< 1 Chronicles 16 >
1 And they brought in the ark of God, and set it in the midst of the tent that David had pitched for it: and they offered burnt offerings and peace offerings before God.
Suka fa kawo akwatin alkawarin Allah, suka sa a cikin tentin da Dawuda ya kafa dominsa, suka kuma miƙa hadayun ƙonawa da hadayu na salama a gaban Allah.
2 And when David had made an end of offering the burnt offering and the peace offerings, he blessed the people in the name of the LORD.
Bayan Dawuda ya gama miƙa hadayu na ƙonawa da hadayu na salama, sai ya albarkaci mutane a cikin sunan Ubangiji.
3 And he dealt to every one of Israel, both man and woman, to every one a loaf of bread, and a portion [of flesh], and a cake of raisins.
Sa’an nan ya ba da dunƙulen burodi da wainar dabino da kuma kauɗar zabibi ga kowane mutumin Isra’ila namiji da ta mace.
4 And he appointed certain of the Levites to minister before the ark of the LORD, and to celebrate and to thank and praise the LORD, the God of Israel:
Ya sa Lawiyawa su yi hidima a gaban akwatin alkawarin Ubangiji, su ɗaukaka, su gode, su kuma yabi Ubangiji, Allah na Isra’ila.
5 Asaph the chief, and second to him Zechariah, Jeiel, and Shemiramoth, and Jehiel, and Mattithiah, and Eliab, and Benaiah, and Obed-edom, and Jeiel, with psalteries and with harps; and Asaph with cymbals, sounding aloud;
Asaf shi ne babba, sai Zakariya na biye, sa’an nan Ya’aziyel, Shemiramot, Yehiyel, Mattitiya, Eliyab, Benahiya, Obed-Edom da Yehiyel. Su ne za su kaɗa molaye, da garayu, Asaf kuwa zai buga ganguna,
6 and Benaiah and Jahaziel the priests with trumpets continually, before the ark of the covenant of God.
Benahiya da Yahaziyel firistoci za su busa ƙahoni kullum a gaban akwatin alkawarin Allah.
7 Then on that day did David first ordain to give thanks unto the LORD, by the hand of Asaph and his brethren.
A wannan rana, da farko, Dawuda ya sa Asaf da’yan’uwansa su rera wannan zabura ta yabo ga Ubangiji.
8 O give thanks unto the LORD, call upon his name; make known his doings among the peoples.
Ku yi godiya ga Ubangiji, ku yi shelar sunansa; ku sanar a cikin al’ummai abin da ya yi.
9 Sing unto him, sing praises unto him; talk ye of all his marvelous works.
Ku rera gare shi, ku rera yabo gare shi; ku faɗa dukan ayyukan banmamakinsa.
10 Glory ye in his holy name: let the heart of them rejoice that seek the LORD.
Ku ɗaukaka a cikin sunansa mai tsarki bari zukatan waɗanda suke neman Ubangiji su yi farin ciki.
11 Seek ye the LORD and his strength; seek his face evermore.
Ku dogara ga Ubangiji da kuma ƙarfinsa; ku nemi fuskarsa kullum.
12 Remember his marvelous works that he hath done; his wonders, and the judgments of his mouth;
Ku tuna ayyukan banmamakin da ya aikata, mu’ujizansa da kuma hukuntai da ya yanke,
13 O ye seed of Israel his servant, ye children of Jacob, his chosen ones.
Ya ku zuriyar Isra’ila bayinsa, Ya ku’ya’yan Yaƙub maza, zaɓaɓɓunsa.
14 He is the LORD our God: his judgments are in all the earth.
Shi ne Ubangiji Allahnmu; hukuntansa suna a cikin dukan duniya.
15 Remember his covenant for ever, the word which he commanded to a thousand generations;
Yakan tuna da alkawarinsa har abada, maganar da ya umarta, har tsararraki dubu,
16 [The covenant] which he made with Abraham, and his oath unto Isaac;
alkawarin da ya yi wa Ibrahim rantsuwar da ya yi ga Ishaku.
17 And confirmed the same unto Jacob for a statute, to Israel for an everlasting covenant:
Ya tabbatar da shi ga Yaƙub kamar ƙa’ida, ga Isra’ila kamar madawwamin alkawari.
18 Saying, Unto thee will I give the land of Canaan, the lot of your inheritance:
“Gare ka zan ba da ƙasar Kan’ana kamar rabon da za ka gāda.”
19 When ye were but a few men in number; yea, very few, and sojourners in it;
Sa’ad da suke kima, kima sosai, da kuma baƙi a cikinta,
20 And they went about from nation to nation, and from one kingdom to another people.
suka yi ta yawo daga al’umma zuwa al’umma, daga wannan mulki zuwa wancan.
21 He suffered no man to do them wrong; yea, he reproved kings for their sakes;
Bai bar wani ya zalunce su ba; saboda su ya tsawata wa sarakuna.
22 [Saying], Touch not mine anointed ones, and do my prophets no harm.
“Kada ku taɓa shafaffuna; kada ku yi wa annabawana lahani.”
23 Sing unto the LORD, all the earth; shew forth his salvation from day to day.
Ku rera ga Ubangiji, ku duniya duka; ku yi shelar cetonsa kowace rana.
24 Declare his glory among the nations, his marvelous works among all the peoples.
Ku furta ɗaukakarsa a cikin al’ummai, ayyukansa masu al’ajabai a cikin mutane.
25 For great is the LORD, and highly to be praised: he also is to be feared above all gods.
Gama Ubangiji mai girma ne ya kuma cancanci yabo; dole a ji tsoronsa fiye da dukan alloli.
26 For all the gods of the peoples are idols: but the LORD made the heavens.
Gama dukan allolin al’ummai gumaka ne, amma Ubangiji ya yi sammai.
27 Honour and majesty are before him: strength and gladness are in his place.
Daraja da ɗaukaka suna a gabansa; ƙarfi da farin ciki suna a wurin zamansa.
28 Give unto the LORD, ye kindreds of the peoples, give unto the LORD glory and strength.
Ku yabi Ubangiji, ku iyalan al’ummai, ku yabi ɗaukaka da ƙarfin Ubangiji,
29 Give unto the LORD the glory due unto his name: bring an offering, and come before him: worship the LORD in the beauty of holiness.
ku ba wa Ubangiji ɗaukakar da ta dace da sunansa. Ku kawo hadaya ku kuma zo gabansa; ku yi wa Ubangiji sujada cikin darajar tsarkinsa.
30 Tremble before him, all the earth: the world also is stablished that it cannot be moved.
Ku yi rawar jiki a gabansa, ya ku duniya duka! Duniya ta kahu sosai; ba za tă jijjigu ba.
31 Let the heavens be glad, and let the earth rejoice; and let them say among the nations, The LORD reigneth.
Bari sammai su yi farin ciki, bari duniya tă yi murna; bari su ce a cikin al’ummai, “Ubangiji yana mulki!”
32 Let the sea roar and the fulness thereof; let the field exult, and all that is therein;
Bari teku da kome da yake cikinsa su yi ruri; bari gonaki da kome a cikinsu su yi farin ciki!
33 Then shall the trees of the wood sing for joy before the LORD, for he cometh to judge the earth.
Sa’an nan itatuwan jeji za su rera, za su rera don farin ciki a gaban Ubangiji, gama ya zo don yă hukunta duniya.
34 O give thanks unto the LORD; for he is good: for his mercy [endureth] for ever.
Ku yi godiya ga Ubangiji, gama shi nagari ne; ƙaunarsa madawwamiya ce.
35 And say ye, Save us, O God of our salvation, and gather us together and deliver us from the nations, to give thanks unto thy holy name, and to triumph in thy praise.
Ku yi kuka, ku ce, “Cece mu, ya Allah Mai Cetonmu; tara mu ka kuma cece mu daga al’ummai, don mu yi godiya ga sunanka mai tsarki, don mu ɗaukaka a cikin yabonka.”
36 Blessed be the LORD, the God of Israel, from everlasting even to everlasting. And all the people said, Amen, and praised the LORD.
Yabi Ubangiji, Allah na Isra’ila, daga madawwami zuwa madawwami. Sai dukan mutane suka ce, “Amin.” Suka kuma “Yabi Ubangiji.”
37 So he left there, before the ark of the covenant of the LORD, Asaph and his brethren, to minister before the ark continually, as every day’s work required:
Dawuda ya bar Asaf da’yan’uwansa a gaban akwatin alkawarin Ubangiji don su yi hidima a can kullum, bisa ga tsari na kowace rana.
38 and Obed-edom with their brethren, threescore and eight; Obed-edom also the son of Jeduthun and Hosah to be doorkeepers:
Ya kuma bar Obed-Edom da’yan’uwansa sittin da takwas don su yi hidima tare. Obed-Edom ɗan Yedutun da Hosa kuma, su ne matsaran ƙofofi.
39 and Zadok the priest, and his brethren the priests, before the tabernacle of the LORD in the high place that was at Gibeon,
Dawuda ya bar Zadok firist da’yan’uwansa firistoci a gaban tabanakul na Ubangiji a tudun da yake a Gibeyon
40 to offer burnt offerings unto the LORD upon the altar of burnt offering continually morning and evening, even according to all that is written in the law of the LORD, which he commanded unto Israel;
don su miƙa hadayun ƙonawa ga Ubangiji a kan bagaden hadaya ta ƙonawa kullum, da safe da kuma yamma, bisa ga kome da yake a rubutacce a cikin Dokar Ubangiji, da ya ba wa Isra’ila.
41 and with them Heman and Jeduthun, and the rest that were chosen, who were expressed by name, to give thanks to the LORD, because his mercy [endureth] for ever;
Tare da su akwai Heman da Yedutun da sauran waɗannan zaɓaɓɓun da aka rubuta sunansu don yin godiya ga Ubangiji, “gama ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
42 and with them Heman and Jeduthun [with] trumpets and cymbals for those that should sound aloud, and [with] instruments for the songs of God: and the sons of Jeduthun to be at the gate.
Heman da Yedutun su ne da hakkin busa ƙahoni da kaɗa kuge da sauran kayan bushe-bushe da na kaɗe-kaɗe, waɗanda ake amfani da su lokacin da ake rera waƙoƙi masu tsarki.’Ya’yan Yedutun maza, su aka ba wa aikin tsaron ƙofa.
43 And all the people departed every man to his house: and David returned to bless his house.
Sa’an nan dukan mutanen suka tashi, kowa ya koma gidansa, Dawuda ya koma gida yă sa wa iyalinsa albarka.