< Psalms 18 >
1 For the leader. Of David, the servant of the Lord, who recited the words of this song to the Lord after the Lord had saved him from the power of all his enemies and from the hand of Saul. He said: I love you, O Lord, my strength.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda bawan Ubangiji. Ya rera ta ga Ubangiji kalmomin wannan waƙa sa’ad da Ubangiji ya cece shi daga hannun dukan abokan gābansa da kuma daga hannun Shawulu, ya ce, Ina ƙaunarka, ya Ubangiji, ƙarfina.
2 The Lord is my rock, my fortress, deliverer, my God, my rock, where I take refuge, my shield, my defender, my tower.
Ubangiji shi ne dutsena, kagarata da kuma mai cetona; Allahna shi ne dutsena, a gare shi nake neman mafaka. Shi ne garkuwata da ƙahon cetona, mafakata.
3 Worthy of praise is the Lord whom I call on, he rescues me from all my foes.
Na kira ga Ubangiji, wanda ya cancanci yabo, na kuwa kuɓuta daga abokan gābana.
4 The waves of death broke about me, fearful floods of chaos.
Igiyoyin mutuwa sun shaƙe ni; rigyawan hallaka sun sha kaina.
5 Sheol threw cords around me, snares of death came to meet me. (Sheol )
Igiyoyin mutuwa sun nannaɗe kewaye da ni; tarkon mutuwa ya yi mini arangama. (Sheol )
6 In distress I cried to the Lord, and shouted for help to my God; in his temple he heard my voice, into his ears came my cry.
Cikin wahalata na yi kira ga Ubangiji; Na yi kuka ga Allahna don taimako. A Haikalinsa ya ji muryata, Kukana na neman taimako ya kai kunnensa.
7 Then the earth shook and quaked, mountains trembled to their foundations, and quaked because of his wrath.
Ƙasa ta yi rawa ta kuma girgiza, tussan duwatsu sun girgiza; sun yi rawa domin ya yi fushi.
8 Smoke went up from his nostrils, devouring fire from his mouth, coals were kindled by it.
Hayaƙi ya tashi daga kafan hancinsa; wuta mai ci daga bakinsa, garwashi wuta mai ci daga bakinsa.
9 Then he bent the sky and came down, thick darkness was under his feet.
Ya buɗe sammai ya sauko; baƙaƙen gizagizai suna a ƙarƙashin ƙafafunsa.
10 He rode on a cherub and flew, darting on wings of wind,
Ya hau kerubobi ya kuma yi firiya; ya yi shawagi a fikafikan iska.
11 with his screen of darkness about him, in thick dark clouds of water.
Ya mai da duhu abin rufuwarsa, rumfa kewaye da shi, baƙaƙen gizagizan ruwan sama na sarari,
12 At the radiance before him there passed hailstones and coals of fire.
daga cikin hasken kasancewarsa gizagizai suka yi gaba, da ƙanƙara da kuma walƙiya.
13 The Lord thundered from heaven, the Most High uttered his voice.
Ubangiji ya yi tsawa daga sama; muryar Mafi Ɗaukaka ya yi kāra.
14 He shot his arrows and scattered them, flashed lightnings, and routed them.
Ya harba kibiyoyinsa ya kuma watsar da abokan gāba, walƙiya mai girma ya fafare su.
15 The channels of the sea were revealed, the world was laid bare to its base, at your rebuke, O Lord, at the blast of the breath of your nostrils.
Kwarin teku sun bayyana tussan duniya sun bayyana a fili sa’ad da ka tsawata, ya Ubangiji, sa’ad da ka numfasa daga hancinka.
16 He stretched from on high, he seized me, drew me up from the mighty waters,
Ya miƙa hannunsa daga sama ya kama ni; ya ja ni daga zurfin ruwaye.
17 and saved me from those who hated me – fierce foes, too mighty for me.
Ya cece ni daga abokin gābana mai ƙarfi, daga abokan gābana, waɗanda suka fi ƙarfina.
18 In my day of distress they assailed me, but the Lord proved my support.
Sun yi arangama da ni a ranar masifa, amma Ubangiji ya zama mai taimakona.
19 To a spacious place he brought me, and, for love of me, he saved me.
Ya fitar da ni zuwa wuri mai sarari; ya kuɓutar da ni, gama yana jin daɗina.
20 The Lord repays my innocence, he rewards my cleanness of hands.
Ubangiji ya yi haka da ni bisa ga adalcina; bisa ga tsabtar hannuwana ya ba ni lada.
21 For I kept the ways of the Lord, nor have wickedly strayed from my God.
Gama na kiyaye hanyoyin Ubangiji; ban yi mugunta ta wurin juyewa daga Allahna ba.
22 His commandments were all before me, his statutes I put not away.
Dukan dokokinsa suna a gābana; ban juye daga ƙa’idodinsa ba.
23 And I was blameless before him, guarding myself from sin.
Na kasance marar laifi a gabansa na kuma kiyaye kaina daga zunubi.
24 So the Lord repaid my innocence, my cleanness of hands in his sight.
Ubangiji ya ba ni lada bisa ga adalcina, bisa ga tsabtan hannuwana a gabansa.
25 With the loyal you are loyal, and with the blameless blameless.
Ga mai aminci ka nuna kanka mai aminci, ga marar laifi ka nuna kanka marar laifi,
26 With the pure you show yourself pure, but shrewd with the devious.
ga mai tsabta ka nuna kanka mai tsabta, amma ga karkatacce, ka nuna kanka mai wayo.
27 For the lowly people you save, but haughty eyes you abase.
Kakan cece mai sauƙinkai amma kakan ƙasƙantar da masu girman kai.
28 You are my lamp, Lord, my God who enlightens my darkness.
Kai Ya Ubangiji, ka sa fitilata ta yi ta ci; Allahna ya mai da duhu ya zama haske.
29 With you I can storm a rampart, with my God I can leap a wall.
Da taimakonka zan iya fāɗa wa runduna; tare da Allahna zan iya rinjayi katanga.
30 As for God, his way is perfect; the word of the Lord is pure. He is shield to all who take refuge in him.
Game da Allah kuwa, hanyarsa cikakkiya ce; maganar Ubangiji marar kuskure ne. Shi garkuwa ne ga dukan waɗanda suke neman mafaka a gare shi.
31 For who is God but the Lord? And who is a rock but our God?
Gama wane ne Allah in ba Ubangiji ba? Wane ne kuwa Dutse in ba Allahnmu ba?
32 The God who arms me with strength, who cleared and smoothed my way.
Allah ne ya ƙarfafa ni da ƙarfi ya kuma sa hanyarta ta zama cikakkiya.
33 He made my feet like hinds’ feet, and set me up on the heights.
Ya sa ƙafafuna kamar ƙafafun barewa; ya sa na iya tsaya a kan ƙwanƙoli.
34 He taught my hands how to fight, and my arms how to bend a bronze bow.
Ya horar da hannuwana don yaƙi; hannuwana za su iya tanƙware bakan tagulla.
35 The shield of your help you gave me, your right hand supports me, you stoop down to make me great.
Ka ba ni garkuwar nasara, kuma hannunka na dama yana riƙe ni; ya sunkuya don ka mai da ni mai girma.
36 In your strength I took giant strides, and my feet never slipped.
Ka fadada hanyar da yake a ƙarƙashina, don kada ɗiɗɗigena yă juya.
37 So I chased the foe till I caught them, and turned not, till I made an end of them.
Na bi abokan gābana na kuma cim musu; ban juya ba sai da na hallaka su.
38 I smashed them, they could not rise, they fell beneath my feet.
Na ragargaza su har ba za su iya tashi ba; sun fāɗi a ƙarƙashin ƙafafuna.
39 You did arm me with strength for war, you did bow my assailants beneath me.
Ka ƙarfafa ni da ƙarfi saboda yaƙi; ka sa abokan gābana suka rusuna mini.
40 You made my foes turn their back to me, and those who did hate me I finished.
Ka sa abokan gābana suka juya suka gudu, na kuma hallaka abokan gābana.
41 They cried for help, but none saved them; to the Lord, but he answered them not.
Sun nemi taimako, amma ba su sami wanda zai cece su ba, ga Ubangiji, amma bai amsa ba.
42 I beat them like dust of the market-place, stamped them like mud of the streets.
Na murƙushe su kamar ƙura mai laushi da iska ke kwashewa; na zubar da su kamar laka a tituna.
43 From the strife of the peoples you saved me, you made me head of the nations, peoples I knew not did serve me.
Ka cece ni daga harin mutane; ka mai da ni kan al’ummai. Mutanen da ban sani ba sun zama bayina,
44 On the instant they hear, they obey me, foreigners come to me cringing.
da zarar sun ji ni, sukan yi mini biyayya; baƙi suna rusuna a gabana.
45 Foreigners lose courage, and come out of their strongholds trembling.
Duk sukan karai; suna zuwa da rawan jiki daga mafakansu.
46 The Lord is alive! Blest be my rock! Exalted be God, my protector!
Ubangiji mai rai ne! Yabo ya tabbata ga Dutsena! Girma ya tabbata ga Allah Mai cetona!
47 The God who gave me revenge, and brought down nations beneath me,
Shi ne Allah mai sāka mini, wanda yake sa al’ummai a ƙarƙashina,
48 who saved me from angry foes, and set me above my assailants, safe from the violent.
wanda yakan cece ni daga abokan gābana. Ana girmama ka bisa abokan gābana; daga masu tā-da-na-zaune-tsaye ka kuɓutar da ni.
49 For this I will praise you among the nations, making music, O Lord, to your name:
Saboda haka zan yabe ka a cikin al’ummai, ya Ubangiji; zan rera yabai ga sunanka.
50 for great triumphs he grants to his king, and faithful love he shows his anointed, to David and his seed evermore.
Yakan ba sarkinsa nasarori; yakan nuna alheri marar ƙarewa ga shafaffensa, ga Dawuda da zuriyarsa har abada.