< Habakkuk 2 >
1 I will take my stand on my watch-tower, and station myself on a turret. I will watch to see what the Lord will say to me, what answer he will make to my complaint.
Zan tsaya wurin tsarona in kuma zauna a kan katanga; zan jira in ga abin da zai ce mini, da kuma wace amsa zan bayar ga wannan kuka.
2 Then the Lord answered me and said: Inscribe the vision plainly on tablets, so that even someone running by could read it.
Sa’an nan Ubangiji ya amsa ya ce, “Ka rubuta wannan ru’uya ka bayyana ta a fili a kan alluna don mai shela yă ruga da ita, yă kai.
3 Though the vision waits for the time set, it hastens to fulfilment and will not fail; Though it linger long, wait for it. For it surely will come and will not be delayed.
Gama ru’uyar tana jiran ƙayyadadden lokaci; tana zancen ƙarshe kuma ba za tă zama ƙarya ba. Ko da ka ga kamar tana jinkiri, ka jira ta; lalle za tă zo, ba za tă makara ba.
4 The strength of the proud fails, but the upright lives by their faithfulness.
“Duba, abokin gāba ya cika da ɗaga kai; sha’awarsa ba daidai ba ce, amma mai adalci zai rayu ta wurin bangaskiyarsa,
5 Wealth is treacherous, the arrogant never have enough. They make their desire as wide as Sheol, are like death, unsatisfied, For they gather to themselves all the nations, bring together to themselves all peoples. (Sheol )
ba shakka, ruwan inabi ya yaudare shi; yana fariya kuma ba ya hutu. Domin shi mai haɗama ne kamar kabari kuma kamar mutuwa, ba ya ƙoshi; yakan tattara dukan al’ummai wa kansa yana kuma kama dukan mutane su zama kamammu. (Sheol )
6 Shouldn’t everyone mock them? sing a taunt-song against them, and say: Woe to the person who amasses what is not theirs, and loads them self down with goods taken in pledge!
“Dukansu ba za su yi masa tsiya, suna yin masa ba’a da dariya ba, suna cewa, “‘Kaito ga wannan wanda ya tara wa kansa kayan sata ya kuma wadatar da kansa da kayan ƙwace! Har yaushe wannan abu zai ci gaba?’
7 Won’t your creditors suddenly rise, and those who will overthrow you awake, and you become their prey?
Masu binka bashi ba za su taso maka nan da nan ba? Ba za su farka su sa ka fargaba ba? Ta haka ka zama ganima a gare su.
8 For as you have plundered many peoples, the survivors will prey upon you. You have shed blood and committed violence to the earth, peoples and their cities.
Domin ka washe al’ummai masu yawa, mutanen da suka rage za su washe ka. Domin ka zub da jinin mutane; ka hallaka ƙasashe, da birane, da kuma kowa da yake cikinsu.
9 Woe to you who seeks unjust gain for your dynasty, who sets your nest on high to be safe from the reach of misfortune!
“Kaito ga wanda ya gina masarautarsa da ƙazamar riba don yă kafa sheƙarsa can bisa, don yă tsere wa zama kango!
10 You have planned only shame for your dynasty. You have destroyed many peoples, and brought guilt upon yourself;
Ka ƙulla lalacin mutane masu yawa, ta haka ka kunyatar da gidanka ka kuma hallaka ranka.
11 the stone will cry out from the wall, and the beam from the timber will answer it.
Duwatsun katanga za su yi kuka, ginshiƙan katako kuma za su amsa.
12 Woe to the person who builds a city by bloodshed, and founds a town by crime
“Kaiton mutumin da ya gina birni da jinin da ya zubar ya kuma kafa gari ta wurin mugun aiki!
13 while the peoples toil for what fires will consume, and the nations weary themselves for nothing! This the Lord of hosts has said,
Ba Ubangiji Maɗaukaki ne ya ƙudura cewa wahalar mutane ta zama mai kawai don wuta ba, cewa al’ummai su gajiyar da kansu a banza ba?
14 and the earth will be as full of the knowledge of the glory of the Lord as the seas are full of water.
Gama duniya za tă cika da sanin ɗaukakar Ubangiji, yadda ruwaye suka rufe teku.
15 Woe to him who in fury gives drink to his neighbor to make him drunk, and see him naked.
“Kaito wanda ya ba wa maƙwabtansa abin sha, yana ta zubawa daga salkan ruwan inabi har sai sun bugu, don dai yă ga tsiraicinsu.
16 You are filled with shame, not glory; drink yourself and be uncovered. The cup from the Lord’s hand will pass in turn to you, and shame will cover your glory!
Za ka cika da kunya a maimakon ɗaukaka. Yanzu lokacinka ne! Kai ma ka sha, a kuma tone asirinka! Gama kwaf na hannun daman Ubangiji yana zuwa kewaye da kai, abin kunya kuma zai rufe darajarka.
17 For the violence done to Lebanon will overwhelm you, the destruction of animals will terrify you, because you shed people’s blood on the earth, destroyed people and their cities.
Ɓarnar da ka yi wa Lebanon zai komo kanka, kuma hallakar dabbobin da ka yi zai sa dabbobi su tsorata ka. Gama ka zub da jinin mutum; ka hallaka ƙasashe, da birane, da kuma kowa da yake cikinsu.
18 What use is an idol? A human made it, a metal image. It cannot speak, it cannot teach truth, Why does its maker trust it?
“Ina amfanin gunki da mutum ne ya sassaƙa? Ko siffar da take koyar da ƙarya? Gama wanda ya yi shi yana dogara ne ga halittarsa; ya yi gumakan da ba sa magana.
19 Woe to the person who says to a block, awake! to a dumb stone, arise! What can it teach? It may be set with gold and silver, but there is no breath at all within it.
Kaito wanda ya ce da katako, ‘Rayu!’ Ko kuwa dutse marar rai, ‘Farka!’ Zai iya bishewa ne? An dalaye shi da zinariya da azurfa; ba numfashi a cikinsa.”
20 The Lord is in his holy temple. Let all the earth be silent before him!
Amma Ubangiji yana a cikin haikalinsa mai tsarki; bari dukan duniya tă yi shiru a gabansa.