< Revelation 11 >

1 Then I was given a measure like a rod, and a voice said to me – ‘Go and measure the Temple of God and the altar, and count the worshiper there.
Aka bani sanda in yi amfani da ita kamar sandar awo. Aka ce mani, “Tashi ka auna haikalin Allah da bagadi, da wadanda ke sujada a cikinsa.
2 But omit the court outside the Temple, and do not measure that, for it has been given up to the nations; and the holy City will be under their heel for forty-two months.
Amma kada ka auna harabar haikalin, domin an ba da shi ga Al'ummai. Za su tattake birnin mai tsarki har wata arba'in da biyu.
3 Then I will give permission to my Two Witnesses, and for those twelve hundred and sixty days they will continue teaching, clothed in sackcloth.’
Zan ba shaidu na biyu iko su yi anabci na kwanaki dubu daya da dari biyu da sittin, sanye da tsummoki.
4 These men are represented by the two olive trees and the two lamps that stand before the Lord of the earth.
Wadannan shaidu sune itatuwan zaitun biyu da kuma fitilu biyu da suke tsaye a gaban Ubangijin duniya.
5 When anyone wishes to harm them, fire comes from their mouths and consumes their enemies; and whoever wishes to harm them will, in this way, inevitably perish.
Idan wani ya yi niyyar cutar da su, wuta na fitowa daga bakinsu ta lashe makiyansu. Duk mai son cutar da su, dole a kashe shi ta wannan hanya.
6 These men have the power to close the heavens, so that no rain may fall during the time that they are teaching; and they have power to turn the streams into blood, and to smite the land with any curse, whenever they will.
Wadannan shaidu suna da iko su kulle sama domin kada a yi ruwa a lokacin da suke anabci. Suna da iko su juya ruwaye su zama jini, su kuma bugi duniya da kowacce irin annoba duk lokacin da suka ga dama.
7 As soon as they have completed their testimony, the wild Beast that ascends from the bottomless pit will make war on them and conquer and kill them. (Abyssos g12)
Sa'adda suka gama shaidarsu, dabban da ke fitowa daga rami marar iyaka zai yi yaki da su. Zai ci nasara da su ya kashe su. (Abyssos g12)
8 Their dead bodies will lie in the streets of the great city, which is mystically spoken of as ‘Sodom’ and ‘Egypt,’ where their Master was crucified.
Gawawwakinsu zasu kwanta kan hanyar babban birnin nan (wanda ma'anar sa ake kira Saduma da Masar) inda aka gicciye Ubangijinsu.
9 People of all nations, and tribes, and languages, and races look at their dead bodies for three days and a half, and do not allow them to be laid in a grave.
Wajen kwana uku da rabi wadansu daga dukan mutane, da kabila, da harshe, da al'umma za su yi kallon gawawwakinsu. Za su ki yarda a sa su cikin kabari.
10 Those who live on the earth rejoice over them and are merry, and they will send presents to one another, because these two prophets brought torments on those who live on the earth.
Mazaunan duniya zasu yi murna da biki a kansu. Har za su aika wa juna kyautai saboda annabawan nan biyu da suka azabtar da mazaunan duniya.
11 After three days and a half the life-giving breath of God entered these men, and they stood up on their feet, and a great terror took possession of those who were watching them.
Amma bayan kwana uku da rabi, numfanshin rai daga wurin Allah zai shiga cikinsu sa'annan za su tsaya a kan kafafunsu. Matsanancin tsoro zata fado kan wadanda za su gansu.
12 The two men heard a loud voice from heaven which said to them – ‘Come up here,’ and they went up to heaven in the cloud, while their enemies watched them.
Sa'annan zasu ji murya mai kara daga sama tana ce masu, “Ku hauro nan!” Sa'annan za su tafi sama cikin gajimarai, makiyansu suna kallo.
13 At that very time a great earthquake occurred. A tenth part of the city fell, and seven thousand people perished in the earthquake. Those who escaped were much terrified, and praised the God of heaven.
A waccan sa'a za a yi babbar girgizar kasa, sai kashi daya cikin goma na garin ya fadi. Mutane dubu bakwai za su mutu a girgizar kasar, wadanda suka tsira kuwa za su tsorata su ba da daukaka ga Allah na sama.
14 The second Woe has passed; and there is a third Woe soon to follow!
Annoba ta biyu ta wuce. Duba! Annoba ta uku tana zuwa nan da nan.
15 Then the seventh angel blew; and loud voices were heard in heaven saying – ‘The kingdom of the world has become the kingdom of our Lord and of his Christ, and he will reign for ever and ever.’ (aiōn g165)
Sa'annan mala'ika na bakwai ya busa kahonsa, sai muryoyi masu kara suka yi magana cikin sama cewa, “Mulkin duniya ya zama mulkin Ubangijinmu da na Almasihunsa. Zai yi mulki har abada abadin.” (aiōn g165)
16 At this the twenty-four elders, who were seated on their thrones before God, prostrated themselves on their faces and worshiped him,
Sa'annan dattawan nan ashirin da hudu da ke zaune a kursiyoyinsu a gaban Allah, suka fadi fuskokinsu na kasa. Suka yi wa Allah sujada.
17 saying – ‘We thank you, Lord, our God, the Almighty, who is and who was, that you have assumed your great power and reigned.
Suka ce, “Mun yi maka godiya, Ubangiji Allah, Madaukaki, wanda yake yanzu da wanda yake a da, saboda ka dauki ikonka mai girma ka fara mulki.
18 The nations were enraged, and your wrath fell on them; the time came for the dead to be judged, and for you to give the reward to your servants the prophets, and to the people of Christ, and to those who honor your name – the high and the low alike – and to destroy those who are destroying the earth.’
Al'ummai suka fusata, amma hasalar ka ta zo. Lokaci ya zo da za a yi wa mattatu sharia, da zaka ba da sakamako ga bayinka annabawa, da masu ba da gaskiya, da wadanda suka ji tsoron sunanka, karami da babba. Lokaci kuma ya yi da za ka hallaka wadanda ke hallakar da duniya.”
19 Then the Temple of God in heaven was opened, and the ark containing his covenant was seen in his Temple; and there followed flashes of lightning, cries, peals of thunder, an earthquake, and a great storm of hail.
Sa'annan aka bude haikalin Allah da ke sama, sai aka ga akwatin alkawarinsa a cikin haikalinsa. Sai ga hasken walkiya, da rugugi, da aradu, da girgizar kasa, da manyan duwatsun kankara.

< Revelation 11 >