unto the border of Egypt: they brought presents, and served Solomon all the days of his life.
Solomon kuwa ya yi mulki a bisa dukan masarautai daga Kogi zuwa ƙasar Filistiyawa, har zuwa iyakar Masar. Waɗannan ƙasashe sun yi ta kawo haraji, suka kuma zama bayin Solomon dukan kwanakin ransa.
22 And Solomon’s provision for one day was thirty measures of fine flour, and threescore measures of meal;
Tanajin Solomon na kowace rana su ne, garwa talatin na garin abinci,
23 ten fat oxen, and twenty oxen out of the pastures, and an hundred sheep, beside harts, and gazelles, and roebucks, and fatted fowl.
shanun da aka yi kiwo a gida guda goma, shanu ashirin da suka ƙoshi daga kiwo, tumaki da awaki ɗari; ban da ƙishimai, bareyi, batsiyoyi, da kaji masu ƙiba.
24 For he had dominion over all [the region] on this side the River, from Tipsah even to Gaza, over all the kings on this side the River: and he had peace on all sides round about him.
Gama ya yi mulki a bisa dukan masarautai yamma da Kogi, daga Tifsa zuwa Gaza, aka kuwa sami zaman lafiya a kowane gefe.
25 And Judah and Israel dwelt safely, every man under his vine and under his fig tree, from Dan even to Beer-sheba, all the days of Solomon.
A kwanakin da Solomon yake raye, Yahuda da Isra’ila, daga Dan zuwa Beyersheba, sun zauna lafiya, kowane mutum ya zauna a ƙarƙashin itacen inabi da na ɓaurensa.
26 And Solomon had forty thousand stalls of horses for his chariots, and twelve thousand horsemen.
Solomon yana da rumfunan dawakai masu jan kekunan yaƙi, dubu huɗu, da kuma dawakai dubu goma sha biyu
27 And those officers provided victual for king Solomon, and for all that came unto king Solomon’s table, every man in his month: they let nothing be lacking.
Shugabannin yankuna, kowanne a watansa yakan yi tanajin abinci domin Sarki Solomon da kuma duk wanda ya zo teburin sarki. Sun tabbatar ba a rasa kome ba.
28 Barley also and straw for the horses and swift steeds brought they unto the place where [the officers] were, every man according to his charge.
Kowa a cikinsu, bisa ga lokacin da aka ba shi, yakan kai hatsin sha’ir da ciyawa domin dawakan-kekunan yaƙi, da sauran dawakai a inda aka ajiye su.
29 And God gave Solomon wisdom and understanding exceeding much, and largeness of heart, even as the sand that is on the sea shore.
Allah ya ba Solomon hikima da hangen nesa mai girma, da kuma fāɗin fahimta marar iyaka, kamar yashi a bakin teku.
30 And Solomon’s wisdom excelled the wisdom of all the children of the east, and all the wisdom of Egypt.
Hikimar Solomon ta fi hikimar mutanen Gabas, ta kuma fi dukan hikimar Masar girma.
31 For he was wiser than all men; than Ethan the Ezrahite, and Heman, and Calcol, and Darda, the sons of Mahol: and his fame was in all the nations round about.
Ya fi kowane mutum hikima, har da Etan dangin Ezra ma. Yana da hikima fiye da Heman, Kalkol da Darda,’ya’yan Mahol maza. Sunansa ya bazu ko’ina a ƙasashen da suke kewaye.
32 And he spake three thousand proverbs: and his songs were a thousand and five.
Ya yi karin magana dubu uku. Waƙoƙinsa kuwa sun kai dubu ɗaya da biyar.
33 And he spake of trees, from the cedar that is in Lebanon even unto the hyssop that springeth out of the wall: he spake also of beasts, and of fowl, and of creeping things, and of fishes.
Ya yi magana a kan rayuwar itatuwa, daga al’ul na Lebanon zuwa hizzob da yake girma a bangaye. Ya kuma yi koyarwa game da dabbobi, da tsuntsaye, da abubuwa masu rarrafe, da kuma kifi.
34 And there came of all peoples to hear the wisdom of Solomon, from all kings of the earth, which had heard of his wisdom.
Mutane suka yi ta zuwa daga ƙasashe dabam-dabam don su ji hikimar Solomon. Sarakuna daga ko’ina a duniya, sun ji labarin hikimarsa, suka kuma aika da mutane don su ji shi.