< Psalms 83 >

1 A song, a psalm of Asaph. Do not keep silent, O God: hold not your peace, be not still, God.
Waƙa ce. Zabura ta Asaf. Ya Allah, kada ka yi shiru; kada ka tsaya cik, ya Allah, kada ka daina motsi.
2 For see! Your enemies roar, those who hate you lift up their heads,
Dubi yadda abokan gābanka suke fariya, dubi yadda maƙiyanka suke ɗaga kansu.
3 laying crafty plans for your people, and plotting against those you treasure.
Da wayo suna ƙulle-ƙulle a kan mutanenka; suna shirya maƙarƙashiya a kan waɗanda kake so.
4 “Come, let us wipe them out as a nation, so Israel’s name will be mentioned no more.”
Suna cewa, “Ku zo, bari mu hallaka su ɗungum a matsayin al’umma, don kada a ƙara tuna da sunan Isra’ila.”
5 For, conspiring with one accord, they have made a league against you
Da zuciya ɗaya suka yi ƙulle-ƙulle tare; suka haɗa kai gāba da kai,
6 Tents of Edom, and Ishmaelites, Moab, and the Hagrites.
tentunan Edom da na mutanen Ishmayel, na Mowab da kuma na Hagirawa,
7 Gebal and Ammon and Amalek, Philistia, with the people of Tyre;
Gebal, Ammon da Amalek, Filistiya, tare da mutanen Taya.
8 Syria, too, is confederate, they have strengthened the children of Lot. (Selah)
Har Assuriya ma ta haɗa kai da su don ta ba da ƙarfi ga zuriyar Lot. (Sela)
9 Deal with them as you dealt with Midian, with Sisera, with Jabin, at the torrent of Kishon,
Ka yi musu abin da ka yi wa Midiyan, yadda ka yi wa Sisera da Yabin a kogin Kishon,
10 who at Endor were destroyed, and became dung for the field.
waɗanda suka hallaka a En Dor suka zama kamar juji a ƙasa.
11 Make their nobles like Oreb and Zeeb, all their princes like Zebah and Zalmunna,
Ka mai da manyansu kamar Oreb da Zeyib, dukan sarakunansu kamar Zeba da Zalmunna,
12 who said, “Let us take for ourselves the meadows of God.”
waɗanda suka ce, “Bari mu mallaki wuraren kiwon Allah.”
13 Whirl them, my God, like dust, like stubble before the wind.
Ka mai da su kamar ɗan tsiron da kan karye, iska ta yi ta turawa, ya Allahna, kamar yayin da iska take hurawa,
14 As the fire that kindles the forest, as flame that sets mountains ablaze,
kamar yadda wuta ke cin kurmi ko harshen wutar da take ci a kan duwatsu,
15 so with your tempest pursue them, terrify them with your hurricane.
haka za ka kore su da iska mai ƙarfi ka kuma firgita su da guguwarka.
16 Make them blush with shame; until they seek your name, O Lord.
Ka rushe fuskokinsu da kunya don mutane su nemi sunanka, ya Ubangiji.
17 Everlasting shame and confusion, disgrace and destruction be theirs.
Bari su kasance cikin kunya da taƙaici; bari su hallaka cikin wulaƙanci.
18 Teach those who you alone are most high over all the earth.
Bari su san cewa kai, wanda sunansa ne Ubangiji, cewa kai kaɗai ne Mafi Ɗaukaka a bisa dukan duniya.

< Psalms 83 >