< 1 Chronicles 5 >
1 And the sons of Reuben the firstborn of Israel, (for he was the firstborn; but, forasmuch as he defiled his father’s couch, his birthright was given unto the sons of Joseph the son of Israel; and the genealogy is not to be reckoned after the birthright.
’Ya’yan Ruben maza ɗan farin Isra’ila (shi ne ɗan fari, amma sa’ad da ya ƙazantar da gadon auren mahaifinsa, sai aka ba wa’yancin ɗan farinsa wa’ya’yan Yusuf maza ɗan Isra’ila; don kada a lissafta shi a tarihin zuriya bisa ga matsayin haihuwarsa,
2 For Judah prevailed above his brethren, and of him came the prince; but the birthright was Joseph’s: )
ko da yake Yahuda shi ne mafi ƙarfi cikin’yan’uwansa kuma mai mulki ya fito daga gare shi,’yancin zaman ɗan fari na Yusuf ne),
3 the sons of Reuben the firstborn of Israel; Hanoch, and Pallu, Hezron, and Carmi.
’ya’yan Ruben ɗan farin Isra’ila maza su ne, Hanok, Fallu, Hezron da Karmi.
4 The sons of Joel; Shemaiah his son, Gog his son, Shimei his son;
Zuriyar Yowel su ne, Shemahiya, Gog, Shimeyi,
5 Micah his son, Reaiah his son, Baal his son;
Mika, Reyahiya, Ba’al,
6 Beerah his son, whom Tilgath-pilneser king of Assyria carried away captive: he was prince of the Reubenites.
da Beyera, wanda Tiglat-Fileser sarkin Assuriya ya ɗauka zuwa zaman bauta. Beyera shi ne shugaban mutanen Ruben.
7 And his brethren by their families, when the genealogy of their generations was reckoned; the chief, Jeiel, and Zechariah,
Danginsu bisa ga iyalansu da aka jera bisa ga tarihin zuriyarsu su ne, Yehiyel shi ne sarki, akwai Zakariya,
8 and Bela the son of Azaz, the son of Shema, the son of Joel, who dwelt in Aroer, even unto Nebo and Baal-meon:
da Bela ɗan Azaz. Azaz ɗan Shema daga dangin Yowel. Yowel ya yi zama a yankin Arower har zuwa Nebo da Ba’al-Meyon.
9 and eastward he dwelt even unto the entering in of the wilderness from the river Euphrates: because their cattle were multiplied in the land of Gilead.
Ta waje gabas sun zauna a ƙasar har zuwa bakin hamadan da ya nausa zuwa Kogin Yuferites, domin dabbobinsu sun ƙaru a Gileyad.
10 And in the days of Saul they made war with the Hagrites, who fell by their hand: and they dwelt in their tents throughout all the [land] east of Gilead.
A zamanin Shawulu zuriyar Ruben sun yi yaƙi da Hagirawa, suka ci su da yaƙi, suka zauna a wuraren zaman Hagirawan ko’ina a dukan yankin gabashin Gileyad.
11 And the sons of Gad dwelt over against them, in the land of Bashan unto Salecah:
Mutanen Gad sun zauna kusa da mutanen Ruben a Bashan, har zuwa Saleka.
12 Joel the chief, and Shapham the second, and Janai, and Shaphat in Bashan:
Yowel shi ne babba, sai Shafan na biyu, sa’an nan Yanai da Shafat, su ne tushen Bashan.
13 And their brethren of their fathers’ houses; Michael, and Meshullam, and Sheba, and Jorai, and Jacan, and Zia, and Eber, seven.
Danginsu, bisa ga iyalai su ne, Mika’ilu, Meshullam, Sheba, Yorai, Yakan, Ziya da Eber, su bakwai ne duka.
14 These were the sons of Abihail the son of Huri, the son of Jaroah, the son of Gilead, the son of Michael, the son of Jeshishai, the son of Jahdo, the son of Buz;
Waɗannan su ne’ya’yan Abihayil ɗan Huri, ɗan Yarowa, ɗan Gileyad, ɗan Mika’ilu, ɗan Yeshishai, ɗan Yado, ɗan Buz.
15 Ahi the son of Abdiel, the son of Guni, chief of their fathers’ houses.
Ahi ɗan Abiyel, ɗan Guni, shi ne kan iyalinsu.
16 And they dwelt in Gilead in Bashan, and in her towns, and in all the suburbs of Sharon, as far as their borders.
Mutanen Gad sun zauna a Bashan da ƙauyukan da suke kurkusa da shi, da kuma a dukan makiyayan Sharon har zuwa iyaka inda suka kai.
17 All these were reckoned by genealogies in the days of Jotham king of Judah, and in the days of Jeroboam king of Israel.
Dukan waɗannan sun shiga tarihin zuriya a lokacin mulkin Yotam sarkin Yahuda da Yerobowam sarkin Isra’ila.
18 The sons of Reuben, and the Gadites, and the half tribe of Manasseh, of valiant men, men able to bear buckler and sword, and to shoot with bow, and skilful in war, were forty and four thousand seven hundred and threescore, that were able to go forth to war.
Mutanen Ruben, mutanen Gad da rabin kabilar Manasse sun kasance da mutane 44,760 shiryayyu don aikin soja, jarumawan da za su iya riƙe garkuwa da takobi, waɗanda suke iya yin amfani da baka, waɗanda kuma aka horar don yaƙi.
19 And they made war with the Hagrites, with Jetur, and Naphish, and Nodab.
Suka yi yaƙi da Hagirawa, Yetur, Nafish da Nodab.
20 And they were helped against them, and the Hagrites were delivered into their hand, and all that were with them: for they cried to God in the battle, and he was entreated of them; because they put their trust in him.
Aka taimake su a yaƙin, Allah kuma ya ba da Hagirawa da dukan abokansu gare su, domin sun yi kuka gare shi a lokacin yaƙin. Ya amsa addu’o’insu, domin sun dogara gare shi.
21 And they took away their cattle; of their camels fifty thousand, and of sheep two hundred and fifty thousand, and of asses two thousand, and of men an hundred thousand.
Suka ƙwace dabbobin Hagirawa, raƙuma dubu hamsin, tumaki dubu ɗari biyu da hamsin da kuma jakuna dubu biyu. Suka kuma kame mutane dubu ɗari ɗaya,
22 For there fell many slain, because the war was of God. And they dwelt in their stead until the captivity.
waɗansu suka mutu, domin yaƙin na Allah ne. Suka zauna a ƙasar har lokacin da aka kai su zaman bauta.
23 And the children of the half tribe of Manasseh dwelt in the land: they increased from Bashan unto Baal-hermon and Senir and mount Hermon.
Mutanen rabin kabilar Manasse sun yi yawa; suka zauna a ƙasar daga Bashan har zuwa Ba’al-Hermon, wato, zuwa Senir (Dutsen Hermon).
24 And these were the heads of their fathers’ houses; even Epher, and Ishi, and Eliel, and Azriel, and Jeremiah, and Hodaviah, and Jahdiel, mighty men of valour, famous men, heads of their fathers’ houses.
Waɗannan su ne kawunan iyalansu. Efer, Ishi, Eliyel, Azriyel, Irmiya, Hodawiya da Yadiyel. Su jarumawa ne, sanannu, su ne kuma kawunan iyalansu.
25 And they trespassed against the God of their fathers, and went a whoring after the gods of the peoples of the land, whom God destroyed before them.
Amma ba su yi aminci da Allahn kakanninsu ba, suka kuma yi karuwanci ga waɗansu allolin mutanen ƙasar, waɗanda Allah ya hallaka a gabansu.
26 And the God of Israel stirred up the spirit of Pul king of Assyria, and the spirit of Tilgath-pilneser king of Assyria, and he carried them away, even the Reubenites, and the Gadites, and the half tribe of Manasseh, and brought them unto Halah, and Habor, and Hara, and to the river of Gozan, unto this day.
Saboda haka Allah na Isra’ila ya zuga ruhun Ful sarkin Assuriya (wato, Tiglat-Fileser sarkin Assuriya), wanda ya kwashe mutanen Ruben, mutanen Gad da rabin kabilar Manasse zuwa zaman bauta. Ya kwashe su zuwa Hala, Habor, Hara da kuma kogin Gozan, inda suke har wa yau.