< 1 Corinthians 10 >
1 For I would not, brethren, have you ignorant, how that our fathers were all under the cloud, and all passed through the sea;
Ina son ku sani, 'yan'uwa, cewa ubaninmu duka suna karkashin gajimarai kuma sun bi ta cikin teku.
2 and were all baptized unto Moses in the cloud and in the sea;
Dukansu an yi masu baftisma cikin gajimarai da kuma teku,
3 and did all eat the same spiritual meat;
kuma dukansu sun ci abincin ruhaniya iri daya.
4 and did all drink the same spiritual drink: for they drank of a spiritual rock that followed them: and the rock was Christ.
Dukansu sun sha abin sha na ruhaniya iri daya. Gama sun sha daga wani dutsen ruhaniya da ya bisu, kuma wannan dutsen Almasihu ne.
5 Howbeit with most of them God was not well pleased: for they were overthrown in the wilderness.
Amma Ubangiji bai ji dadin yawancinsu ba, saboda haka gawawakin su suka bazu a jeji.
6 Now these things were our examples, to the intent we should not lust after evil things, as they also lusted.
Wadan nan al'amura, an rubuta mana su domin muyi koyi da su, kada mu yi sha'awar miyagun ayyuka kamar yadda suka yi.
7 Neither be ye idolaters, as were some of them; as it is written, The people sat down to eat and drink, and rose up to play.
Kada ku zama masu bautar gumaka kamar yadda wadansun su suka yi. Wannan kamar yadda aka rubuta ne, “Mutanen sukan zauna su ci su sha kuma su tashi suyi wasa.”
8 Neither let us commit fornication, as some of them committed, and fell in one day three and twenty thousand.
Kada mu shiga zina da faskanci kamar yadda yawancin su suka yi, a rana guda mutane dubu ashirin da uku suka mutu.
9 Neither let us tempt the Lord, as some of them tempted, and perished by the serpents.
Kada mu gwada Almasihu kamar yadda yawancinsu suka yi, macizai suka yi ta kashe su.
10 Neither murmur ye, as some of them murmured, and perished by the destroyer.
kada kuma ku zama masu gunaguni kamar yadda suka yi, suka yi ta mutuwa a hannun malaikan mutuwa.
11 Now these things happened unto them by way of example; and they were written for our admonition, upon whom the ends of the ages are come. (aiōn )
Wadannan abubuwa sun faru dasu ne a matsayin misalai a garemu. An rubuta su domin gargadinmu - mu wadanda karshen zamanai yazo kanmu. (aiōn )
12 Wherefore let him that thinketh he standeth take heed lest he fall.
Saboda haka, bari duk wanda yake tunanin shi tsayyaye ne, to yayi hattara kada ya fadi.
13 There hath no temptation taken you but such as man can bear: but God is faithful, who will not suffer you to be tempted above that ye are able; but will with the temptation make also the way of escape, that ye may be able to endure it.
Babu gwajin da ya same ku wanda ba a saba da shi ba cikin dukan mutane. A maimako, Allah mai aminci ne. Da ba zaya bari ku jarabtu ba fiye da iyawarku. Tare da gwajin zai tanadar da hanyar fita, domin ku iya jurewa.
14 Wherefore, my beloved, flee from idolatry.
Saboda haka ya kaunatattu na, ku guji bautar gumaka.
15 I speak as to wise men; judge ye what I say.
Ina magana da ku kamar masu zurfin tunani, domin ku auna abin da ni ke fadi.
16 The cup of blessing which we bless, is it not a communion of the blood of Christ? The bread which we break, is it not a communion of the body of Christ?
Kokon albarka da muke sa wa albarka, ba tarayya bane cikin jinin Almasihu? Gurasa da muke karyawa ba tarayya bane cikin jikin Almasihu?
17 seeing that we, who are many, are one bread, one body: for we all partake of the one bread.
Domin akwai gurasa guda, mu da muke dayawa jiki daya ne. Dukanmu munci daga gurasa daya ne.
18 Behold Israel after the flesh: have not they which eat the sacrifices communion with the altar?
Dubi mutanen Isra'ila: ba wadanda ke cin hadayu ke da rabo a bagadi ba?
19 What say I then? that a thing sacrificed to idols is anything, or that an idol is anything?
Me nake cewa? gunki wani abu ne? Ko kuma abincin da aka mika wa gunki hadaya wani abu ne?
20 But [I say], that the things which the Gentiles sacrifice, they sacrifice to devils, and not to God: and I would not that ye should have communion with devils.
Amma ina magana game da abubuwan da al'ummai suke hadaya, suna wa aljannu ne hadaya ba Allah ba. Ba na son kuyi tarayya da al'janu!
21 Ye cannot drink the cup of the Lord, and the cup of devils: ye cannot partake of the table of the Lord, and of the table of devils.
Ba zaku sha daga kokon Ubangiji ku kuma sha na Al'janu ba, ba za kuyi zumunta a teburin Ubangiji ku yi a na Al'janu ba.
22 Or do we provoke the Lord to jealousy? are we stronger than he?
Ko muna so mu sa Ubangiji kishi ne? Mun fi shi karfi ne?
23 All things are lawful; but all things are not expedient. All things are lawful; but all things edify not.
“Komai dai dai ne,” amma ba komai ke da amfani ba, “Komai dai dai ne,” amma ba komai ke gina mutane ba.
24 Let no man seek his own, but [each] his neighbour’s [good].
Kada wani ya nemi abinda zaya amfane shi. A maimako, kowa ya nemi abinda zaya amfani makwabcinsa.
25 Whatsoever is sold in the shambles, eat, asking no question for conscience sake;
Kana iya cin duk abin da ake sayarwa a kasuwa, ba tare da tamboyoyin lamiri ba.
26 for the earth is the Lord’s, and the fulness thereof.
Gama “duniya da duk abin da ke cikin ta na Ubangiji ne.”
27 If one of them that believe not biddeth you [to a feast], and ye are disposed to go; whatsoever is set before you, eat, asking no question for conscience sake.
Idan marar bangaskiya ya gayyace ka cin abinci, kana kuma da niyyar zuwa, ka je ka ci duk abinda aka kawo maka, ba tare da tamboyoyin lamiri ba.
28 But if any man say unto you, This hath been offered in sacrifice, eat not, for his sake that shewed it, and for conscience sake:
Amma idan wani ya ce maka, “Wannan abinci an yi wa gumaka hadaya da shi ne” To kada ka ci. Wannan za ka yi ne saboda wanda ya shaida maka, da kuma lamiri ( gama duniya da dukan abinda ke cikin ta na Ubangiji ne).
29 conscience, I say, not thine own, but the other’s; for why is my liberty judged by another conscience?
Ba ina nufin lamirin ka ba, amma lamirin wanda ya fada maka. Don me za a hukunta 'yanci na domin lamirin wani?
30 If I by grace partake, why am I evil spoken of for that for which I give thanks?
Idan na ci abincin tare da bada godiya, don mi za a zage ni don abin da na bada godiya a kansa?
31 Whether therefore ye eat, or drink, or whatsoever ye do, do all to the glory of God.
Saboda haka, ko kana ci ko kana shi, ka yi komai domin daukakar Allah.
32 Give no occasion of stumbling, either to Jews, or to Greeks, or to the church of God:
Kada ka zama sanadiyyar tuntube, ga Yahudawa, ko Helenawa, ko ikilisiyar Allah.
33 even as I also please all men in all things, not seeking mine own profit, but the [profit] of the many, that they may be saved.
Na yi kokari in farantawa dukan mutane rai cikin dukan abubuwa. Ba riba nake nema wa kaina ba, amma domin kowa. Na yi wannan ne domin su sami ceto.