< Psalms 64 >
1 For the leader. A psalm of David. Hear, O my God, the voice of my lament: guard my life from the dread of the foe.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Ka ji ni, ya Allah, yayinda nake faɗin abin da yake damuna; ka tsare raina daga barazanan abokin gāba.
2 Hide me from villains who secretly plot, from the blustering throng of the workers of evil,
Ka ɓoye ni daga ƙulle-ƙullen mugaye, daga daure dauren wannan taro masu aikata mugunta.
3 who have sharpened their tongue like a sword, and aimed bitter words like arrows,
Sukan wāsa harsunansu kamar takuba su harba kalmominsu kamar kibiyoyi masu kisa.
4 which from ambush they launch at the blameless, shooting swiftly and unafraid.
Sukan yin kwanto su harbi marar laifi; sukan yi harbi nan da nan, ba tsoro.
5 They strengthen their wicked purpose, they tell of the snares they have hidden, they say to themselves, ‘Who can see?’
Sukan ƙarfafa juna a mugayen ƙulle-ƙullensu, sukan yi magana yadda za su ɓoye tarkunansu; su ce, “Wa zai gan su?”
6 They think out their crimes full cunningly hidden deep in their crafty hearts.
Sukan yi ƙulle-ƙullen rashin adalci su ce, “Mun gama ƙulla cikakkiyar maƙarƙashiya tsab!” Zuciyar mutum da tunaninsa, suna da wuyar ganewa.
7 But God with his arrow will shoot them, swiftly shall they be smitten.
Amma Allah zai harbe su da kibiyoyi; nan da nan za a buge su su fāɗi.
8 For their tongue he will bring them to ruin, all will shudder with horror at the sight of them.
Zai juya harshensu a kansu yă kuma kawo su ga hallaka; duk waɗanda suka gan su za su kaɗa kai, suna musu ba’a.
9 Then every person, touched to awe, as they ponder what God has wrought, will tell the tale of his deeds.
Dukan mutane za su ji tsoro; za su yi shelar ayyukan Allah su kuma yi tunanin abin da ya aikata.
10 In the Lord shall the righteous rejoice, in him shall they take refuge; and all the true-hearted shall glory.
Bari masu adalci su yi farin ciki a cikin Ubangiji su kuma nemi mafaka a gare shi; bari dukan masu gaskiya a zuciya su yabe shi!