< Micah 1 >
1 The Lord’s message which came to Micah of Morsheth in the reigns of Jotham, Ahaz and Hezekiah, kings of Judah. The visions he saw about Samaria and Jerusalem.
Maganar Ubangiji ta zo wa Mika mutumin Moreshet a zamanin Yotam, da na Ahaz, da kuma na Hezekiya, sarakunan Yahuda, Mika ya ga wahayi a kan Samariya da kuma a kan Urushalima. Ga abin da ya ce.
2 Listen, all you peoples! Pay attention, all you inhabitants of the earth! For the Lord God will be a witness against you, the Lord from his holy temple!
Ku ji, ya ku mutane duka, ki saurara, ya ke duniya da dukan mazauna cikinki, bari Ubangiji Mai Iko Duka yă zama shaida a kanku, daga haikalinsa mai tsarki.
3 The Lord is coming from his holy place, he descends and treads on the heights of the earth,
Duba! Ubangiji yana zuwa daga wurin zamansa; zai sauko yă taka maɗaukakan wuraren duniya.
4 so that the mountains melt beneath like wax in the presence of the fire, and the valleys break apart like water poured down a steep descent.
Duwatsu za su narke a ƙarƙashin ƙafafunsa, kamar kaki a gaban wuta, kwaruruka kuma za su ɓace, kamar ruwan da yake gangarowa daga tsauni.
5 All this is because of the crime of Jacob, and for the sin of the house of Israel. What was the crime of Jacob? Was it not Samaria? What is the sin of Judah? Is it not Jerusalem?
Duk wannan zai faru saboda laifin Yaƙub, da kuma zunuban gidan Isra’ila ne. Mene ne laifin Yaƙub? Shin, ba Samariya ba ce? Ina ne maɗaukakan wuraren Yahuda? Shin, ba Urushalima ba ce?
6 ‘I will make Samaria a ruin in an open field, and a place where a vineyard is planted, I will hurl down her stones into the valley, and lay bare her foundations.
“Saboda haka zan mai da Samariya tarin juji, wurin noman inabi. Zan zubar da duwatsunta a cikin kwari in kuma bar harsashin gininta a bayyane.
7 ‘All her images will be shattered, and all her statues will be burned with fire, and all her idols I will lay in ruins. For they were acquired by prostitution, and to prostitution they will return.’
Za a ragargaje dukan allolinta; za a ƙone dukan baye-bayenta na haikali da wuta; zan lalatar da dukan gumakanta. Tun da ta wurin karuwanci ne ta tattara su, ga karuwanci kuma za su koma.”
8 This is why I will mourn and wail, I will go barefoot and naked, I will howl like the jackals and mourn like the desert owl.
Saboda wannan zan yi baƙin ciki, in yi kuka; zan yi tafiya ba takalmi, zan tuɓe, in kuma yi tafiya tsirara. Zan yi kuka kamar dila, in yi baƙin ciki kamar mujiya.
9 For the blow that Samaria has received is incurable. It has spread over Judah, it extends even to the gate of my people, even to Jerusalem.
Gama raunin Samariya ba mai warkewa ba ne; ya bazu har Yahuda. Ya ma kai bakin ƙofar mutanena, har ma Urushalima da kanta.
10 Don’t tell this in Gath! Don’t even cry – but sit in the dust at Beth-leaphrah.
Kada a faɗe shi a Gat; kada ma a yi kuka. A maimako haka, a yi birgima a cikin ƙura a Bet-Leyafra.
11 Pass by, inhabitants of Shaphir, naked and ashamed! The inhabitants of Zaanan cannot leave their city. Beth-ezel laments and removes its support from you.
Ku wuce tsirara da kuma kunya, ku mazaunan Shafir. Bet-Ezel tana makoki domin babu wani daga Za’anan da ya fito don yă taimaka.
12 The inhabitants of Maroth wait anxiously for good! But the Lord has sent disaster to the gates of Jerusalem.
Mazaunan Marot sun ƙosa su ga alheri, amma Ubangiji ya sauko da azaba, har zuwa ƙofar Urushalima.
13 Harness the horse to the chariot, inhabitants of Lachish. You led the daughter of Zion, Jerusalem, into sin, in you are found the crimes of Israel.
Ku da kuke zama a Lakish, ku ɗaura wa dawakai kekunan yaƙi. Gama ku kuka fara yin zunubi a Sihiyona, gama an sami laifofin Isra’ila a cikinku.
14 Therefore you must give parting gifts to Moresheth-gath. Beth-achzib will betray the kings of Israel.
Saboda haka za ku ba da kyautan bankwana ga Moreshet Gat. Garin Akzib zai zama abin yaudara ga sarakunan Isra’ila.
15 I will hand you to a conqueror, people of Mareshah, the leaders of Israel will hide in Adullam Cave!
Ku mazaunan Maresha Ubangiji zai kawo wanda zai ci ku da yaƙi. Sarakunan Isra’ila za su gudu zuwa Adullam.
16 Shave your head in morning for the children you love, until you are bald as vultures, because they have left you for exile.
Ku aske kanku ƙwal don makoki, ku yi wa kanku ƙwalƙwal kamar ungulu. Gama za a ja’ya’yan da kuke farin ciki a kai su bauta.